< 1 Sama’ila 22 >

1 Dawuda ya bar Gat, ya tsere zuwa kogon Adullam. Da’yan’uwansa da kuma iyalan mahaifinsa suka ji labari, sai suka tafi can wurinsa.
Therfor Dauid yede fro thennus, and fledde in to the denne of Odollam; and whanne hise britheren, and al the hows of his fadir hadden herd this, thei camen doun thidur to hym.
2 Dukan mutanen da suke cikin wahala, da waɗanda ake binsu bashi, da masu damuwoyi, suka tattaru a wurin Dawuda. Shi kuwa ya zama shugabansu. Yawansu ya kai ɗari huɗu.
And alle men that weren set in angwisch, and oppressid with othere mennus dette, and in bittir soule, camen togidere to hym; and he was maad the prince `of hem, and as foure hundrid men weren with hym.
3 Daga can Dawuda ya tafi Mizfa a Mowab. Ya ce wa sarkin Mowab, “Za ka yarda mahaifina da mahaifiyata su zo su zauna a wurinka kafin in san abin da Allah zai yi da ni?”
And Dauid yede forth fro thennus in to Masphat, which is of Moab; and he seide to the kyng of Moab, Y preye, dwelle my fadir and my modir with you, til Y wite what thing God schal do to me.
4 Saboda haka ya bar su a wurin sarkin Mowab, suka zauna da shi duk tsawon lokacin da Dawuda yake ta ɓuya a kogwannin duwatsu.
And he lefte hem bifor the face of the kyng of Moab; and thei dwelliden at hym in alle daies, `in whiche Dauid was in `the forselet, ether stronghold.
5 Amma annabin nan Gad ya ce wa Dawuda, “Kada ka zauna a nan, maza ka tashi ka shiga ƙasar Yahuda”. Sai Dawuda ya tashi ya tafi jejin Heret.
And Gad, the profete, seide to Dauid, Nyle thou dwelle in `the forselet; go thou forth, and go in to the lond of Juda. And Dauid yede forth, and cam in to the forest of Areth.
6 Sai Shawulu ya sami labari cewa an ga Dawuda da mutanensa. Shawulu kuwa yana zaune da māshinsa kusa a ƙarƙashin itacen tsamiya a tudun Gibeya, tare da dukan ma’aikatansa kewaye da shi.
And Saul herde, that Dauid apperide, and the men that weren with hym. Forsothe whanne Saul dwellide in Gabaa, and was in the wode which is in Rama, and `helde a spere in the hond, and alle hise seruauntis stoden aboute hym,
7 Ya ce musu, “Mutanen Benyamin, ku saurara; ɗan Yesse zai iya ba dukanku filaye da gonakin inabi ne? Zai ba dukanku shugabanci na dubbai ko shugabanci na ɗari-ɗari?
he seide to hise seruauntis that stoden nyy hym, The sones of Gemyny, here me now; whether the sone of Ysai schal yyue to alle you feeldis and vyneris, and schal make alle you tribunes and centuriouns?
8 Abin da ya sa dukanku kuka gama baki a kaina? Ba wanda ya gaya mini lokacin da ɗana ya yi yarjejjeniya da ɗan Yesse, ba wanda ya kulla da ni, ko ya gaya mini cewa ɗana ya sa bawana yă tayar mini, yana fakona kamar yadda yake a yau.”
For alle ye han swore, ether conspirid, togidere ayens me, and noon is that tellith to me; moost sithen also my sone hath ioyned boond of pees with the sone of Ysai; noon is of you, that sorewith `for my stide, nether that tellith to me, for my sone hath reisid my seruaunt ayens me, settynge tresoun to me `til to dai.
9 Amma Doyeg mutumin Edom da yake tsaye tare da fadawan Shawulu ya ce, “Na ga ɗan Yesse ya zo wurin Ahimelek ɗan Ahitub a Nob.
Sotheli Doech of Ydumye answeride, that stood nyy, and was the firste among `the seruauntis of Saul, and seide, Y siy `the sone of Ysai in Nobe, at Achymelech, preest, the sone of Achitob;
10 Ahimelek ya roƙi Ubangiji saboda shi, ya kuma ba shi guzuri da takobin Goliyat Bafilistin.”
which counseilide the Lord for Dauid, and yaf meetis `to hym, but also he yaf to Dauid the swerd of Goliath Filistei.
11 Sai sarki ya aika aka kira masa Ahimelek firist ɗan Ahitub da dukan iyalin mahaifinsa. Dukansu suka zo wurin sarki.
Therfor the kyng sente to clepe Achymelech, the preest, `the sone of Achitob, and al the hows of his fadir, of preestis that weren in Nobe; whiche alle camen to the kyng.
12 Shawulu ya ce, “Ka saurara yanzu, ɗan Ahitub.” Ya amsa ya ce, “Ina saurara, ranka yă daɗe.”
And Saul seide to Achymelech, Here, thou sone of Achitob.
13 Shawulu ya ce masa, “Don me ka gama baki da ɗan Yesse a kaina har ka ba shi burodi da takobin (Goliyat), ka kuma roƙi Allah don yă tayar mini, yă kuma yi fakona kamar yadda yake yi yau?”
Which answeride, Lord, Y am redi. And Saul seide to hym, Whi hast thou conspirid ayens me, thou, and the sone of Ysai, and yauest looues and a swerd to hym, and councelidist the Lord for hym, that he schulde rise ayens me, and he dwellith a tretour `til to dai?
14 Ahimelek ya ce wa sarki, “A cikin bayinka duka, wa ke da aminci iri na Dawuda, surukin sarki, shugaban jarumanka wanda ake girmamawa da gaske a gidanka?
And Achymelech answeride to the kyng, and seide, And who among alle thi seruauntis is as Dauid feithful, and the sone in lawe `of the kyng, and goynge at thi comaundement, and gloriouse in thin hows?
15 A wannan rana ce da na fara roƙon Allah saboda shi? Kada sarki yă zargi bawansa ko wani daga iyalin mahaifinsa, gama bawanka bai san kome a kan dukan waɗannan al’amura ba.”
Whether Y bigan to dai to counsele the Lord for hym? Fer be this fro me; suppose not the kyng ayens his seruaunt `siche a thing in al `the hows of my fadir; for thi seruaunt knew not ony thing, ether litil ethir greet, of this cause.
16 Amma sarki ya ce, “Lalle Ahimelek za ka mutu, da kai da dukan iyalin mahaifinka.”
And the kyng seide, Achymelech, thou schalt die bi deeth, thou, and al the hows of thi fadir.
17 Sai sarki ya umarci matsaran da suke tsaye kusa da shi ya ce, “Ku kakkashe firistocin Ubangiji, gama su ma sun goyi bayan Dawuda. Sun san yana gudu, duk da haka ba su gaya mini ba.” Amma ma’aikatan sarki ba su yarda su sa hannu su kashe firistocin Ubangiji ba.
And the kyng seide to men able to be sent out, that stoden aboute hym, Turne ye, and sle the preestis of the Lord, for the hond of hem is with Dauid; and thei wisten that he fledde, and thei schewiden not to me. Sotheli the seruauntis of the kyng nolden holde forth her hond in to the preestis of the Lord.
18 Sai sarki ya umarce Doyeg ya ce, “Ka juya ka kakkashe firistocin.” Doyeg mutumin Edom ya juya ya kakkashe firistocin. A ranar kuwa ya kashe mutum tamanin da biyar waɗanda suke sanye da efod na lilin.
And the kyng seide to Doech, Turne thou, and hurle in to the preestis of the Lord. And Doech of Ydumee turnede, and hurlide in to the preestis, and stranglide in that dai foure score and fyue men, clothid with `ephoth of lynnun cloth.
19 Ya kuma hallaka Nob birnin firistoci, ya kashe dukan mata, da maza, da yara, da jarirai, da shanu, da jakuna, da kuma tumaki.
Forsothe he smoot Nobe, the citee of preestis, by the scharpnesse of swerd, men and wymmen, litle children and soukynge, and oxe, and asse, and sheep, bi the scharpnesse of swerd.
20 Amma Abiyatar ɗan Ahimelek jikan Ahitub ya tsere, ya gudu zuwa wurin Dawuda.
Forsothe o sone of Achymelech, sone of Achitob, ascapide, of which sone the name was Abiathar; and he fledde to Dauid,
21 Abiyatar gaya wa Dawuda cewa, “Shawulu ya hallaka firistocin Ubangiji.”
and telde to hym that Saul hadde slayn the preestis of the Lord.
22 Dawuda ya ce wa Abiyatar, “Lalle a wancan ranar, sa’ad da na ga Doyeg mutumin Edom a can, na san tabbatacce zai gaya wa sarki. Ni ne sanadin mutuwar dukan iyalin mahaifinka.
And Dauid seide to Abiathar, Sotheli Y wiste, `that is, Y coniectide, ether dredde, in that dai, that whanne Doech of Ydumee was there, he wolde telle with out doute to Saul; Y am gilti of alle the lyues of thi fadir.
23 Ka zauna tare da ni, kada ka ji tsoro mutumin da yake neman ranka, yana nema raina ma. Ka zauna lafiya tare da ni.”
Dwelle thou with me, drede thou not; if ony man sekith thi lijf, he schal seke also my lijf, and thou schalt be kept with me.

< 1 Sama’ila 22 >