< 1 Sama’ila 22 >
1 Dawuda ya bar Gat, ya tsere zuwa kogon Adullam. Da’yan’uwansa da kuma iyalan mahaifinsa suka ji labari, sai suka tafi can wurinsa.
David therefore departed from there, and escaped to the cave of Adullam. And when his brothers and all his father's house heard it, they went down there to him.
2 Dukan mutanen da suke cikin wahala, da waɗanda ake binsu bashi, da masu damuwoyi, suka tattaru a wurin Dawuda. Shi kuwa ya zama shugabansu. Yawansu ya kai ɗari huɗu.
And every man who was in distress, and every man who was in debt, and every man who was discontented, gathered themselves to him, and he became captain over them. And there were with him about four hundred men.
3 Daga can Dawuda ya tafi Mizfa a Mowab. Ya ce wa sarkin Mowab, “Za ka yarda mahaifina da mahaifiyata su zo su zauna a wurinka kafin in san abin da Allah zai yi da ni?”
And David went from there to Mizpeh of Moab, and he said to the king of Moab, Let my father and my mother, I pray thee, come forth, and be with you, till I know what God will do for me.
4 Saboda haka ya bar su a wurin sarkin Mowab, suka zauna da shi duk tsawon lokacin da Dawuda yake ta ɓuya a kogwannin duwatsu.
And he brought them before the king of Moab, and they dwelt with him all the while that David was in the stronghold.
5 Amma annabin nan Gad ya ce wa Dawuda, “Kada ka zauna a nan, maza ka tashi ka shiga ƙasar Yahuda”. Sai Dawuda ya tashi ya tafi jejin Heret.
And the prophet Gad said to David, Abide not in the stronghold. Depart, and get thee into the land of Judah. Then David departed, and came into the forest of Hereth.
6 Sai Shawulu ya sami labari cewa an ga Dawuda da mutanensa. Shawulu kuwa yana zaune da māshinsa kusa a ƙarƙashin itacen tsamiya a tudun Gibeya, tare da dukan ma’aikatansa kewaye da shi.
And Saul heard that David was discovered, and the men who were with him. Now Saul was sitting in Gibeah, under the tamarisk tree in Ramah with his spear in his hand, and all his servants were standing about him.
7 Ya ce musu, “Mutanen Benyamin, ku saurara; ɗan Yesse zai iya ba dukanku filaye da gonakin inabi ne? Zai ba dukanku shugabanci na dubbai ko shugabanci na ɗari-ɗari?
And Saul said to his servants who stood about him, Hear now, ye Benjamites. Will the son of Jesse give every one of you fields and vineyards? Will he make you all captains of thousands and captains of hundreds,
8 Abin da ya sa dukanku kuka gama baki a kaina? Ba wanda ya gaya mini lokacin da ɗana ya yi yarjejjeniya da ɗan Yesse, ba wanda ya kulla da ni, ko ya gaya mini cewa ɗana ya sa bawana yă tayar mini, yana fakona kamar yadda yake a yau.”
that all of you have conspired against me, and there is none who discloses to me when my son makes a league with the son of Jesse? And there is none of you who is sorry for me, or discloses to me that my son has stirred up my servant against me, to lie in wait, as at this day.
9 Amma Doyeg mutumin Edom da yake tsaye tare da fadawan Shawulu ya ce, “Na ga ɗan Yesse ya zo wurin Ahimelek ɗan Ahitub a Nob.
Then answered Doeg the Edomite, who stood by the servants of Saul, and said, I saw the son of Jesse coming to Nob, to Ahimelech the son of Ahitub.
10 Ahimelek ya roƙi Ubangiji saboda shi, ya kuma ba shi guzuri da takobin Goliyat Bafilistin.”
And he inquired of Jehovah for him, and gave him food, and gave him the sword of Goliath the Philistine.
11 Sai sarki ya aika aka kira masa Ahimelek firist ɗan Ahitub da dukan iyalin mahaifinsa. Dukansu suka zo wurin sarki.
Then the king sent to call Ahimelech the priest, the son of Ahitub, and all his father's house, the priests who were in Nob. And they came to the king, all of them.
12 Shawulu ya ce, “Ka saurara yanzu, ɗan Ahitub.” Ya amsa ya ce, “Ina saurara, ranka yă daɗe.”
And Saul said, Hear now, thou son of Ahitub. And he answered, Here I am, my lord.
13 Shawulu ya ce masa, “Don me ka gama baki da ɗan Yesse a kaina har ka ba shi burodi da takobin (Goliyat), ka kuma roƙi Allah don yă tayar mini, yă kuma yi fakona kamar yadda yake yi yau?”
And Saul said to him, Why have ye conspired against me, thou and the son of Jesse, in that thou have given him bread, and a sword, and have inquired of God for him, that he should rise against me to lie in wait as at this day?
14 Ahimelek ya ce wa sarki, “A cikin bayinka duka, wa ke da aminci iri na Dawuda, surukin sarki, shugaban jarumanka wanda ake girmamawa da gaske a gidanka?
Then Ahimelech answered the king, and said, And who among all thy servants is so faithful as David, who is the king's son-in-law, and is taken into thy council, and is honorable in thy house?
15 A wannan rana ce da na fara roƙon Allah saboda shi? Kada sarki yă zargi bawansa ko wani daga iyalin mahaifinsa, gama bawanka bai san kome a kan dukan waɗannan al’amura ba.”
Have I today begun to inquire of God for him? Be it far from me. Let not the king impute anything to his servant, nor to all the house of my father, for thy servant knows nothing of all this, less or more.
16 Amma sarki ya ce, “Lalle Ahimelek za ka mutu, da kai da dukan iyalin mahaifinka.”
And the king said, Thou shall surely die, Ahimelech, thou, and all thy father's house.
17 Sai sarki ya umarci matsaran da suke tsaye kusa da shi ya ce, “Ku kakkashe firistocin Ubangiji, gama su ma sun goyi bayan Dawuda. Sun san yana gudu, duk da haka ba su gaya mini ba.” Amma ma’aikatan sarki ba su yarda su sa hannu su kashe firistocin Ubangiji ba.
And the king said to the guard who stood about him, Turn, and kill the priests of Jehovah, because their hand also is with David, and because they knew that he fled, and did not disclose it to me. But the servants of the king would not put forth their hand to fall upon the priests of Jehovah.
18 Sai sarki ya umarce Doyeg ya ce, “Ka juya ka kakkashe firistocin.” Doyeg mutumin Edom ya juya ya kakkashe firistocin. A ranar kuwa ya kashe mutum tamanin da biyar waɗanda suke sanye da efod na lilin.
And the king said to Doeg, Turn thou, and fall upon the priests. And Doeg the Edomite turned, and he fell upon the priests, and he killed on that day eighty-five persons who wore a linen ephod.
19 Ya kuma hallaka Nob birnin firistoci, ya kashe dukan mata, da maza, da yara, da jarirai, da shanu, da jakuna, da kuma tumaki.
And Nob, the city of the priests, he smote with the edge of the sword, both men and women, sons and sucklings, and oxen and donkeys and sheep, with the edge of the sword.
20 Amma Abiyatar ɗan Ahimelek jikan Ahitub ya tsere, ya gudu zuwa wurin Dawuda.
And one of the sons of Ahimelech, the son of Ahitub, named Abiathar, escaped, and fled after David.
21 Abiyatar gaya wa Dawuda cewa, “Shawulu ya hallaka firistocin Ubangiji.”
And Abiathar told David that Saul had slain Jehovah's priests.
22 Dawuda ya ce wa Abiyatar, “Lalle a wancan ranar, sa’ad da na ga Doyeg mutumin Edom a can, na san tabbatacce zai gaya wa sarki. Ni ne sanadin mutuwar dukan iyalin mahaifinka.
And David said to Abiathar, I knew on that day, when Doeg the Edomite was there, that he would surely tell Saul. I have occasioned the death of all the persons of thy father's house.
23 Ka zauna tare da ni, kada ka ji tsoro mutumin da yake neman ranka, yana nema raina ma. Ka zauna lafiya tare da ni.”
Abide thou with me. Fear not, for he who seeks my life seeks thy life, for with me thou shall be in safeguard.