< 1 Sama’ila 21 >

1 Dawuda ya tafi Nob a wurin Ahimelek firist. Da Ahimelek ya gan shi sai ya firgita ya ce, “Me ya sa kai kaɗai ne? Me ya sa ba wani tare da kai?”
Then came David to Nob to Ahimelech the priest; and Ahimelech came to meet David trembling, and said unto him: 'Why art thou alone, and no man with thee?'
2 Dawuda ya ce wa Ahimelek firist, “Na zo aikin sarki ne, ya kuwa ce kada in sanar wa kowa abin da ya sa in yi. Na faɗa wa mutanena inda za su same ni.
And David said unto Ahimelech the priest: 'The king hath commanded me a business, and hath said unto me: Let no man know any thing of the business whereabout I send thee, and what I have commanded thee; and the young men have I appointed to such and such a place.
3 Yanzu, me kake da shi a hannu? Ka ba ni burodi guda biyar, ko wani abu da kake da shi a nan.”
Now therefore what is under thy hand? five loaves of bread? give them in my hand, or whatsoever there is present.'
4 Amma firist ya ce wa Dawuda, “Ba ni da burodi iri na kowa da kowa, sai dai akwai burodin da aka tsarkake. Za ka iya ɗauka ku ci idan mutanenka ba su kwana da mata ba.”
And the priest answered David, and said: 'There is no common bread under my hand, but there is holy bread; if only the young men have kept themselves from women.'
5 Dawuda ya ce, “Lalle ne a keɓe muke daga mata. Mutanena sukan keɓe kansu a koyaushe suka tashi’yar tafiya, balle fa a yau!”
And David answered the priest, and said unto him: 'Of a truth women have been kept from us about these three days; when I came out, the vessels of the young men were holy, though it was but a common journey; how much more then to-day, when there shall be holy bread in their vessels?'
6 Don haka firist ya ba shi keɓaɓɓen burodi, tun da yake babu wani burodi a can sai dai burodin Kasancewa da aka cire daga gaban Ubangiji, aka sa burodi mai zafi a maimakon wanda aka cire a ranar.
So the priest gave him holy bread; for there was no bread there but the showbread, that was taken from before the LORD, to put hot bread in the day when it was taken away. —
7 A ranar kuwa, ɗaya daga cikin bayin Shawulu yana can, a tsare a gaban Ubangiji, sunansa Doyeg, mutumin Edom, shugaban makiyayan Shawulu.
Now a certain man of the servants of Saul was there that day, detained before the LORD; and his name was Doeg the Edomite, the chiefest of the herdmen that belonged to Saul. —
8 Dawuda ya ce wa Ahimelek, “Ba ka da māshi ko takobi a nan? Ban kawo māshina ko wani makami ba gama saƙon sarki ya zo mini da gaggawa.”
And David said unto Ahimelech: 'And is there peradventure here under thy hand spear or sword? for I have neither brought my sword nor my weapons with me, because the king's business required haste.'
9 Sai firist ya ce, “Takobin Goliyat Bafilistin nan wanda ka kashe a Kwarin Ela yana nan. An naɗe shi da ƙyallen aka ajiye a bayan Efod, in kana so, sai ka ɗauka. Ba wani takobi kuma sai wancan.” Dawuda ya ce, “Ba ni shi, ai, ba wani kamar sa.”
And the priest said: 'The sword of Goliath the Philistine, whom thou slewest in the vale of Elah, behold, it is here wrapped in a cloth behind the ephod; if thou wilt take that, take it; for there is no other save that here.' And David said: 'There is none like that; give it me.'
10 A ranar, Dawuda ya gudu daga wajen Shawulu ya tafi wuri Akish sarkin Gat.
And David arose, and fled that day for fear of Saul, and went to Achish the king of Gath.
11 Amma bayin Akish suka ce masa, “Wannan ba shi ne Dawuda sarkin ƙasar ba? Ashe, ba shi ne aka yi ta yin waƙoƙi a kansa, ana raye-raye, ana cewa, “Shawulu ya kashe dubbai, Dawuda kuwa ya kashe dubun dubbai?”
And the servants of Achish said unto him: 'Is not this David the king of the land? Did they not sing one to another of him in dances, saying: Saul hath slain his thousands, and David his ten thousands?'
12 Dawuda ya riƙe waɗannan kalmomi a zuciyarsa, ya kuma ji tsoron Akish sarkin Gat sosai.
And David laid up these words in his heart, and was sore afraid of Achish the king of Gath.
13 Don haka sai ya yi kamar ya taɓu a gabansu. A duk lokacin da yake tare da su, sai yă yi kamar ya haukace. Ya yi ta zāne-zāne a ƙofofi, ya bar miyau yana ta bin gemunsa.
And he changed his demeanour before them, and feigned himself mad in their hands, and scrabbled on the doors of the gate, and let his spittle fall down upon his beard.
14 Akish ya ce wa bayinsa, “Duba, wannan mutum yana hauka. Me ya sa kuka kawo shi a wurina?
Then said Achish unto his servants: 'Lo, when ye see a man that is mad, wherefore do ye bring him to me?
15 Na rasa masu hauka ne da za ku kawo mini wannan mutum yă yi ta hauka a gabana? Dole ne wannan mutum yă shiga gidana?”
Do I lack madmen, that ye have brought this fellow to play the madman in my presence? shall this fellow come into my house?'

< 1 Sama’ila 21 >