< 1 Sama’ila 20 >

1 Sai Dawuda ya gudu daga Nayiwot a Rama ya je wurin Yonatan ya ce, “Me na yi? Wane laifi ne na yi? Ta wace hanya ce na yi wa mahaifinka laifi har da yake neman yă kashe ni?”
And David fled from Nayoth near Ramah, and came and said before Jonathan, What have I done? what is my iniquity? and what is my sin before thy father, that he seeketh my life?
2 Yonatan ya ce, “Faufau, ba za ka mutu ba! Ka ji nan, mahaifina ba ya yin kome ba tare da ya shawarce da ni ba. Me ya sa ya ɓoye mini wannan? Ba zai yiwu ba.”
And he said unto him, God forbid; thou shalt not die: behold, my father is not wont to do a great thing or a small thing, which he doth not inform me of; and why should my father conceal this thing from me? it is not so.
3 Sai Dawuda ya rantse ya ce, “Mahaifinka ya san cewa, na sami tagomashi a gare ka, domin haka ba zai sanar maka da wannan ba, don kada yă baƙanta maka rai. Na rantse da Ubangiji, da kai kuma, taki ɗaya kaɗai ya rage tsakanina da mutuwa.”
But David swore again, and said, Thy father well knoweth that I have found grace in thy eyes; wherefore he said, Jonathan must not know this, lest he be grieved: nevertheless, as truly as the Lord liveth, and thy soul liveth, there was but one step between me and death.
4 Sai Yonatan ya ce, “Duk abin da kake so in yi maka zan yi.”
Then said Jonathan unto David, Whatsoever thy soul sayeth will I do for thee.
5 Dawuda ya ce, “Gobe fa shi ne Bikin Sabon Wata, ya kamata in ci tare da sarki amma bari in tafi fili in ɓuya har jibi da yamma.
And David said unto Jonathan, Behold, tomorrow is the new-moon, and I should as usual sit with the king to eat; but let me go, that I may hide myself in the field until the third evening.
6 In mahaifinka bai gan ni ba, ka gaya masa cewa, ‘Dawuda ya nemi izinina domin yă hanzarta yă tafi garinsa a Betlehem saboda ana hadaya ta shekara-shekara don dukan zuriyarsa.’
If thy father at all miss me, then do thou say, David asked earnestly leave of me that he might run to Beth-lechem his city; for there is a yearly sacrifice there for all the family.
7 In ya yi na’am, to, bawanka ya tsira. Amma in ka ga ya damu, to, ka tabbata ya yi niyya yă kashe ni.
If he should say thus, It is well: then shall thy servant have peace; but if it be at all displeasing to him, then know that the evil is determined on by him.
8 Kai kuma, ka nuna alheri ga bawanka, gama ka riga ka yi yarjejjeniya da ni a gaban Ubangiji, in kuwa na yi laifi ne sai ka kashe ni da kanka. Don me za ka bashe ni ga mahaifinka?”
And do thou deal kindly with thy servant; for into a covenant of the Lord hast thou brought thy servant with thee; but if there be in me any iniquity, slay me thyself; for why shouldst thou bring me to thy father?
9 Yonatan ya ce, “Labudda! In na ji ƙishin-ƙishin, cewa mahaifina yana neman yă kashe ka ashe, ba zan gaya maka ba?”
And Jonathan said, Far be it from thee; for if I should know for certain that evil were determined on by my father to come upon thee, would I not tell it thee?
10 Dawuda ya ce, “Wa zai gaya mini idan mahaifinka ya amsa maka da amsa marar daɗi?”
Then said David to Jonathan, Who shall tell it me? or what, if thy father answer thee roughly?
11 Yonatan ya ce, “Zo mu fita zuwa fili.” Sai suka tafi tare.
And Jonathan said unto David, Come, let us go out into the field. And they went out, both of them, into the field.
12 Sai Yonatan ya ce wa Dawuda, “Na yi rantse da Ubangiji, Allah na Isra’ila cewa war haka jibi, zan yi ƙoƙari in ji daga mahaifina, idan ya yi magana mai kyau game da kai, zan gaya maka.
And Jonathan said unto David, May the God of Israel [punish me] if, when I have sounded my father about this time tomorrow, or of the third day, and, behold, if he be good toward David, I do not then send unto thee, and inform thee of it.
13 Amma in mahaifina ya sa zuciya yă cuce ka, Ubangiji yă hukunta ni da hukunci mai tsanani in ban gaya maka ba, in kuma sa ka ka tafi lafiya. Ubangiji yă kasance tare da kai kamar yadda ya kasance da mahaifina.
May the Lord do so to Jonathan and continue so yet farther, that, if it please my father [to do] thee evil, I will inform thee of it, and send thee away, that thou mayest go in peace; and may the Lord be with thee, as he hath been with my father.
14 Amma ka nuna mini alheri marar ƙarewa iri ta Ubangiji dukan rayuwata don kada a kashe ni.
And wilt thou not, should I be yet alive, show me the kindness of the Lord, that I may not die?
15 Kada kuma ka yanke alherinka ga iyalina ko da Ubangiji ya hallaka dukan maƙiyin Dawuda a duniya.”
But, surely, thou wilt not withdraw thy kindness from my house for ever, not even when the Lord cutteth off the enemies of David, every one, from off the face of the earth.
16 Saboda haka Yonatan ya yi yarjejjeniya da gidan Dawuda cewa Ubangiji yă kawo dukan maƙiyin Dawuda ga mutuwa.
So Jonathan made a covenant with the house of David, [saying, ] May the Lord require it at the hand of David's enemies.
17 Yonatan kuwa ya sa Dawuda ya sāke tabbatar masa rantsuwansa game da abokantakarsa da shi, gama yana ƙaunar Dawuda kamar ransa.
And Jonathan caused David to swear again, by his love for him; for he loved him as he loved his own soul.
18 Sai Yonatan ya gaya wa Dawuda cewa, “Gobe ne Bikin Sabon Wata, za a rasa ka, da yake kujerarka za tă kasance ba kowa a kai.
Then Jonathan said to David, Tomorrow is the new-moon: and thou wilt be missed, because thy seat will be left empty.
19 Jibi wajajen yamma, ka tafi wurin da ka ɓuya lokacin da wannan matsala ta fara, ka tsaya kusa da dutsen Etsel.
And when thou hast stayed till the third day, then shalt thou go down greatly, and come to the place where thou didst hide thyself on the work-day; and thou shalt remain by the stone Ezel.
20 Zan harbi kibiya uku ta wajen, sai ka ce dai ina harbin baka.
And I will myself shoot three arrows on the side thereof, as though I were shooting at a mark.
21 Sa’an nan zan aiki yaro in ce masa, ‘Je ka nemo kibiyoyin.’ In na ce masa, ‘Duba, kibiyoyin suna wannan gefen da kake, kawo su,’ sai ka fito, wato, tabbatacce muddin Ubangiji yana raye, ka tsira, ba wani hatsari.
And, behold, I will send the lad, saying, Go, find the arrows; if I should now say unto the lad, Behold, the arrows are on this side of thee: then take him and come; for there is peace to thee, and it is nothing; as the Lord liveth.
22 Amma in na ce wa yaron, ‘Duba, kibiyoyin suna gaba da kai,’ sai ka tafi, gama Ubangiji ya sallame ka.
But if thus I should say unto the young man, Behold, the arrows are beyond thee: then go thy way, for the Lord hath sent thee off.
23 Game da al’amarin da muka tattauna da ni da kai kuwa, ka tuna fa Ubangiji ne shaida tsakanina da kai har abada.”
And touching the matter of which we have spoken, thou and I, behold, the Lord is between me and thee for ever.
24 Dawuda ya tafi ya ɓuya a fili. Sa’ad da ranar Bikin Sabon Wata ta zo, sarki ya zauna don yă ci.
So David hid himself in the field: and when the new-moon was come, the king set himself down to the repast to eat.
25 Ya zauna a kujeransa inda ya saba zama kusa da bango yana fuskantar Yonatan, Abner kuma ya zauna kusa da sarki. Amma kujeran Dawuda ba kowa.
And the king sat upon his seat, as at other times, upon the seat by the wall: and when Jonathan arose, Abner seated himself by the side of Saul, and David's place was left empty.
26 Shawulu bai ce kome ba a ranar domin ya yi tsammani wataƙila wani abu ya faru da Dawuda ya mai da shi marar tsarki, tabbatacce ba shi da tsarki.
Nevertheless Saul spoke not the least on that day; for he thought, Something hath befallen him, he is not clean; because he hath not yet purified himself.
27 Amma kashegari, rana ta biyu ga wata, kujeran Dawuda kuma ba kowa, sai Shawulu ya ce wa ɗansa Yonatan, “Me ya sa ɗan Yesse bai zo cin abinci, jiya da yau ba?”
And it came to pass on the morrow, the second day of the new-moon, that David's place was left empty; and Saul said unto Jonathan his son, Wherefore is the son of Jesse not come, both yesterday and today, to the repast?
28 Yonatan ya ce, “Dawuda ya nemi izinina don yă tafi Betlehem.
And Jonathan answered Saul, David asked earnestly leave of me to go as far as Beth-lechem.
29 Ya ce, ‘Bari in tafi gama iyalinmu suna miƙa hadaya a gari,’yan’uwana kuwa sun gayyace ni in kasance a can. In na sami yardarka, bari in tafi in ga’yan’uwana.’ Dalilin ke nan da bai zo ci da sarki ba.”
And he said, Let me go, I pray thee; for we have a family-sacrifice in the city, and my brother himself hath commanded it to me; and now, if I have found favor in thy eyes, let me get away, I pray thee, that I may see my brothers: therefore is he not come unto the king's table.
30 Fushin Shawulu ya ƙuna a kan Yonatan, sai ya ce masa, “Kai shege ne, haihuwar banzan mace; ai, na san kana goyon bayan ɗan Yesse don ka wulaƙantar da kanka da mahaifinka.
And the anger of Saul was kindled against Jonathan, and he said unto him, Thou son of perverse rebelliousness! do I not know that thou hast chosen the son of Jesse to thy own shame, and to the shame of thy mother's nakedness?
31 Muddin ɗan Yesse yana da rai a duniya, ba za ka kahu ba. Sarautarka kuma ba za tă kahu ba. Yanzu sai ka je ka kawo mini shi. Dole yă mutu.”
For all the days that the son of Jesse liveth upon the ground, thou wilt not have any permanence with thy kingdom: therefore now send and fetch him unto me, for he shall surely die.
32 Yonatan ya ce wa mahaifinsa, “Me ya sa zai mutu? Me ya yi?”
And Jonathan answered Saul his father, and said unto him, Wherefore shall he be put to death? what hath he done?
33 Amma Shawulu ya jefe shi da māshi don yă kashe shi. A nan ne Yonatan ya san lalle mahaifinsa ya yi niyya yă kashe Dawuda.
And Saul cast his spear at him to smite him: and Jonathan understood that it was determined on by his father to put David to death.
34 Yonatan ya tashi daga tebur cin abincin da fushi. A rana ta biyun kuwa bai ci abinci ba, gama yana baƙin ciki game da rashin kunyar mahaifinsa game da Dawuda.
And Jonathan arose from the table in fierce anger, and did eat no food on the second day of the new-moon; for he was grieved for David; because his father had made him feel ashamed.
35 Da safe Yonatan ya tafi domin yă sadu da Dawuda a fili. Ya tafi tare da wani ƙaramin yaro.
And it came to pass in the morning, that Jonathan went out into the field to the place appointed with David, and a little lad was with him.
36 Ya ce wa yaron, “Yi ruga da gudu ka nemo kibiyoyin da na harba.” Da yaron ya ruga sai ya harba kibiya a gaba da shi.
And he said unto his lad, Run, do find out the arrows which I shoot: and the lad ran, and he shot the arrow so as to pass beyond him.
37 Da yaron ya isa wurin da kibiyan Yonatan ya fāɗi, Yonatan ya kira shi ya ce, “Kibiyan na gabanka fa.”
And when the lad was come to the place of the arrow which Jonathan had shot, Jonathan called after the lad, and said, Behold, the arrow is beyond thee!
38 Sai ya tā da murya ya ce, “Maza, yi sauri kada ka tsaya.” Yaron ya ɗauko kibiya ya kawo wa maigidansa.
And Jonathan called after the lad, Make haste, speed, stay not: and Jonathan's lad gathered up the arrows, and came to his master.
39 (Yaron kuwa bai san kome game da wannan abu ba, sai Yonatan da Dawuda kawai.)
But the lad knew not the least: only Jonathan and David knew the matter.
40 Yonatan ya ba wa yaron makaman ya ce, “Ka ɗauka ka koma gari.”
And Jonathan gave his weapons unto the lad who was with him, and said unto him, Go, carry them to the city.
41 Da yaron ya tafi, sai Dawuda ya tashi daga inda ya ɓuya kusa da tarin duwatsu, ya rusuna har sau uku. Sa’an nan suka sumbaci juna, suka yi kuka, Dawuda kuwa ya yi kuka sosai.
And as soon as the lad was gone, David arose from the south side [of the stone], and fell on his face to the ground, and bowed himself three times: and they kissed one another, and wept one with another, until David exceeded.
42 Yonatan ya ce wa Dawuda, “Sauka lafiya, mun riga mun yi rantsuwar abokantaka da juna a cikin sunan Ubangiji cewa, ‘Ubangiji ne shaida tsakanina da kai, tsakanin zuriyarka da zuriyata har abada.’” Sai Dawuda ya tafi, Yonatan kuwa ya koma gari.
And Jonathan said to David, Go in peace: what we have sworn, both of us, in the name of the Lord, saying, The Lord shall be between me and thee, and between my seed and thy seed for ever, [shall be kept]. And he arose and departed; and Jonathan went into the city.

< 1 Sama’ila 20 >