< 1 Sama’ila 20 >
1 Sai Dawuda ya gudu daga Nayiwot a Rama ya je wurin Yonatan ya ce, “Me na yi? Wane laifi ne na yi? Ta wace hanya ce na yi wa mahaifinka laifi har da yake neman yă kashe ni?”
David s’enfuit de Naïot près de Rama et vint trouver Jonathan, à qui il dit: "Qu’ai-je fait à ton père, quel est mon tort, quelle est ma faute à son égard, pour qu’il en veuille à ma vie?"
2 Yonatan ya ce, “Faufau, ba za ka mutu ba! Ka ji nan, mahaifina ba ya yin kome ba tare da ya shawarce da ni ba. Me ya sa ya ɓoye mini wannan? Ba zai yiwu ba.”
"Oh! non, lui répondit-il, tu ne mourras point: mon père ne fait rien, ni grande ni petite chose, sans me l’avoir fait connaître; pourquoi donc m’aurait-il laissé ignorer ce dessein? Cela n’est pas."
3 Sai Dawuda ya rantse ya ce, “Mahaifinka ya san cewa, na sami tagomashi a gare ka, domin haka ba zai sanar maka da wannan ba, don kada yă baƙanta maka rai. Na rantse da Ubangiji, da kai kuma, taki ɗaya kaɗai ya rage tsakanina da mutuwa.”
David insista avec serment et dit: "Ton père sait bien que j’ai trouvé faveur à tes yeux, et il se sera dit: Que Jonathan n’en sache rien, il en serait affligé… Mais, certes, par le Dieu vivant et ta propre vie! Il n’y a qu’un pas entre moi et la mort."
4 Sai Yonatan ya ce, “Duk abin da kake so in yi maka zan yi.”
Jonathan dit à David: "Que veux-tu donc que je fasse pour toi?"
5 Dawuda ya ce, “Gobe fa shi ne Bikin Sabon Wata, ya kamata in ci tare da sarki amma bari in tafi fili in ɓuya har jibi da yamma.
David répondit à Jonathan: "C’Est demain la néoménie, et je dois être assis à table près du roi. Tu me permettras de m’absenter, et je me cacherai dans la campagne 'jusqu’au troisième soir.
6 In mahaifinka bai gan ni ba, ka gaya masa cewa, ‘Dawuda ya nemi izinina domin yă hanzarta yă tafi garinsa a Betlehem saboda ana hadaya ta shekara-shekara don dukan zuriyarsa.’
Si ton père remarque mon absence, tu diras: David m’a demandé la permission de courir à Bethléem, sa ville, où toute sa famille célèbre le sacrifice annuel.
7 In ya yi na’am, to, bawanka ya tsira. Amma in ka ga ya damu, to, ka tabbata ya yi niyya yă kashe ni.
Si alors il dit: Bon! C’Est le salut pour ton serviteur; mais s’il se met en colère, sache qu’il a résolu mon malheur.
8 Kai kuma, ka nuna alheri ga bawanka, gama ka riga ka yi yarjejjeniya da ni a gaban Ubangiji, in kuwa na yi laifi ne sai ka kashe ni da kanka. Don me za ka bashe ni ga mahaifinka?”
Tu agiras amicalement envers ton serviteur, car c’est dans une alliance divine que tu l’as fait entrer avec toi. Que si je suis en faute, fais-moi mourir toi-même, et pourquoi m’amènerais-tu à ton père?"
9 Yonatan ya ce, “Labudda! In na ji ƙishin-ƙishin, cewa mahaifina yana neman yă kashe ka ashe, ba zan gaya maka ba?”
Jonathan répondit: "Loin de toi cette pensée! Certes, si je savais ta perte arrêtée dans l’esprit de mon père, est-ce que je ne te le ferais pas savoir?"
10 Dawuda ya ce, “Wa zai gaya mini idan mahaifinka ya amsa maka da amsa marar daɗi?”
"Mais, dit David à Jonathan, qui m’avertira, si ton père t’adresse à toi-même une parole sévère?"
11 Yonatan ya ce, “Zo mu fita zuwa fili.” Sai suka tafi tare.
"Viens, dit Jonathan à David, sortons dans la campagne." Et tous deux s’en allèrent dans la campagne.
12 Sai Yonatan ya ce wa Dawuda, “Na yi rantse da Ubangiji, Allah na Isra’ila cewa war haka jibi, zan yi ƙoƙari in ji daga mahaifina, idan ya yi magana mai kyau game da kai, zan gaya maka.
Et Jonathan dit à David: "Par l’Eternel, Dieu d’Israël! Je sonderai mon père dans ces trois jours; s’il est bien disposé pour David, et si alors je ne te l’envoie pas révéler,
13 Amma in mahaifina ya sa zuciya yă cuce ka, Ubangiji yă hukunta ni da hukunci mai tsanani in ban gaya maka ba, in kuma sa ka ka tafi lafiya. Ubangiji yă kasance tare da kai kamar yadda ya kasance da mahaifina.
que le Seigneur en fasse tant et plus à Jonathan! Que si mon père se complaisait dans la pensée de te nuire, je te le révélerai, je te ferai partir, et tu t’en iras en paix; et que le Seigneur t’assiste comme il a assisté mon père!
14 Amma ka nuna mini alheri marar ƙarewa iri ta Ubangiji dukan rayuwata don kada a kashe ni.
Et puisses-tu, tant que je vivrai, puisses-tu m’être bienveillant au nom du Seigneur, pour que je ne meure point;
15 Kada kuma ka yanke alherinka ga iyalina ko da Ubangiji ya hallaka dukan maƙiyin Dawuda a duniya.”
et ne jamais retirer ta bienveillance à ma maison; pas même quand le Seigneur aura fait disparaître de la terre chacun des ennemis de David!"
16 Saboda haka Yonatan ya yi yarjejjeniya da gidan Dawuda cewa Ubangiji yă kawo dukan maƙiyin Dawuda ga mutuwa.
Ainsi Jonathan contracta ce pacte avec la maison de David: "Que Dieu demande compte du parjure aux ennemis de David!"
17 Yonatan kuwa ya sa Dawuda ya sāke tabbatar masa rantsuwansa game da abokantakarsa da shi, gama yana ƙaunar Dawuda kamar ransa.
Et Jonathan continua d’adjurer David au nom de son affection pour lui, car il l’aimait comme lui-même.
18 Sai Yonatan ya gaya wa Dawuda cewa, “Gobe ne Bikin Sabon Wata, za a rasa ka, da yake kujerarka za tă kasance ba kowa a kai.
Jonathan lui dit: "C’Est demain néoménie; ton absence sera remarquée, ta place étant vide.
19 Jibi wajajen yamma, ka tafi wurin da ka ɓuya lokacin da wannan matsala ta fara, ka tsaya kusa da dutsen Etsel.
Parvenu au troisième jour, tu t’enfonceras encore plus avant, jusqu’au lieu où tu étais caché le jour de l’événement, et tu attendras près de la pierre itinéraire.
20 Zan harbi kibiya uku ta wajen, sai ka ce dai ina harbin baka.
Moi, je lancerai trois flèches de ce côté, comme pour tirer à la cible;
21 Sa’an nan zan aiki yaro in ce masa, ‘Je ka nemo kibiyoyin.’ In na ce masa, ‘Duba, kibiyoyin suna wannan gefen da kake, kawo su,’ sai ka fito, wato, tabbatacce muddin Ubangiji yana raye, ka tsira, ba wani hatsari.
puis, j’enverrai le jeune esclave ramasser les flèches. Si je lui dis: Vois, les flèches sont en deçà de toi, prends-les! alors reviens, car il y aura sécurité pour toi et nul danger, par I’Eternel!
22 Amma in na ce wa yaron, ‘Duba, kibiyoyin suna gaba da kai,’ sai ka tafi, gama Ubangiji ya sallame ka.
Mais si je dis au jeune homme: Vois, les flèches sont en avant de toi, va-t-en, car le Seigneur veut ton départ.
23 Game da al’amarin da muka tattauna da ni da kai kuwa, ka tuna fa Ubangiji ne shaida tsakanina da kai har abada.”
Quant à la parole que nous avons échangée, toi et moi, l’Eternel en est, entre nous deux, l’immuable garant."
24 Dawuda ya tafi ya ɓuya a fili. Sa’ad da ranar Bikin Sabon Wata ta zo, sarki ya zauna don yă ci.
David resta caché dans la campagne. La néoménie venue, le roi se mit à table pour le repas.
25 Ya zauna a kujeransa inda ya saba zama kusa da bango yana fuskantar Yonatan, Abner kuma ya zauna kusa da sarki. Amma kujeran Dawuda ba kowa.
Le roi s’était assis à sa place, comme d’habitude sur son siège près du mur, Jonathan se tint debout, Abner prit place auprès de Saül, et le siège de David resta inoccupé.
26 Shawulu bai ce kome ba a ranar domin ya yi tsammani wataƙila wani abu ya faru da Dawuda ya mai da shi marar tsarki, tabbatacce ba shi da tsarki.
Saül ne fit aucune observation ce jour-là. Il se disait: "C’Est un accident. Il est sans doute impur, oui, il est impur!"
27 Amma kashegari, rana ta biyu ga wata, kujeran Dawuda kuma ba kowa, sai Shawulu ya ce wa ɗansa Yonatan, “Me ya sa ɗan Yesse bai zo cin abinci, jiya da yau ba?”
Mais le second jour de la néoménie, la place de David étant encore vacante, Saül dit à son fils Jonathan: "Pourquoi le fils de Jessé n’a-t-il paru ni hier ni aujourd’hui au repas?"
28 Yonatan ya ce, “Dawuda ya nemi izinina don yă tafi Betlehem.
Jonathan répondit à Saül: "C’Est que David m’a demandé la permission d’aller à Bethléem.
29 Ya ce, ‘Bari in tafi gama iyalinmu suna miƙa hadaya a gari,’yan’uwana kuwa sun gayyace ni in kasance a can. In na sami yardarka, bari in tafi in ga’yan’uwana.’ Dalilin ke nan da bai zo ci da sarki ba.”
Il a dit: Laisse-moi partir, car nous avons un banquet de famille dans la ville, et mon frère lui-même me l’a demandé. Si donc j’ai trouvé faveur à tes yeux, permets-moi de m’échapper pour visiter mes frères. C’Est pour cela qu’il n’est pas venu à la table du roi."
30 Fushin Shawulu ya ƙuna a kan Yonatan, sai ya ce masa, “Kai shege ne, haihuwar banzan mace; ai, na san kana goyon bayan ɗan Yesse don ka wulaƙantar da kanka da mahaifinka.
Saül se mit en colère contre Jonathan et lui dit: "Fils perfide et rebelle! Crois-tu que j’ignore que tu chéris le fils de Jessé, à ta honte et à la honte des flancs de ta mère?
31 Muddin ɗan Yesse yana da rai a duniya, ba za ka kahu ba. Sarautarka kuma ba za tă kahu ba. Yanzu sai ka je ka kawo mini shi. Dole yă mutu.”
Non, tant que le fils de Jessé sera vivant sur la terre, ni toi ni ta royauté ne pourrez subsister! Partant, ordonne qu’on me l’amène, car il a mérité la mort,"
32 Yonatan ya ce wa mahaifinsa, “Me ya sa zai mutu? Me ya yi?”
Répondant à Saül, son père, Jonathan lui dit: "Pourquoi serait-il mis à mort? Qu’a-t-il fait?"
33 Amma Shawulu ya jefe shi da māshi don yă kashe shi. A nan ne Yonatan ya san lalle mahaifinsa ya yi niyya yă kashe Dawuda.
Saül lança son javelot contre lui pour le frapper; Jonathan reconnut alors que son père avait résolu la mort de David.
34 Yonatan ya tashi daga tebur cin abincin da fushi. A rana ta biyun kuwa bai ci abinci ba, gama yana baƙin ciki game da rashin kunyar mahaifinsa game da Dawuda.
Jonathan se leva de table, exaspéré, et il ne prit aucune nourriture le jour de cette seconde néoménie, affligé qu’il était au sujet de David, parce que son père l’avait outragé.
35 Da safe Yonatan ya tafi domin yă sadu da Dawuda a fili. Ya tafi tare da wani ƙaramin yaro.
Le matin venu, Jonathan se rendit aux champs, à l’endroit convenu avec David; un jeune serviteur l’accompagnait.
36 Ya ce wa yaron, “Yi ruga da gudu ka nemo kibiyoyin da na harba.” Da yaron ya ruga sai ya harba kibiya a gaba da shi.
Il dit à son serviteur: "Cours ramasser, je te prie, les flèches que je lancerai." Le serviteur courut, mais lui, il lança les flèches de manière à le dépasser.
37 Da yaron ya isa wurin da kibiyan Yonatan ya fāɗi, Yonatan ya kira shi ya ce, “Kibiyan na gabanka fa.”
Comme le serviteur atteignit l’endroit où Jonathan avait dirigé les flèches, celui-ci lui cria: "Mais les flèches sont en avant de toi!"
38 Sai ya tā da murya ya ce, “Maza, yi sauri kada ka tsaya.” Yaron ya ɗauko kibiya ya kawo wa maigidansa.
Puis Jonathan cria au serviteur: "Vite, hâte-toi, ne t’arrête point!" Et le serviteur de Jonathan ramassa les flèches et revint vers son maître.
39 (Yaron kuwa bai san kome game da wannan abu ba, sai Yonatan da Dawuda kawai.)
Or, le serviteur ne s’était douté de rien; Jonathan et David seuls étaient d’intelligence.
40 Yonatan ya ba wa yaron makaman ya ce, “Ka ɗauka ka koma gari.”
Jonathan remit ses armes à son serviteur et lui dit: "Va, porte cela à la ville."
41 Da yaron ya tafi, sai Dawuda ya tashi daga inda ya ɓuya kusa da tarin duwatsu, ya rusuna har sau uku. Sa’an nan suka sumbaci juna, suka yi kuka, Dawuda kuwa ya yi kuka sosai.
Le serviteur parti, David vint du côté du midi, tomba la face contre terre et se prosterna trois fois. Ils s’embrassèrent et pleurèrent ensemble, David surtout versa d’abondantes larmes.
42 Yonatan ya ce wa Dawuda, “Sauka lafiya, mun riga mun yi rantsuwar abokantaka da juna a cikin sunan Ubangiji cewa, ‘Ubangiji ne shaida tsakanina da kai, tsakanin zuriyarka da zuriyata har abada.’” Sai Dawuda ya tafi, Yonatan kuwa ya koma gari.
Et Jonathan dit à David: "Va en paix, puisque nous nous sommes juré mutuellement au nom de l’Eternel, en disant: Que Dieu soit entre toi et moi, entre ta postérité et la mienne, à tout jamais!" Il se mit en route et partit, tandis que Jonathan retourna à la ville.