< 1 Sama’ila 22 >

1 Dawuda ya bar Gat, ya tsere zuwa kogon Adullam. Da’yan’uwansa da kuma iyalan mahaifinsa suka ji labari, sai suka tafi can wurinsa.
And he went David from there and he escaped to [the] cave of Adullam and they heard brothers his and all [the] household of father his and they went down to him there towards.
2 Dukan mutanen da suke cikin wahala, da waɗanda ake binsu bashi, da masu damuwoyi, suka tattaru a wurin Dawuda. Shi kuwa ya zama shugabansu. Yawansu ya kai ɗari huɗu.
And they gathered together to him every man of distress and every man whom [belonged] to him a creditor and every man bitter of soul and he became over them a commander and they were with him about four hundred man.
3 Daga can Dawuda ya tafi Mizfa a Mowab. Ya ce wa sarkin Mowab, “Za ka yarda mahaifina da mahaifiyata su zo su zauna a wurinka kafin in san abin da Allah zai yi da ni?”
And he went David from there Mizpah of Moab and he said - to [the] king of Moab let him go out please father my and mother my with you until that I will know what? will he do for me God.
4 Saboda haka ya bar su a wurin sarkin Mowab, suka zauna da shi duk tsawon lokacin da Dawuda yake ta ɓuya a kogwannin duwatsu.
And he led them with [the] presence of [the] king of Moab and they remained with him all [the] days of [the] being of David in the stronghold.
5 Amma annabin nan Gad ya ce wa Dawuda, “Kada ka zauna a nan, maza ka tashi ka shiga ƙasar Yahuda”. Sai Dawuda ya tashi ya tafi jejin Heret.
And he said Gad the prophet to David not you must remain in the stronghold go and you will go for yourself [the] land of Judah and he went David and he came [the] forest of Hereth.
6 Sai Shawulu ya sami labari cewa an ga Dawuda da mutanensa. Shawulu kuwa yana zaune da māshinsa kusa a ƙarƙashin itacen tsamiya a tudun Gibeya, tare da dukan ma’aikatansa kewaye da shi.
And he heard Saul that he was known David and [the] men who [were] with him and Saul [was] sitting at Gibeah under the tamarisk tree at the high place and spear his [was] in hand his and all servants his [were] standing with him.
7 Ya ce musu, “Mutanen Benyamin, ku saurara; ɗan Yesse zai iya ba dukanku filaye da gonakin inabi ne? Zai ba dukanku shugabanci na dubbai ko shugabanci na ɗari-ɗari?
And he said Saul to servants his who were standing with him listen please O Ben-jaminites also? to all of you will he give [the] son of Jesse fields and vineyards all of you will he appoint commanders of thousands and commanders of hundreds.
8 Abin da ya sa dukanku kuka gama baki a kaina? Ba wanda ya gaya mini lokacin da ɗana ya yi yarjejjeniya da ɗan Yesse, ba wanda ya kulla da ni, ko ya gaya mini cewa ɗana ya sa bawana yă tayar mini, yana fakona kamar yadda yake a yau.”
For you have conspired all of you on me and there not [is one who] opens ear my when made son my with [the] son of Jesse and not [was] feeling pain any of you on me and opening ear my that he has raised up son my servant my on me to an ambusher as the day this.
9 Amma Doyeg mutumin Edom da yake tsaye tare da fadawan Shawulu ya ce, “Na ga ɗan Yesse ya zo wurin Ahimelek ɗan Ahitub a Nob.
And he answered Doeg the Edomite and he [was] standing with [the] servants of Saul and he said I saw [the] son of Jesse coming Nob towards to Ahimelech [the] son of Ahitub.
10 Ahimelek ya roƙi Ubangiji saboda shi, ya kuma ba shi guzuri da takobin Goliyat Bafilistin.”
And he enquired for him by Yahweh and food he gave to him and [the] sword of Goliath the Philistine he gave to him.
11 Sai sarki ya aika aka kira masa Ahimelek firist ɗan Ahitub da dukan iyalin mahaifinsa. Dukansu suka zo wurin sarki.
And he sent the king to summon Ahimelech [the] son of Ahitub the priest and all [the] house of father his the priests who [were] at Nob and they came all of them to the king.
12 Shawulu ya ce, “Ka saurara yanzu, ɗan Ahitub.” Ya amsa ya ce, “Ina saurara, ranka yă daɗe.”
And he said Saul listen please O son of Ahitub and he said here [am] I O lord my.
13 Shawulu ya ce masa, “Don me ka gama baki da ɗan Yesse a kaina har ka ba shi burodi da takobin (Goliyat), ka kuma roƙi Allah don yă tayar mini, yă kuma yi fakona kamar yadda yake yi yau?”
And he said (to him *Q(k)*) Saul why? have you conspired on me you and [the] son of Jesse when giving you to him bread and a sword and [you] enquired for him by God to rise up against me to an ambusher as the day this.
14 Ahimelek ya ce wa sarki, “A cikin bayinka duka, wa ke da aminci iri na Dawuda, surukin sarki, shugaban jarumanka wanda ake girmamawa da gaske a gidanka?
And he answered Ahimelech the king and he said and who? among all servants your [is] like David faithful and [the] son-in-law of the king and [one who] turns aside to bodyguard your and honored in household your.
15 A wannan rana ce da na fara roƙon Allah saboda shi? Kada sarki yă zargi bawansa ko wani daga iyalin mahaifinsa, gama bawanka bai san kome a kan dukan waɗannan al’amura ba.”
This day did I begin? (to enquire *Q(k)*) for him by God far be it to me may not he put the king against servant his anything against all [the] house of father my for not he knew servant your in all this anything small or great.
16 Amma sarki ya ce, “Lalle Ahimelek za ka mutu, da kai da dukan iyalin mahaifinka.”
And he said the king certainly you will die O Ahimelech you and all [the] house of father your.
17 Sai sarki ya umarci matsaran da suke tsaye kusa da shi ya ce, “Ku kakkashe firistocin Ubangiji, gama su ma sun goyi bayan Dawuda. Sun san yana gudu, duk da haka ba su gaya mini ba.” Amma ma’aikatan sarki ba su yarda su sa hannu su kashe firistocin Ubangiji ba.
And he said the king to the runners who were standing with him turn round and put to death - [the] priests of Yahweh for also hand their [is] with David and for they knew that [was] fleeing he and not they uncovered (ear my *Q(K)*) and not they were willing [the] servants of the king to stretch out hand their to fall on [the] priests of Yahweh.
18 Sai sarki ya umarce Doyeg ya ce, “Ka juya ka kakkashe firistocin.” Doyeg mutumin Edom ya juya ya kakkashe firistocin. A ranar kuwa ya kashe mutum tamanin da biyar waɗanda suke sanye da efod na lilin.
And he said the king (to Doeg *Q(k)*) turn round you and fall on the priests and he turned round (Doeg *Q(k)*) the Edomite and he fell he on the priests and he killed - on the day that eighty and five man [who] carried an ephod of linen.
19 Ya kuma hallaka Nob birnin firistoci, ya kashe dukan mata, da maza, da yara, da jarirai, da shanu, da jakuna, da kuma tumaki.
And Nob [the] city of the priests he struck to [the] mouth of [the] sword from man and unto woman from child and unto suckling-child and ox[en] and donkey[s] and sheep to [the] mouth of [the] sword.
20 Amma Abiyatar ɗan Ahimelek jikan Ahitub ya tsere, ya gudu zuwa wurin Dawuda.
And he escaped a son one of Ahimelech [the] son of Ahitub and name his [was] Abiathar and he fled after David.
21 Abiyatar gaya wa Dawuda cewa, “Shawulu ya hallaka firistocin Ubangiji.”
And he told Abiathar to David that he had killed Saul [the] priests of Yahweh.
22 Dawuda ya ce wa Abiyatar, “Lalle a wancan ranar, sa’ad da na ga Doyeg mutumin Edom a can, na san tabbatacce zai gaya wa sarki. Ni ne sanadin mutuwar dukan iyalin mahaifinka.
And he said David to Abiathar I knew on the day that that [was] there (Doeg *Q(k)*) the Edomite that certainly he will tell to Saul I I have turned in every life of [the] house of father your.
23 Ka zauna tare da ni, kada ka ji tsoro mutumin da yake neman ranka, yana nema raina ma. Ka zauna lafiya tare da ni.”
Remain! with me may not you be afraid for [the one] who he seeks life my he seeks life your for [are] in good care you with me.

< 1 Sama’ila 22 >