< 1 Sama’ila 21 >

1 Dawuda ya tafi Nob a wurin Ahimelek firist. Da Ahimelek ya gan shi sai ya firgita ya ce, “Me ya sa kai kaɗai ne? Me ya sa ba wani tare da kai?”
And David comes to Nob, to Ahimelech the priest, and Ahimelech trembles at meeting David and says to him, “Why [are] you alone, and no man [is] with you?”
2 Dawuda ya ce wa Ahimelek firist, “Na zo aikin sarki ne, ya kuwa ce kada in sanar wa kowa abin da ya sa in yi. Na faɗa wa mutanena inda za su same ni.
And David says to Ahimelech the priest, “The king has commanded me [on] a matter, and he says to me, Let no man know anything of the matter about which I send you, and which I have commanded you; and [my] young men know [to go] to such and such a place.
3 Yanzu, me kake da shi a hannu? Ka ba ni burodi guda biyar, ko wani abu da kake da shi a nan.”
And now, what is there under your hand? Give five loaves into my hand, or that which is found.”
4 Amma firist ya ce wa Dawuda, “Ba ni da burodi iri na kowa da kowa, sai dai akwai burodin da aka tsarkake. Za ka iya ɗauka ku ci idan mutanenka ba su kwana da mata ba.”
And the priest answers David and says, “There is no common bread under my hand, but there is holy bread; if only the youths have been kept from women.”
5 Dawuda ya ce, “Lalle ne a keɓe muke daga mata. Mutanena sukan keɓe kansu a koyaushe suka tashi’yar tafiya, balle fa a yau!”
And David answers the priest and says to him, “Surely, if women have been restrained from us as before in my going out, then the vessels of the young men are holy, and it [is] a common way; and also, surely it is sanctified today in the vessel.”
6 Don haka firist ya ba shi keɓaɓɓen burodi, tun da yake babu wani burodi a can sai dai burodin Kasancewa da aka cire daga gaban Ubangiji, aka sa burodi mai zafi a maimakon wanda aka cire a ranar.
And the priest gives the holy thing to him, for there was no bread there except the Bread of the Presentation, which is turned aside from the presence of YHWH to put hot bread [there] in the day of its being taken away.
7 A ranar kuwa, ɗaya daga cikin bayin Shawulu yana can, a tsare a gaban Ubangiji, sunansa Doyeg, mutumin Edom, shugaban makiyayan Shawulu.
And there [is] a man of the servants of Saul detained before YHWH on that day, and his name [is] Doeg the Edomite, chief of the shepherds whom Saul has.
8 Dawuda ya ce wa Ahimelek, “Ba ka da māshi ko takobi a nan? Ban kawo māshina ko wani makami ba gama saƙon sarki ya zo mini da gaggawa.”
And David says to Ahimelech, “And is there not spear or sword here under your hand? For I have taken neither my sword nor my vessels in my hand, for the matter of the king was urgent.”
9 Sai firist ya ce, “Takobin Goliyat Bafilistin nan wanda ka kashe a Kwarin Ela yana nan. An naɗe shi da ƙyallen aka ajiye a bayan Efod, in kana so, sai ka ɗauka. Ba wani takobi kuma sai wancan.” Dawuda ya ce, “Ba ni shi, ai, ba wani kamar sa.”
And the priest says, “The sword of Goliath the Philistine, whom you struck in the Valley of Elah, behold, it is wrapped in a garment behind the ephod, if you take it to yourself, take; for there is none other except it in this [place].” And David says, “There is none like it—give it to me.”
10 A ranar, Dawuda ya gudu daga wajen Shawulu ya tafi wuri Akish sarkin Gat.
And David rises and flees on that day from the face of Saul, and comes to Achish king of Gath;
11 Amma bayin Akish suka ce masa, “Wannan ba shi ne Dawuda sarkin ƙasar ba? Ashe, ba shi ne aka yi ta yin waƙoƙi a kansa, ana raye-raye, ana cewa, “Shawulu ya kashe dubbai, Dawuda kuwa ya kashe dubun dubbai?”
and the servants of Achish say to him, “Is this not David, the king of the land? Is it not of this one [that] they sing in dances, saying, Saul struck among his thousands, and David among his myriads?”
12 Dawuda ya riƙe waɗannan kalmomi a zuciyarsa, ya kuma ji tsoron Akish sarkin Gat sosai.
And David lays these words in his heart, and is exceedingly afraid of the face of Achish king of Gath,
13 Don haka sai ya yi kamar ya taɓu a gabansu. A duk lokacin da yake tare da su, sai yă yi kamar ya haukace. Ya yi ta zāne-zāne a ƙofofi, ya bar miyau yana ta bin gemunsa.
and changes his behavior before their eyes, and feigns himself mad in their hand, and scribbles on the doors of the gate, and lets down his spittle to his beard.
14 Akish ya ce wa bayinsa, “Duba, wannan mutum yana hauka. Me ya sa kuka kawo shi a wurina?
And Achish says to his servants, “Behold, you see a man acting as a madman; why do you bring him to me?
15 Na rasa masu hauka ne da za ku kawo mini wannan mutum yă yi ta hauka a gabana? Dole ne wannan mutum yă shiga gidana?”
Am I lacking madmen, that you have brought in this one to act as a madman before me? Does this one come into my house?”

< 1 Sama’ila 21 >