< 1 Sama’ila 2 >

1 Sai Hannatu ta yi addu’a ta ce, “Zuciyata tana farin ciki a cikin Ubangiji; a cikin Ubangiji an sa ina jin daɗi ƙwarai. Na buɗe bakina na yi wa abokan gābana dariya. Kai! Ina murna domin ka cece ni!
Ana je molila in rekla: »Moje srce se razveseljuje v Gospodu, moj rog je povišan v Gospodu. Moja usta so povečana nad mojimi sovražniki, ker se veselim v tvoji rešitvi duše.
2 “Babu wani mai tsarki kamar Ubangiji babu wani, in ban da kai; babu wani dutse kamar Allahnmu.
Nihče ni svet kakor Gospod, kajti nikogar ni poleg tebe. Niti ni nobene skale, podobne našemu Bogu.
3 “Ka daina maganganu na girman kai ka kuma daina faɗin kalmomin ɗaga kai; gama Ubangiji Allah ne masani daga gare shi kuma ana auna ayyuka.
Ne govorite več tako silno ponosno, naj aroganca ne pride iz vaših ust, kajti Gospod je Bog spoznanja in pri njem so tehtana dejanja.
4 “An kakkarya bakkuna masu yaƙi, amma su da ka raunana an ba su makaman ƙarfi.
Loki mogočnih mož so zlomljeni in tisti, ki so se spotaknili, so opasani z močjo.
5 Waɗanda a dā suna da abinci sosai; yanzu suna ƙodago saboda abinci, masu fama da yunwa kuwa sun daina jin yunwa. Ita da take bakararriya, ta haifi’ya’ya bakwai amma ita da tana da’ya’ya da yawa, ta zama mai baƙin ciki.
Tisti, ki so bili siti, so se dali v najem zaradi kruha; tisti, ki so bili lačni, so oslabeli, tako, da je jalova rodila sedmero in tista, ki ima mnogo otrok, je postala slabotna.
6 “Ubangiji ne ke kawo mutuwa, yă kuma rayar yana kai ga kabari, yă kuma tā da. (Sheol h7585)
Gospod ubija in oživlja. Privede dol do groba in privede gor. (Sheol h7585)
7 Ubangiji ne yakan aika da talauci da kuma dukiya; yakan ƙasƙantar yă kuma ɗaukaka.
Gospod dela revne in dela bogate, ponižuje in povzdiguje.
8 Yakan tā da matalauci daga ƙura, yă kuma ɗaga mai bukata daga tarin toka; yă zaunar da su tare da’ya’yan sarki; yă kuma sa su gāji mulki na ɗaukaka. “Harsashin duniya na Ubangiji ne; a bisansu ne ya kafa duniya.
Revnega vzdiguje iz prahu in berača povzdiguje iz gnojišča, da ju posadi med prince in jima stori, da podedujeta prestol slave, kajti stebri zemlje so Gospodovi in nanje je postavil zemeljski [krog].
9 Zai kiyaye ƙafafun masu tsarki, amma mugaye za su lalace cikin duhu. “Ba bisa ga ƙarfi mutum ba ne mutum ke nasara;
Varoval bo stopala svojih svetih in zlobni bodo tiho v temi, kajti noben človek ne bo prevladal z močjo.
10 waɗanda suke gāba da Ubangiji za su hallaka. Zai yi musu tsawa daga sama, Ubangiji zai hukunta dukan duniya. “Zai ba wa sarkinsa ƙarfi, yă kuma ɗaukaka shafaffensa.”
Gospodovi nasprotniki bodo zlomljeni na koščke. Iz nebes bo zagrmel nad njimi. Gospod bo sodil konce zemlje; moč bo dal svojemu kralju in povišal rog svojega maziljenca.«
11 Sa’an nan, Elkana ya koma gida a Rama amma yaron ya yi hidima a gaban Ubangiji a ƙarƙashin Eli firist.
Elkaná je odšel v Ramo, k svoji hiši. Otrok pa je služil Gospodu pred duhovnikom Élijem.
12 ’Ya’yan Eli firist, mutane ne masu mugunta. Ba su ɗauki Ubangiji a bakin kome ba.
Torej Élijeva sinova sta bila Beliálova sinova; onadva nista poznala Gospoda.
13 Al’ada ce ga firistoci da mutane cewa in wani ya miƙa hadaya, yayinda nama yake kan wuta, bawan firist zai zo da babban cokali mai yatsu,
In običaj duhovnikov z ljudstvom je bil, da ko je katerikoli mož daroval klavno daritev, je prišel duhovnikov služabnik, medtem ko je meso vrelo, s kavljem za meso, s tremi zobmi, v svoji roki;
14 zai soka cokali mai yatsun a tukunyar, ko butar da ake dafan naman. Duk abin da cokali mai yatsun ya cako daga tukunyar, ya zama na firist. Haka aka yi ta yi wa Isra’ilawan da suka zo miƙa hadaya a Shilo.
in to zabodel v ponev ali kotliček ali kotel ali lonec; vse, kar so kavlji za meso prinesli gor, je duhovnik vzel zase. Tako sta počela v Šilu vsem Izraelcem, ki so prihajali tja.
15 Tun ma kafin a ƙona kitse, bawan firist yakan zo yă ce wa mutumin da yake miƙa hadaya, “Ka ba wa firist nama domin yă gasa, ba zai karɓi dafaffen nama daga wurinka ba, sai ɗanye.”
Tudi preden so sežgali tolščo, je prišel duhovnikov služabnik in rekel možu, ki je daroval: »Izroči meso za pečenje duhovniku, kajti od tebe ne bo imel kuhanega mesa, temveč surovega.«
16 In kuwa mutumin ya ce masa, “Bari kitse yă ƙone tukuna, sa’an nan ka ɗiba duk abin da kake so.” Sai bawan yă ce masa, “A’a, ka ba ni yanzu, in ka ƙi kuwa zan ɗiba ƙarfi da yaji.”
Če pa bi mu katerikoli moški rekel: »Naj ne izpustijo, da sedaj zažgejo tolščo, potem pa vzemi, kolikor si želi tvoja duša; « Potem bi mu odgovoril: » Ne, temveč mi boš to dal sedaj. Če pa ne, bom to vzel s silo.«
17 Wannan zunubin samarin ya yi muni ƙwarai a gaban Ubangiji, domin sun wulaƙanta hadayar Ubangiji, ƙwarai da gaske.
Zato je bil greh mladeničev zelo velik pred Gospodom, kajti moža sta prezirala Gospodovo daritev.
18 Amma yaron nan Sama’ila, yana hidima a gaban Ubangiji yana sanye da efod na lilin.
Toda Samuel je služil pred Gospodom, ko je bil še otrok, opasan z lanenim efódom.
19 Kowace shekara mahaifiyarsa takan ɗinka’yar taguwa ta kai masa sa’ad da ita da mijinta suka je miƙa hadaya ta shekara.
Poleg tega mu je mati iz leta v leto izdelala majhen plašč in ga prinesla k njemu, ko je prišla gor s svojim soprogom, da daruje letno klavno daritev.
20 Eli yakan sa wa Elkana da matarsa albarka, yă ce, Ubangiji yă ba ka waɗansu’ya’ya ta wurin matan nan, maimakon wanda ta roƙa daga Ubangiji, ta kuma ba da shi ga Ubangiji. Bayan haka sai su koma gida.
Éli je blagoslovil Elkaná in njegovo ženo ter rekel: » Gospod ti daj seme od te ženske, zaradi posojila, ki je posojen Gospodu.« In odšli so na svoj dom.
21 Hannatu kuwa ta sami alfarma daga Ubangiji. Ta yi ciki. Ana cikin haka Sama’ila kuwa sai girma yake ta yi a gaban Ubangiji.
Gospod je obiskal Ano, tako da je spočela in rodila [še] tri sinove in dve hčeri. Otrok Samuel pa je rasel pred Gospodom.
22 To, Eli kuwa ya tsufa ƙwarai, yana kuma jin labari duk abin da’ya’yansa suke yi wa dukan Isra’ila, da yadda suke lalata da matan da suke hidima a bakin ƙofar Tentin Sujada.
Torej Éli je bil zelo star in slišal vse, kar sta njegova sinova počela vsemu Izraelu in kako sta ležala z ženskami, ki so se zbirale pri vratih šotorskega svetišča skupnosti.
23 Saboda haka ya ce musu, “Don me kuke yin waɗannan abubuwa? Na sami labari daga wurin mutane a kan duk ayyukan muguntanku.
Rekel jima je: »Zakaj počneta takšne stvari? Kajti od vsega ljudstva slišim o vajinih zlih postopanjih.
24 A’a,’ya’yana ba labari mai kyau nake ji cikin mutanen Ubangiji ba.
Ne, moja sinova, kajti to ni dober glas, ki ga slišim. Vidva povzročata Gospodovemu ljudstvu, da greši.
25 In mutum ya yi wa wani laifi Allah yakan kāre shi; amma in mutum ya yi wa Ubangiji zunubi wa zai kāre shi?” Duk da haka,’ya’yansa ba su kula da gargaɗin mahaifinsu ba, domin nufin Ubangiji ne yă hallaka su.
Če en mož greši zoper drugega, ga bo sodil sodnik, toda če mož greši zoper Gospoda, kdo bo posredoval zanj.« Vendar nista prisluhnila glasu svojega očeta, ker ju je Gospod hotel ubiti.
26 Yaron nan Sama’ila ya dinga girma cikin kwarjini da cikin tagomashi a gaba Ubangiji da mutane.
Otrok Samuel pa je rasel in bil je v naklonjenosti tako z Gospodom kakor tudi z ljudmi.
27 Wani mutum ya zo wurin Eli ya ce masa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ashe ban bayana kaina sosai ga mahaifinka lokacin da yake a Masar a ƙarƙashin Fir’auna ba?
K Éliju je prišel Božji mož ter mu rekel: »Tako govori Gospod: ›Ali sem se očitno prikazal hiši tvojega očeta, ko so bili v Egiptu, v faraonovi hiši?
28 Na zaɓi mahaifinka daga cikin dukan kabilar Isra’ila yă zama firist nawa don yă yi hidima a bagade, don yă ƙona turare mai ƙanshi, don kuma yă sanya doguwar riga a gabana. Na kuma ba wa iyalin mahaifinka dukan hadaya ta ƙonawa da Isra’ila suka miƙa.
In ali sem ga izbral izmed vseh Izraelovih rodov, da bo moj duhovnik, da daruje na mojem oltarju, da zažiga kadilo, da nosi efód pred menoj? In ali sem dal hiši tvojega očeta vse daritve, narejene z ognjem, Izraelovih otrok?
29 Don me kuke rena hadayata da sadakokina da na ƙayyade domin mazaunina? Don me kake girmama’ya’yanka fiye da ni ta wurin cinye sashe mafi kyau na kowane hadayar da mutanena Isra’ila suka miƙa?’
Zakaj brcate ob mojo klavno daritev in ob mojo daritev, ki sem jo zapovedal v svojem prebivališču in svoja sinova bolj častiš kakor mene, da ste se odebelili z glavnimi izmed vseh daritev Izraela, mojega ljudstva?‹
30 “Saboda haka Ubangiji Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na yi alkawari cewa gidanka da gidan mahaifinka za su yi mini hidima a gabana har abada.’ Amma, yanzu Allah ya ce, ba zai yiwu ba; waɗanda suke girmama ni; Ni ma zan girmama su. Amma waɗanda suke ƙasƙantar da ni, haka za a ƙasƙantar da su.
Zato govori Gospod, Izraelov Bog: ›Zares sem rekel, da naj bi tvoja hiša in hiša tvojega očeta hodili pred menoj na veke.‹ Toda sedaj govori Gospod: ›To bodi daleč od mene, kajti tiste, ki spoštujejo mene, bom jaz spoštoval in tisti, ki me prezirajo, bodo prezirani.
31 Lokaci yana zuwa sa’ad da zan rage ƙarfinka da ƙarfin iyalin gidan mahaifinka. Domin kada a sāke samun tsohon mutum a zuriyarka.
Glej, pridejo dnevi, ko bom odsekal tvoj laket in laket hiše tvojega očeta, da v tvoji hiši ne bo starca.
32 Za ka zama da ɓacin rai a mazaunina ko da yake za a yi wa Isra’ila alheri. A zuriyarka ba za a taɓa samun tsohon mutum ba.
In ti boš videl sovražnika v mojem prebivališču v vsem bogastvu, ki ga bo Bog dal Izraelu, in v tvoji hiši na veke ne bo starca.
33 Kowannenku da ban kashe daga hidima a bagadena ba, za a bar shi don yă cika idanunka da hawaye da kuma baƙin ciki, dukan sauran zuriyarka kuwa za su mutu a ƙuruciyarsu.
Moški od tebe, ki ga ne bom odsekal izpred svojega oltarja, bo [preostal], da použije tvoje oči in da žalosti tvoje srce in ves narast tvoje hiše bo umrl v cvetu njihove starosti.
34 “‘Abin da kuma ya faru da’ya’yanka biyu Hofni da Finehas zai zama alama a gare ka; saboda mutuwarsu za tă zama a rana ɗaya.
To ti bo znamenje, ki bo prišlo nad tvoja dva sinova, na Hofníja in Pinhása; v enem dnevu bosta oba izmed njiju umrla.
35 Zan tayar wa kaina amintaccen firist wanda zai aikata abin da nake so yă yi, zan kuwa ba shi zuriya da koyaushe za su yi aiki a gaban zaɓaɓɓen sarkina.
Jaz pa si bom dvignil zvestega duhovnika, ki bo delal glede na to, kar je v mojem srcu in v mojem umu in zgradil mu bom zanesljivo hišo; in ta bo hodil pred mojim maziljencem na veke.
36 Sa’an nan duk wanda ya rage a zuriyarka zai zo yă durƙusa a gabansa yă roƙi kuɗi da abinci, zai kuma roƙa a yardar masa yă taimaki firistoci da aiki domin yă sami abin da zai ci.’”
Zgodilo se bo, da bo vsak, kdor preostane v tvoji hiši, prišel in klečeplazil k njemu za košček srebra in grižljaj kruha in rekel bo: ›Postavi me, prosim te, v eno izmed duhovniških služb, da bom lahko jedel kos kruha.‹«

< 1 Sama’ila 2 >