< 1 Sama’ila 21 >

1 Dawuda ya tafi Nob a wurin Ahimelek firist. Da Ahimelek ya gan shi sai ya firgita ya ce, “Me ya sa kai kaɗai ne? Me ya sa ba wani tare da kai?”
David se rendit à Nob auprès du sacrificateur Achimélec. Achimélec vint à la rencontre de David en tremblant, et lui dit: « Pourquoi es-tu seul, et n'y a-t-il personne avec toi? ».
2 Dawuda ya ce wa Ahimelek firist, “Na zo aikin sarki ne, ya kuwa ce kada in sanar wa kowa abin da ya sa in yi. Na faɗa wa mutanena inda za su same ni.
David répondit au prêtre Achimélec: « Le roi m'a ordonné de faire quelque chose et m'a dit: « Que personne ne sache rien de l'affaire pour laquelle je t'envoie et de ce que je t'ai ordonné. J'ai envoyé les jeunes gens dans un certain lieu.
3 Yanzu, me kake da shi a hannu? Ka ba ni burodi guda biyar, ko wani abu da kake da shi a nan.”
Maintenant, qu'est-ce qui est sous ta main? Donnez-moi, je vous prie, cinq pains en main, ou tout ce qui est disponible. »
4 Amma firist ya ce wa Dawuda, “Ba ni da burodi iri na kowa da kowa, sai dai akwai burodin da aka tsarkake. Za ka iya ɗauka ku ci idan mutanenka ba su kwana da mata ba.”
Le prêtre répondit à David: « Je n'ai pas de pain ordinaire, mais il y a du pain saint, si seulement les jeunes gens se sont tenus à l'écart des femmes. »
5 Dawuda ya ce, “Lalle ne a keɓe muke daga mata. Mutanena sukan keɓe kansu a koyaushe suka tashi’yar tafiya, balle fa a yau!”
David prit la parole devant le prêtre et lui dit: « En vérité, les femmes ont été éloignées de nous comme d'habitude ces trois jours. Quand je suis sorti, les vases des jeunes gens étaient saints, bien que ce ne fût qu'un voyage ordinaire. Combien plus aujourd'hui leurs vases seront-ils saints? »
6 Don haka firist ya ba shi keɓaɓɓen burodi, tun da yake babu wani burodi a can sai dai burodin Kasancewa da aka cire daga gaban Ubangiji, aka sa burodi mai zafi a maimakon wanda aka cire a ranar.
Et le prêtre lui donna des pains saints; car il n'y avait là que le pain de démonstration qui avait été enlevé devant l'Éternel, pour être remplacé par du pain chaud le jour où il avait été enlevé.
7 A ranar kuwa, ɗaya daga cikin bayin Shawulu yana can, a tsare a gaban Ubangiji, sunansa Doyeg, mutumin Edom, shugaban makiyayan Shawulu.
Or un homme parmi les serviteurs de Saül était là ce jour-là, détenu devant l'Éternel; il s'appelait Doëg, l'Édomite, le meilleur des bergers qui appartenaient à Saül.
8 Dawuda ya ce wa Ahimelek, “Ba ka da māshi ko takobi a nan? Ban kawo māshina ko wani makami ba gama saƙon sarki ya zo mini da gaggawa.”
David dit à Achimélec: « N'y a-t-il pas ici sous ta main une lance ou une épée? Car je n'ai pas apporté avec moi mon épée ou mes armes, parce que les affaires du roi exigeaient la hâte. »
9 Sai firist ya ce, “Takobin Goliyat Bafilistin nan wanda ka kashe a Kwarin Ela yana nan. An naɗe shi da ƙyallen aka ajiye a bayan Efod, in kana so, sai ka ɗauka. Ba wani takobi kuma sai wancan.” Dawuda ya ce, “Ba ni shi, ai, ba wani kamar sa.”
Le prêtre dit: « Voici l'épée de Goliath le Philistin, que tu as tué dans la vallée d'Elah, et qui est ici enveloppée dans un tissu derrière l'éphod. Si tu veux la prendre, prends-la, car il n'y en a pas d'autre ici que celle-là. » David a dit: « Il n'y en a pas de semblable. Donne-le moi. »
10 A ranar, Dawuda ya gudu daga wajen Shawulu ya tafi wuri Akish sarkin Gat.
David se leva et s'enfuit ce jour-là par crainte de Saül, et il alla chez Akish, roi de Gath.
11 Amma bayin Akish suka ce masa, “Wannan ba shi ne Dawuda sarkin ƙasar ba? Ashe, ba shi ne aka yi ta yin waƙoƙi a kansa, ana raye-raye, ana cewa, “Shawulu ya kashe dubbai, Dawuda kuwa ya kashe dubun dubbai?”
Les serviteurs d'Akish lui dirent: « Ce David n'est-il pas le roi du pays? Ne chantaient-ils pas l'un l'autre à son sujet dans les danses, en disant, « Saül a tué ses milliers d'hommes, et David ses dix mille? »
12 Dawuda ya riƙe waɗannan kalmomi a zuciyarsa, ya kuma ji tsoron Akish sarkin Gat sosai.
David garda ces paroles dans son cœur, et il eut très peur d'Akish, roi de Gath.
13 Don haka sai ya yi kamar ya taɓu a gabansu. A duk lokacin da yake tare da su, sai yă yi kamar ya haukace. Ya yi ta zāne-zāne a ƙofofi, ya bar miyau yana ta bin gemunsa.
Il changea de comportement devant eux et fit semblant d'être fou entre leurs mains, il gribouilla sur les battants de la porte et laissa tomber ses crachats sur sa barbe.
14 Akish ya ce wa bayinsa, “Duba, wannan mutum yana hauka. Me ya sa kuka kawo shi a wurina?
Alors Akish dit à ses serviteurs: « Regardez, vous voyez que cet homme est fou. Pourquoi donc me l'amenez-vous?
15 Na rasa masu hauka ne da za ku kawo mini wannan mutum yă yi ta hauka a gabana? Dole ne wannan mutum yă shiga gidana?”
Est-ce que je manque de fous, pour que vous ayez amené cet homme pour qu'il fasse le fou en ma présence? Cet homme devrait-il entrer dans ma maison? »

< 1 Sama’ila 21 >