< 1 Sama’ila 21 >

1 Dawuda ya tafi Nob a wurin Ahimelek firist. Da Ahimelek ya gan shi sai ya firgita ya ce, “Me ya sa kai kaɗai ne? Me ya sa ba wani tare da kai?”
Potem je David prišel v Nob, k duhovniku Ahimélehu in Ahiméleh se je bal ob srečanju z Davidom in mu je rekel: »Zakaj si sam in ni nikogar s teboj?«
2 Dawuda ya ce wa Ahimelek firist, “Na zo aikin sarki ne, ya kuwa ce kada in sanar wa kowa abin da ya sa in yi. Na faɗa wa mutanena inda za su same ni.
David je rekel duhovniku Ahimélehu: »Kralj mi je zapovedal opravilo in mi rekel: ›Naj noben človek ne izve karkoli o opravilu, s katerim te pošiljam in kaj sem ti zapovedal in svoje služabnike sem določil na takšen in takšen kraj.‹
3 Yanzu, me kake da shi a hannu? Ka ba ni burodi guda biyar, ko wani abu da kake da shi a nan.”
Zdaj torej kaj je pod tvojo roko? Daj mi pet hlebov kruha v roko ali kar je prisotnega.«
4 Amma firist ya ce wa Dawuda, “Ba ni da burodi iri na kowa da kowa, sai dai akwai burodin da aka tsarkake. Za ka iya ɗauka ku ci idan mutanenka ba su kwana da mata ba.”
Duhovnik je Davidu odgovoril in rekel: » Tam ni običajnega kruha pod mojo roko, temveč je posvečen kruh, če so se vsaj mladeniči zadržali pred ženskami.«
5 Dawuda ya ce, “Lalle ne a keɓe muke daga mata. Mutanena sukan keɓe kansu a koyaushe suka tashi’yar tafiya, balle fa a yau!”
David je odgovoril duhovniku in mu rekel: »Resnično so bile ženske zadržane pred nami te tri dni, odkar sem prišel ven in posode mladeničev so svete in kruh je nekako običajen, da, kot bi bil ta dan posvečen v posodi.«
6 Don haka firist ya ba shi keɓaɓɓen burodi, tun da yake babu wani burodi a can sai dai burodin Kasancewa da aka cire daga gaban Ubangiji, aka sa burodi mai zafi a maimakon wanda aka cire a ranar.
Tako mu je duhovnik dal posvečenega kruha, kajti tam ni bilo kruha, razen hleba navzočnosti, kar je bilo vzeto izpred Gospoda, da se položi vroč kruh na dan, ko je bil ta vzet.
7 A ranar kuwa, ɗaya daga cikin bayin Shawulu yana can, a tsare a gaban Ubangiji, sunansa Doyeg, mutumin Edom, shugaban makiyayan Shawulu.
Torej nek mož izmed Savlovih služabnikov se je ta dan zadrževal tam pred Gospodom in njegovo ime je bilo Doég, Edómec, glavni izmed črednikov, ki so pripadali Savlu.
8 Dawuda ya ce wa Ahimelek, “Ba ka da māshi ko takobi a nan? Ban kawo māshina ko wani makami ba gama saƙon sarki ya zo mini da gaggawa.”
David je rekel Ahimélehu: »In ali ni tukaj pod tvojo roko sulica ali meč? Kajti s seboj nisem prinesel niti svojega meča niti svojih orožij, ker je kraljev posel zahteval naglico.«
9 Sai firist ya ce, “Takobin Goliyat Bafilistin nan wanda ka kashe a Kwarin Ela yana nan. An naɗe shi da ƙyallen aka ajiye a bayan Efod, in kana so, sai ka ɗauka. Ba wani takobi kuma sai wancan.” Dawuda ya ce, “Ba ni shi, ai, ba wani kamar sa.”
Duhovnik je rekel: »Meč Filistejca Goljata, ki si ga umoril v dolini Elá, glej, ta je tukaj, za efódom zavit v oblačilo. Če hočeš vzeti tega, ga vzemi, kajti nobenega drugega ni, razen tega tukaj.« David je rekel: »Nobenega ni podobnega temu; daj mi ga.«
10 A ranar, Dawuda ya gudu daga wajen Shawulu ya tafi wuri Akish sarkin Gat.
David se je vzdignil in tisti dan iz strahu pred Savlom pobegnil in šel k Ahíšu, kralju v Gatu.
11 Amma bayin Akish suka ce masa, “Wannan ba shi ne Dawuda sarkin ƙasar ba? Ashe, ba shi ne aka yi ta yin waƙoƙi a kansa, ana raye-raye, ana cewa, “Shawulu ya kashe dubbai, Dawuda kuwa ya kashe dubun dubbai?”
Ahíševi služabniki so mu rekli: » Ali ni to David, kralj dežele? Ali niso prepevale druga drugi o njem v plesih, rekoč: ›Savel je umoril svoje tisoče, David pa svoje deset tisoče?‹«
12 Dawuda ya riƙe waɗannan kalmomi a zuciyarsa, ya kuma ji tsoron Akish sarkin Gat sosai.
David si je te besede položil v svoje srce in se boleče bal Ahíša, kralja iz Gata.
13 Don haka sai ya yi kamar ya taɓu a gabansu. A duk lokacin da yake tare da su, sai yă yi kamar ya haukace. Ya yi ta zāne-zāne a ƙofofi, ya bar miyau yana ta bin gemunsa.
Pred njimi je spremenil svoje obnašanje in v njihovih rokah se je hlinil zmešanega in praskal po vhodih velikih vrat in si svojo slino pustil izlivati na svojo brado.
14 Akish ya ce wa bayinsa, “Duba, wannan mutum yana hauka. Me ya sa kuka kawo shi a wurina?
Potem je Ahíš rekel svojim služabnikom: »Glejte no! Vidite, človek je zmešan. Zakaj ste ga torej privedli k meni?
15 Na rasa masu hauka ne da za ku kawo mini wannan mutum yă yi ta hauka a gabana? Dole ne wannan mutum yă shiga gidana?”
Mar potrebujem zmešanih ljudi, da ste pripeljali tega pajdaša, da igra norca v moji prisotnosti? Ali naj ta pajdaš pride v mojo hišo?«

< 1 Sama’ila 21 >