< 1 Sama’ila 22 >

1 Dawuda ya bar Gat, ya tsere zuwa kogon Adullam. Da’yan’uwansa da kuma iyalan mahaifinsa suka ji labari, sai suka tafi can wurinsa.
So David left there and escaped to the cave of Adullam. When his brothers and all his father's house heard it, they went down there to him.
2 Dukan mutanen da suke cikin wahala, da waɗanda ake binsu bashi, da masu damuwoyi, suka tattaru a wurin Dawuda. Shi kuwa ya zama shugabansu. Yawansu ya kai ɗari huɗu.
Everyone who was in distress, everyone who was in debt, and everyone who was discontented—they all gathered to him. David became captain over them. There were about four hundred men with him.
3 Daga can Dawuda ya tafi Mizfa a Mowab. Ya ce wa sarkin Mowab, “Za ka yarda mahaifina da mahaifiyata su zo su zauna a wurinka kafin in san abin da Allah zai yi da ni?”
Then David went from there to Mizpah in Moab. He said to the king of Moab, “Please let my father and my mother go out with you until I know what God will do for me.”
4 Saboda haka ya bar su a wurin sarkin Mowab, suka zauna da shi duk tsawon lokacin da Dawuda yake ta ɓuya a kogwannin duwatsu.
He left them with the king of Moab. His father and mother stayed with him the whole time that David was in his stronghold.
5 Amma annabin nan Gad ya ce wa Dawuda, “Kada ka zauna a nan, maza ka tashi ka shiga ƙasar Yahuda”. Sai Dawuda ya tashi ya tafi jejin Heret.
Then the prophet Gad said to David, “Do not stay in your stronghold. Leave and go into the land of Judah.” So David left there and went into the forest of Hereth.
6 Sai Shawulu ya sami labari cewa an ga Dawuda da mutanensa. Shawulu kuwa yana zaune da māshinsa kusa a ƙarƙashin itacen tsamiya a tudun Gibeya, tare da dukan ma’aikatansa kewaye da shi.
Saul heard that David had been discovered, along with the men who were with him. Now Saul was sitting in Gibeah under the tamarisk tree in Ramah, with his spear in his hand, and all his servants were standing around him.
7 Ya ce musu, “Mutanen Benyamin, ku saurara; ɗan Yesse zai iya ba dukanku filaye da gonakin inabi ne? Zai ba dukanku shugabanci na dubbai ko shugabanci na ɗari-ɗari?
Saul said to his servants who stood around him, “Listen now, people of Benjamin! Will the son of Jesse give every one of you fields and vineyards? Will he make you all captains of thousands and captains of hundreds,
8 Abin da ya sa dukanku kuka gama baki a kaina? Ba wanda ya gaya mini lokacin da ɗana ya yi yarjejjeniya da ɗan Yesse, ba wanda ya kulla da ni, ko ya gaya mini cewa ɗana ya sa bawana yă tayar mini, yana fakona kamar yadda yake a yau.”
in exchange for all of you plotting against me? None of you informs me when my son makes a covenant with the son of Jesse. None of you is sorry for me. None of you informs me that my son has incited my servant David against me. Today he hides and waits for me so he may attack me.”
9 Amma Doyeg mutumin Edom da yake tsaye tare da fadawan Shawulu ya ce, “Na ga ɗan Yesse ya zo wurin Ahimelek ɗan Ahitub a Nob.
Then Doeg the Edomite, who stood by the servants of Saul, answered, “I saw the son of Jesse come to Nob, to Ahimelech son of Ahitub.
10 Ahimelek ya roƙi Ubangiji saboda shi, ya kuma ba shi guzuri da takobin Goliyat Bafilistin.”
He prayed to Yahweh that he might help him, and he gave him provisions and the sword of Goliath the Philistine.”
11 Sai sarki ya aika aka kira masa Ahimelek firist ɗan Ahitub da dukan iyalin mahaifinsa. Dukansu suka zo wurin sarki.
Then the king sent someone to summon the priest Ahimelech son of Ahitub and all his father's house, the priests who were in Nob. All of them came to the king.
12 Shawulu ya ce, “Ka saurara yanzu, ɗan Ahitub.” Ya amsa ya ce, “Ina saurara, ranka yă daɗe.”
Saul said, “Listen now, son of Ahitub.” He answered, “Here I am, my master.”
13 Shawulu ya ce masa, “Don me ka gama baki da ɗan Yesse a kaina har ka ba shi burodi da takobin (Goliyat), ka kuma roƙi Allah don yă tayar mini, yă kuma yi fakona kamar yadda yake yi yau?”
Saul said to him, “Why have you plotted against me, you and the son of Jesse, in that you have given him bread, and a sword, and have prayed to God that he might help him, so that he might rise up against me, to hide in secret, as he does today?”
14 Ahimelek ya ce wa sarki, “A cikin bayinka duka, wa ke da aminci iri na Dawuda, surukin sarki, shugaban jarumanka wanda ake girmamawa da gaske a gidanka?
Then Ahimelech answered the king and said, “Who among all your servants is so faithful as David, who is the king's son-in-law and is over your bodyguard, and is honored in your house?
15 A wannan rana ce da na fara roƙon Allah saboda shi? Kada sarki yă zargi bawansa ko wani daga iyalin mahaifinsa, gama bawanka bai san kome a kan dukan waɗannan al’amura ba.”
Is today the first time I have prayed to God to help him? Far be it from me! Do not let the king impute anything to his servant or to all the house of my father. For your servant knows nothing of this whole matter.”
16 Amma sarki ya ce, “Lalle Ahimelek za ka mutu, da kai da dukan iyalin mahaifinka.”
The king replied, “You will surely die, Ahimelech, you and all your father's house.”
17 Sai sarki ya umarci matsaran da suke tsaye kusa da shi ya ce, “Ku kakkashe firistocin Ubangiji, gama su ma sun goyi bayan Dawuda. Sun san yana gudu, duk da haka ba su gaya mini ba.” Amma ma’aikatan sarki ba su yarda su sa hannu su kashe firistocin Ubangiji ba.
The king said to the guard that stood around him, “Turn and kill the priests of Yahweh. Because their hand also is with David, and because they knew that he fled, but did not reveal it to me.” But the servants of the king would not put out their hand to kill the priests of Yahweh.
18 Sai sarki ya umarce Doyeg ya ce, “Ka juya ka kakkashe firistocin.” Doyeg mutumin Edom ya juya ya kakkashe firistocin. A ranar kuwa ya kashe mutum tamanin da biyar waɗanda suke sanye da efod na lilin.
Then the king said to Doeg, “Turn and kill the priests.” So Doeg the Edomite turned and attacked the priests; he killed eighty-five persons who wore a linen ephod that day.
19 Ya kuma hallaka Nob birnin firistoci, ya kashe dukan mata, da maza, da yara, da jarirai, da shanu, da jakuna, da kuma tumaki.
He also put to the sword Nob, the city of the priests; both men and women, children and infants, and oxen and donkeys and sheep he put to the sword.
20 Amma Abiyatar ɗan Ahimelek jikan Ahitub ya tsere, ya gudu zuwa wurin Dawuda.
But one of the sons of Ahimelech son of Ahitub, named Abiathar, escaped and fled after David.
21 Abiyatar gaya wa Dawuda cewa, “Shawulu ya hallaka firistocin Ubangiji.”
Abiathar told David that Saul had killed Yahweh's priests.
22 Dawuda ya ce wa Abiyatar, “Lalle a wancan ranar, sa’ad da na ga Doyeg mutumin Edom a can, na san tabbatacce zai gaya wa sarki. Ni ne sanadin mutuwar dukan iyalin mahaifinka.
David said to Abiathar, “I knew on that day, when Doeg the Edomite was there, that he would surely tell Saul. I am responsible for every death in your father's family!
23 Ka zauna tare da ni, kada ka ji tsoro mutumin da yake neman ranka, yana nema raina ma. Ka zauna lafiya tare da ni.”
Stay with me and do not be afraid. For the one who seeks your life seeks mine as well. You will be safe with me.”

< 1 Sama’ila 22 >