< 1 Sama’ila 20 >
1 Sai Dawuda ya gudu daga Nayiwot a Rama ya je wurin Yonatan ya ce, “Me na yi? Wane laifi ne na yi? Ta wace hanya ce na yi wa mahaifinka laifi har da yake neman yă kashe ni?”
Et David s'enfuyant de Najoth qui est en Rama, s'en vint, et dit devant Jonathan: Qu'ai-je fait? Quelle est mon iniquité, et quel est mon péché devant ton père, qu'il recherche ma vie?
2 Yonatan ya ce, “Faufau, ba za ka mutu ba! Ka ji nan, mahaifina ba ya yin kome ba tare da ya shawarce da ni ba. Me ya sa ya ɓoye mini wannan? Ba zai yiwu ba.”
Et [Jonathan] lui dit: A Dieu ne plaise! tu ne mourras point. Voici, mon père ne fait aucune chose, ni grande, ni petite, qu'il ne me la découvre; et pourquoi mon père me cacherait-il cette chose-là? il n'en est rien.
3 Sai Dawuda ya rantse ya ce, “Mahaifinka ya san cewa, na sami tagomashi a gare ka, domin haka ba zai sanar maka da wannan ba, don kada yă baƙanta maka rai. Na rantse da Ubangiji, da kai kuma, taki ɗaya kaɗai ya rage tsakanina da mutuwa.”
Alors David jurant, dit encore: Ton père sait certainement que je suis dans tes bonnes grâces, et il aura dit: que Jonathan ne sache rien de ceci, de peur qu'il n'en soit attristé; mais l'Eternel est vivant, et ton âme vit, qu'il n'y a qu'un pas entre moi et la mort.
4 Sai Yonatan ya ce, “Duk abin da kake so in yi maka zan yi.”
Alors Jonathan dit à David: Que désires-tu que je fasse? Et je le ferai pour toi.
5 Dawuda ya ce, “Gobe fa shi ne Bikin Sabon Wata, ya kamata in ci tare da sarki amma bari in tafi fili in ɓuya har jibi da yamma.
Et David dit à Jonathan: Voici, c'est demain la nouvelle lune, et j'ai accoutumé de m'asseoir auprès du Roi pour manger, laisse-moi donc aller et je me cacherai aux champs, jusqu'au troisième soir.
6 In mahaifinka bai gan ni ba, ka gaya masa cewa, ‘Dawuda ya nemi izinina domin yă hanzarta yă tafi garinsa a Betlehem saboda ana hadaya ta shekara-shekara don dukan zuriyarsa.’
Si ton père vient à s'informer de moi, tu lui répondras: On m'a demandé instamment que David allât en diligence à Bethléhem sa ville, parce que toute sa famille fait un sacrifice solennel.
7 In ya yi na’am, to, bawanka ya tsira. Amma in ka ga ya damu, to, ka tabbata ya yi niyya yă kashe ni.
S'il dit ainsi: A la bonne heure; cela va bien pour ton serviteur. Mais s'il se met fort en colère, sache que sa malice est venue à son comble.
8 Kai kuma, ka nuna alheri ga bawanka, gama ka riga ka yi yarjejjeniya da ni a gaban Ubangiji, in kuwa na yi laifi ne sai ka kashe ni da kanka. Don me za ka bashe ni ga mahaifinka?”
Use donc de gratuité envers ton serviteur, puisque tu as fait entrer ton serviteur en alliance avec toi, [le nom de l'Eternel y étant intervenu]; que s'il y a [quelque] iniquité en moi, fais-moi mourir toi-même; car pourquoi me mènerais-tu à ton père?
9 Yonatan ya ce, “Labudda! In na ji ƙishin-ƙishin, cewa mahaifina yana neman yă kashe ka ashe, ba zan gaya maka ba?”
Et Jonathan lui dit: A Dieu ne plaise que cela t'arrive; car si je puis connaître en quelque sorte que la malice de mon père soit venue à son comble pour se décharger sur toi, ne te le ferai-je point savoir?
10 Dawuda ya ce, “Wa zai gaya mini idan mahaifinka ya amsa maka da amsa marar daɗi?”
Et David répondit à Jonathan: Qui me fera entendre quelle réponse fâcheuse t'aura faite ton père?
11 Yonatan ya ce, “Zo mu fita zuwa fili.” Sai suka tafi tare.
Et Jonathan dit à David: Viens et sortons aux champs. Ils sortirent donc eux deux aux champs.
12 Sai Yonatan ya ce wa Dawuda, “Na yi rantse da Ubangiji, Allah na Isra’ila cewa war haka jibi, zan yi ƙoƙari in ji daga mahaifina, idan ya yi magana mai kyau game da kai, zan gaya maka.
Alors Jonathan dit à David: Ô Eternel! Dieu d'Israël, quand j'aurai sondé mon père demain, environ cette heure ou après demain, et qu'il y aura du bien pour David, si alors je n'envoie vers toi, et si je ne te le découvre;
13 Amma in mahaifina ya sa zuciya yă cuce ka, Ubangiji yă hukunta ni da hukunci mai tsanani in ban gaya maka ba, in kuma sa ka ka tafi lafiya. Ubangiji yă kasance tare da kai kamar yadda ya kasance da mahaifina.
Que l'Eternel fasse ainsi à Jonathan, et ainsi y ajoute; que si mon père a résolu de te faire du mal, je te le ferai savoir, et je te laisserai aller, et tu t'en iras en paix, et l'Eternel sera avec toi comme il a été avec mon père.
14 Amma ka nuna mini alheri marar ƙarewa iri ta Ubangiji dukan rayuwata don kada a kashe ni.
Mais n'est-il pas ainsi, que si je suis encore vivant, n'est-il pas, dis-je ainsi, que tu useras envers moi de la gratuité de l'Eternel, en sorte que je ne meure point?
15 Kada kuma ka yanke alherinka ga iyalina ko da Ubangiji ya hallaka dukan maƙiyin Dawuda a duniya.”
Et que tu ne retireras point ta gratuité de ma maison à jamais, non pas même quand l'Eternel retranchera tous les ennemis de David de dessus la terre?
16 Saboda haka Yonatan ya yi yarjejjeniya da gidan Dawuda cewa Ubangiji yă kawo dukan maƙiyin Dawuda ga mutuwa.
Et Jonathan traita [alliance] avec la maison de David, [ en disant]: Que l'Eternel [le] redemande de la main des ennemis de David.
17 Yonatan kuwa ya sa Dawuda ya sāke tabbatar masa rantsuwansa game da abokantakarsa da shi, gama yana ƙaunar Dawuda kamar ransa.
Jonathan fit encore jurer David par l'amour qu'il lui portait; car il l'aimait autant que son âme.
18 Sai Yonatan ya gaya wa Dawuda cewa, “Gobe ne Bikin Sabon Wata, za a rasa ka, da yake kujerarka za tă kasance ba kowa a kai.
Puis Jonathan lui dit: C'est demain la nouvelle lune, et on s'informera de toi; car ta place sera vide.
19 Jibi wajajen yamma, ka tafi wurin da ka ɓuya lokacin da wannan matsala ta fara, ka tsaya kusa da dutsen Etsel.
Or ayant attendu jusqu'au troisième soir, tu descendras en diligence, et tu viendras au lieu où tu t'étais caché le jour de cette affaire, et tu demeureras auprès de la pierre d'Ezel.
20 Zan harbi kibiya uku ta wajen, sai ka ce dai ina harbin baka.
Et je tirerai trois flèches à côté de cette pierre, comme si je tirais à quelque but.
21 Sa’an nan zan aiki yaro in ce masa, ‘Je ka nemo kibiyoyin.’ In na ce masa, ‘Duba, kibiyoyin suna wannan gefen da kake, kawo su,’ sai ka fito, wato, tabbatacce muddin Ubangiji yana raye, ka tsira, ba wani hatsari.
Et voici, j'enverrai un garçon, [et je lui dirai]: Va, trouve les flèches. Et si je dis au garçon en termes exprès: Voilà, les flèches sont au deçà de toi, prends-les, et t'en viens; alors il va bien pour toi; et il n'y aura rien; l'Eternel est vivant.
22 Amma in na ce wa yaron, ‘Duba, kibiyoyin suna gaba da kai,’ sai ka tafi, gama Ubangiji ya sallame ka.
Mais si je dis ainsi au jeune garçon: Voilà, les flèches sont au delà de toi; va-t'en, car l'Eternel te renvoie.
23 Game da al’amarin da muka tattauna da ni da kai kuwa, ka tuna fa Ubangiji ne shaida tsakanina da kai har abada.”
Et quant à la parole que nous nous sommes donnée toi et moi; voici, l'Eternel est entre moi et toi à jamais.
24 Dawuda ya tafi ya ɓuya a fili. Sa’ad da ranar Bikin Sabon Wata ta zo, sarki ya zauna don yă ci.
David donc se cacha au champ; et la nouvelle lune étant venue, le Roi s'assit pour prendre son repas.
25 Ya zauna a kujeransa inda ya saba zama kusa da bango yana fuskantar Yonatan, Abner kuma ya zauna kusa da sarki. Amma kujeran Dawuda ba kowa.
Et le Roi s'étant assis en son siège, comme les autres fois, au siège qui était près de la paroi, Jonathan se leva, et Abner s'assit à côté de Saül; mais la place de David était vide.
26 Shawulu bai ce kome ba a ranar domin ya yi tsammani wataƙila wani abu ya faru da Dawuda ya mai da shi marar tsarki, tabbatacce ba shi da tsarki.
Et Saül n'en dit rien ce jour-là, car il disait en soi-même: Il lui est arrivé quelque chose; il n'est point net, certainement il n'est point net.
27 Amma kashegari, rana ta biyu ga wata, kujeran Dawuda kuma ba kowa, sai Shawulu ya ce wa ɗansa Yonatan, “Me ya sa ɗan Yesse bai zo cin abinci, jiya da yau ba?”
Mais le lendemain de la nouvelle lune, qui était le second [jour du mois], la place de David fut encore vide; et Saül dit à Jonathan son fils: Pourquoi le fils d'Isaï n'a-t-il été ni hier ni aujourd'hui au repas?
28 Yonatan ya ce, “Dawuda ya nemi izinina don yă tafi Betlehem.
Et Jonathan répondit à Saül: On m'a instamment prié que David allât jusqu'à Bethléhem.
29 Ya ce, ‘Bari in tafi gama iyalinmu suna miƙa hadaya a gari,’yan’uwana kuwa sun gayyace ni in kasance a can. In na sami yardarka, bari in tafi in ga’yan’uwana.’ Dalilin ke nan da bai zo ci da sarki ba.”
Même il m'a dit: Je te prie, laisse-moi aller; car notre famille fait un sacrifice en la ville, et mon frère m'a commandé [de m'y trouver]; maintenant donc si je suis dans tes bonnes grâces, je te prie que j'y aille, afin que je voie mes frères. C'est pour cela qu'il n'est point venu à la table du Roi.
30 Fushin Shawulu ya ƙuna a kan Yonatan, sai ya ce masa, “Kai shege ne, haihuwar banzan mace; ai, na san kana goyon bayan ɗan Yesse don ka wulaƙantar da kanka da mahaifinka.
Alors la colère de Saül s'enflamma contre Jonathan, et il lui dit: Fils de la méchante rebelle, ne sais-je pas bien que tu as choisi le fils d'Isaï à ta honte; et à la honte de la turpitude de ta mère?
31 Muddin ɗan Yesse yana da rai a duniya, ba za ka kahu ba. Sarautarka kuma ba za tă kahu ba. Yanzu sai ka je ka kawo mini shi. Dole yă mutu.”
Car tout le temps que le fils d'Isaï vivra sur la terre tu ne seras point établi, ni toi, ni ton Royaume; c'est pourquoi envoie sur l'heure, et amène-le moi, car il est digne de mort.
32 Yonatan ya ce wa mahaifinsa, “Me ya sa zai mutu? Me ya yi?”
Et Jonathan répondit à Saül son père, et lui dit: Pourquoi le ferait-on mourir? qu'a-t-il fait?
33 Amma Shawulu ya jefe shi da māshi don yă kashe shi. A nan ne Yonatan ya san lalle mahaifinsa ya yi niyya yă kashe Dawuda.
Et Saül lança une hallebarde contre lui pour le frapper. Alors Jonathan connut que son père avait conclu de faire mourir David.
34 Yonatan ya tashi daga tebur cin abincin da fushi. A rana ta biyun kuwa bai ci abinci ba, gama yana baƙin ciki game da rashin kunyar mahaifinsa game da Dawuda.
Et Jonathan se leva de table tout en colère, et ne prit point son repas le second jour de la nouvelle lune; car il était affligé à cause de David, parce que son père l'avait déshonoré.
35 Da safe Yonatan ya tafi domin yă sadu da Dawuda a fili. Ya tafi tare da wani ƙaramin yaro.
Et le [lendemain] matin Jonathan sortit aux champs, selon l'assignation qu'il avait donnée à David, et [il amena] avec lui un petit garçon.
36 Ya ce wa yaron, “Yi ruga da gudu ka nemo kibiyoyin da na harba.” Da yaron ya ruga sai ya harba kibiya a gaba da shi.
Et il dit à son garçon: Cours, trouve maintenant les flèches que je m'en vais tirer. Et le garçon courut, et [Jonathan] tira une flèche au delà de lui.
37 Da yaron ya isa wurin da kibiyan Yonatan ya fāɗi, Yonatan ya kira shi ya ce, “Kibiyan na gabanka fa.”
Et le garçon étant venu jusqu'au lieu où était la flèche que Jonathan avait tirée, Jonathan cria après lui, et lui dit: La flèche n'[est-]elle pas au delà de toi?
38 Sai ya tā da murya ya ce, “Maza, yi sauri kada ka tsaya.” Yaron ya ɗauko kibiya ya kawo wa maigidansa.
Et Jonathan criait après le garçon: Hâte-toi, ne t'arrête point; et le garçon amassa les flèches, et vint à son Seigneur.
39 (Yaron kuwa bai san kome game da wannan abu ba, sai Yonatan da Dawuda kawai.)
Mais le garçon ne savait rien de cette affaire; il n'y avait que David et Jonathan qui le sussent.
40 Yonatan ya ba wa yaron makaman ya ce, “Ka ɗauka ka koma gari.”
Et Jonathan donna son arc et ses flèches au garçon qu'il avait, et lui dit: Va, porte-les dans la ville.
41 Da yaron ya tafi, sai Dawuda ya tashi daga inda ya ɓuya kusa da tarin duwatsu, ya rusuna har sau uku. Sa’an nan suka sumbaci juna, suka yi kuka, Dawuda kuwa ya yi kuka sosai.
Et le garçon s'en étant allé, David se leva du côté du Midi, et se jeta le visage contre terre, et se prosterna par trois fois, et ils se baisèrent l'un l'autre, et pleurèrent tous deux; jusques-là que David pleura extraordinairement.
42 Yonatan ya ce wa Dawuda, “Sauka lafiya, mun riga mun yi rantsuwar abokantaka da juna a cikin sunan Ubangiji cewa, ‘Ubangiji ne shaida tsakanina da kai, tsakanin zuriyarka da zuriyata har abada.’” Sai Dawuda ya tafi, Yonatan kuwa ya koma gari.
Et Jonathan dit à David: Va-t'en en paix; selon que nous avons juré tous deux au Nom de l'Eternel, en disant: L'Eternel soit entre moi et toi, et entre ma postérité et ta postérité à jamais. David donc se leva, et s'en alla; et Jonathan rentra dans la ville.