< 1 Sama’ila 2 >

1 Sai Hannatu ta yi addu’a ta ce, “Zuciyata tana farin ciki a cikin Ubangiji; a cikin Ubangiji an sa ina jin daɗi ƙwarai. Na buɗe bakina na yi wa abokan gābana dariya. Kai! Ina murna domin ka cece ni!
و حنا دعا نموده، گفت: «دل من در خداوند وجد می‌نماید. و شاخ من در نزد خداوند برافراشته شده. و دهانم بر دشمنانم وسیع گردیده است. زیرا که در نجات تو شادمان هستم.۱
2 “Babu wani mai tsarki kamar Ubangiji babu wani, in ban da kai; babu wani dutse kamar Allahnmu.
مثل یهوه قدوسی نیست. زیرا غیر از تو کسی نیست. و مثل خدای ما صخره‌ای نیست.۲
3 “Ka daina maganganu na girman kai ka kuma daina faɗin kalmomin ɗaga kai; gama Ubangiji Allah ne masani daga gare shi kuma ana auna ayyuka.
سخنان تکبرآمیز دیگر مگویید. و غرور از دهان شما صادر نشود. زیرا یهوه خدای علام است. وبه او اعمال، سنجیده می‌شود.۳
4 “An kakkarya bakkuna masu yaƙi, amma su da ka raunana an ba su makaman ƙarfi.
کمان جباران را شکسته است. و آنانی که می‌لغزیدند، کمر آنها به قوت بسته شد.۴
5 Waɗanda a dā suna da abinci sosai; yanzu suna ƙodago saboda abinci, masu fama da yunwa kuwa sun daina jin yunwa. Ita da take bakararriya, ta haifi’ya’ya bakwai amma ita da tana da’ya’ya da yawa, ta zama mai baƙin ciki.
سیرشدگان، خویشتن را برای نان اجیر ساختند. و کسانی که گرسنه بودند، استراحت یافتند. بلکه زن نازا هفت فرزند زاییده است. و آنکه اولادبسیار داشت، زبون گردیده.۵
6 “Ubangiji ne ke kawo mutuwa, yă kuma rayar yana kai ga kabari, yă kuma tā da. (Sheol h7585)
خداوند می‌میراند و زنده می‌کند؛ به قبر فرودمی آورد و برمی خیزاند. (Sheol h7585)۶
7 Ubangiji ne yakan aika da talauci da kuma dukiya; yakan ƙasƙantar yă kuma ɗaukaka.
خداوند فقیر می‌سازد و غنی می‌گرداند؛ پست می‌کند و بلند می‌سازد.۷
8 Yakan tā da matalauci daga ƙura, yă kuma ɗaga mai bukata daga tarin toka; yă zaunar da su tare da’ya’yan sarki; yă kuma sa su gāji mulki na ɗaukaka. “Harsashin duniya na Ubangiji ne; a bisansu ne ya kafa duniya.
فقیر را از خاک برمی افرازد. و مسکین را از مزبله برمی دارد تا ایشان را با امیران بنشاند. و ایشان راوارث کرسی جلال گرداند. زیرا که ستونهای زمین از آن خداوند است. و ربع مسکون را بر آنهااستوار نموده است.۸
9 Zai kiyaye ƙafafun masu tsarki, amma mugaye za su lalace cikin duhu. “Ba bisa ga ƙarfi mutum ba ne mutum ke nasara;
پایهای مقدسین خود را محفوظ می‌دارد. اماشریران در ظلمت خاموش خواهند شد، زیرا که انسان به قوت خود غالب نخواهد آمد.۹
10 waɗanda suke gāba da Ubangiji za su hallaka. Zai yi musu tsawa daga sama, Ubangiji zai hukunta dukan duniya. “Zai ba wa sarkinsa ƙarfi, yă kuma ɗaukaka shafaffensa.”
آنانی که با خداوند مخاصمه کنند، شکسته خواهند شد. او بر ایشان از آسمان صاعقه خواهدفرستاد. خداوند، اقصای زمین را داوری خواهدنمود، و به پادشاه خود قوت خواهد بخشید. وشاخ مسیح خود را بلند خواهد گردانید.»۱۰
11 Sa’an nan, Elkana ya koma gida a Rama amma yaron ya yi hidima a gaban Ubangiji a ƙarƙashin Eli firist.
پس القانه به خانه خود به راما رفت و آن پسر به حضور عیلی کاهن، خداوند را خدمت می‌نمود.۱۱
12 ’Ya’yan Eli firist, mutane ne masu mugunta. Ba su ɗauki Ubangiji a bakin kome ba.
و پسران عیلی از بنی بلیعال بودند وخداوند را نشناختند.۱۲
13 Al’ada ce ga firistoci da mutane cewa in wani ya miƙa hadaya, yayinda nama yake kan wuta, bawan firist zai zo da babban cokali mai yatsu,
و عادت کاهنان با قوم این بود که چون کسی قربانی می‌گذرانید هنگامی که گوشت پخته می‌شد، خادم کاهن با چنگال سه دندانه در دست خود می‌آمد۱۳
14 zai soka cokali mai yatsun a tukunyar, ko butar da ake dafan naman. Duk abin da cokali mai yatsun ya cako daga tukunyar, ya zama na firist. Haka aka yi ta yi wa Isra’ilawan da suka zo miƙa hadaya a Shilo.
و آن را به تاوه یامرجل یا دیگ یا پاتیل فرو برده، هر‌چه چنگال برمی آورد کاهن آن را برای خود می‌گرفت، وهمچنین با تمامی اسرائیل که در آنجا به شیلوه می‌آمدند، رفتار می‌نمودند.۱۴
15 Tun ma kafin a ƙona kitse, bawan firist yakan zo yă ce wa mutumin da yake miƙa hadaya, “Ka ba wa firist nama domin yă gasa, ba zai karɓi dafaffen nama daga wurinka ba, sai ɗanye.”
و نیز قبل ازسوزانیدن پیه، خادم کاهن آمده، به کسی‌که قربانی می‌گذرانید، می‌گفت: «گوشت به جهت کباب برای کاهن بده، زیرا گوشت پخته از تونمی گیرد بلکه خام.»۱۵
16 In kuwa mutumin ya ce masa, “Bari kitse yă ƙone tukuna, sa’an nan ka ɗiba duk abin da kake so.” Sai bawan yă ce masa, “A’a, ka ba ni yanzu, in ka ƙi kuwa zan ɗiba ƙarfi da yaji.”
و آن مرد به وی می‌گفت: «پیه را اول بسوزانند و بعد هر‌چه دلت می‌خواهدبرای خود بگیر.» او می‌گفت: «نی، بلکه الان بده، والا به زور می‌گیرم.»۱۶
17 Wannan zunubin samarin ya yi muni ƙwarai a gaban Ubangiji, domin sun wulaƙanta hadayar Ubangiji, ƙwarai da gaske.
پس گناهان آن جوانان به حضور خداوند بسیار عظیم بود، زیرا که مردمان هدایای خداوند را مکروه می‌داشتند.۱۷
18 Amma yaron nan Sama’ila, yana hidima a gaban Ubangiji yana sanye da efod na lilin.
و اما سموئیل به حضور خداوند خدمت می کرد، و او پسر کوچک بود و بر کمرش ایفودکتان بسته بود.۱۸
19 Kowace shekara mahaifiyarsa takan ɗinka’yar taguwa ta kai masa sa’ad da ita da mijinta suka je miƙa hadaya ta shekara.
و مادرش برای وی جبه کوچک می‌ساخت، و آن را سال به سال همراه خودمی آورد، هنگامی که با شوهر خود برمی آمد تاقربانی سالیانه را بگذرانند.۱۹
20 Eli yakan sa wa Elkana da matarsa albarka, yă ce, Ubangiji yă ba ka waɗansu’ya’ya ta wurin matan nan, maimakon wanda ta roƙa daga Ubangiji, ta kuma ba da shi ga Ubangiji. Bayan haka sai su koma gida.
و عیلی القانه وزنش را برکت داده، گفت: «خداوند تو را از این زن به عوض عاریتی که به خداوند داده‌ای، اولادبدهد.» پس به مکان خود رفتند.۲۰
21 Hannatu kuwa ta sami alfarma daga Ubangiji. Ta yi ciki. Ana cikin haka Sama’ila kuwa sai girma yake ta yi a gaban Ubangiji.
و خداوند از حنا تفقد نمود و او حامله شده، سه پسر و دو دختر زایید، و آن پسر، سموئیل به حضور خداوند نمو می‌کرد.۲۱
22 To, Eli kuwa ya tsufa ƙwarai, yana kuma jin labari duk abin da’ya’yansa suke yi wa dukan Isra’ila, da yadda suke lalata da matan da suke hidima a bakin ƙofar Tentin Sujada.
و عیلی بسیار سالخورده شده بود، و هر‌چه پسرانش با تمامی اسرائیل عمل می‌نمودند، می‌شنید، و اینکه چگونه با زنانی که نزد در خیمه اجتماع خدمت می‌کردند، می‌خوابیدند.۲۲
23 Saboda haka ya ce musu, “Don me kuke yin waɗannan abubuwa? Na sami labari daga wurin mutane a kan duk ayyukan muguntanku.
پس به ایشان گفت: «چرا چنین کارها می‌کنید زیرا که اعمال بد شما را از تمامی این قوم می‌شنوم.۲۳
24 A’a,’ya’yana ba labari mai kyau nake ji cikin mutanen Ubangiji ba.
چنین مکنید‌ای پسرانم زیرا خبری که می‌شنوم خوب نیست، شما باعث عصیان قوم خداوند می‌باشید.۲۴
25 In mutum ya yi wa wani laifi Allah yakan kāre shi; amma in mutum ya yi wa Ubangiji zunubi wa zai kāre shi?” Duk da haka,’ya’yansa ba su kula da gargaɗin mahaifinsu ba, domin nufin Ubangiji ne yă hallaka su.
اگر شخصی بر شخصی گناه ورزد خدا او را داوری خواهد کرد اما اگرشخصی بر خداوند گناه ورزد، کیست که برای وی شفاعت نماید؟» اما ایشان سخن پدر خود رانشنیدند، زیرا خداوند خواست که ایشان راهلاک سازد.۲۵
26 Yaron nan Sama’ila ya dinga girma cikin kwarjini da cikin tagomashi a gaba Ubangiji da mutane.
و آن پسر، سموئیل، نمو می‌یافت و هم نزدخداوند و هم نزد مردمان پسندیده می‌شد.۲۶
27 Wani mutum ya zo wurin Eli ya ce masa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ashe ban bayana kaina sosai ga mahaifinka lokacin da yake a Masar a ƙarƙashin Fir’auna ba?
و مرد خدایی نزد عیلی آمده، به وی گفت: «خداوند چنین می‌گوید: آیا خود را بر خاندان پدرت هنگامی که ایشان در مصر در خانه فرعون بودند، ظاهر نساختم؟۲۷
28 Na zaɓi mahaifinka daga cikin dukan kabilar Isra’ila yă zama firist nawa don yă yi hidima a bagade, don yă ƙona turare mai ƙanshi, don kuma yă sanya doguwar riga a gabana. Na kuma ba wa iyalin mahaifinka dukan hadaya ta ƙonawa da Isra’ila suka miƙa.
و آیا او را از جمیع اسباط اسرائیل برنگزیدم تا کاهن من بوده، نزدمذبح من بیاید. و بخور بسوزاند و به حضور من ایفود بپوشد، وآیا جمیع هدایای آتشین بنی‌اسرائیل را به خاندان پدرت نبخشیدم؟۲۸
29 Don me kuke rena hadayata da sadakokina da na ƙayyade domin mazaunina? Don me kake girmama’ya’yanka fiye da ni ta wurin cinye sashe mafi kyau na kowane hadayar da mutanena Isra’ila suka miƙa?’
پس چرا قربانی‌ها و هدایای مرا که در مسکن خود امر فرمودم، پایمال می‌کنید و پسران خود رازیاده از من محترم می‌داری، تا خویشتن را ازنیکوترین جمیع هدایای قوم من، اسرائیل فربه سازی.۲۹
30 “Saboda haka Ubangiji Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na yi alkawari cewa gidanka da gidan mahaifinka za su yi mini hidima a gabana har abada.’ Amma, yanzu Allah ya ce, ba zai yiwu ba; waɗanda suke girmama ni; Ni ma zan girmama su. Amma waɗanda suke ƙasƙantar da ni, haka za a ƙasƙantar da su.
بنابراین یهوه، خدای اسرائیل می‌گوید: البته گفتم که خاندان تو و خاندان پدرت به حضور من تا به ابد سلوک خواهند نمود، لیکن الان خداوند می‌گوید: حاشا از من! زیرا آنانی که مرا تکریم نمایند، تکریم خواهم نمود و کسانی که مرا حقیر شمارند، خوار خواهند شد.۳۰
31 Lokaci yana zuwa sa’ad da zan rage ƙarfinka da ƙarfin iyalin gidan mahaifinka. Domin kada a sāke samun tsohon mutum a zuriyarka.
اینک ایامی می‌آید که بازوی تو را و بازوی خاندان پدرتو را قطع خواهم نمود که مردی پیر در خانه تویافت نشود.۳۱
32 Za ka zama da ɓacin rai a mazaunina ko da yake za a yi wa Isra’ila alheri. A zuriyarka ba za a taɓa samun tsohon mutum ba.
و تنگی مسکن مرا خواهی دید، در هر احسانی که به اسرائیل خواهد شد، و مردی پیر در خانه تو ابد نخواهد بود.۳۲
33 Kowannenku da ban kashe daga hidima a bagadena ba, za a bar shi don yă cika idanunka da hawaye da kuma baƙin ciki, dukan sauran zuriyarka kuwa za su mutu a ƙuruciyarsu.
و شخصی رااز کسان تو که از مذبح خود قطع نمی نمایم برای کاهیدن چشم تو و رنجانیدن دلت خواهد بود، وجمیع ذریت خانه تو در جوانی خواهند مرد.۳۳
34 “‘Abin da kuma ya faru da’ya’yanka biyu Hofni da Finehas zai zama alama a gare ka; saboda mutuwarsu za tă zama a rana ɗaya.
واین برای تو علامت باشد که بر دو پسرت حفنی وفینحاس واقع می‌شود که هر دوی ایشان در یک روز خواهند مرد.۳۴
35 Zan tayar wa kaina amintaccen firist wanda zai aikata abin da nake so yă yi, zan kuwa ba shi zuriya da koyaushe za su yi aiki a gaban zaɓaɓɓen sarkina.
و کاهن امینی به جهت خودبرپا خواهم داشت که موافق دل و جان من رفتارخواهد نمود، و برای او خانه مستحکمی بنا خواهم کرد، و به حضور مسیح من پیوسته سلوک خواهد نمود.۳۵
36 Sa’an nan duk wanda ya rage a zuriyarka zai zo yă durƙusa a gabansa yă roƙi kuɗi da abinci, zai kuma roƙa a yardar masa yă taimaki firistoci da aiki domin yă sami abin da zai ci.’”
و واقع خواهد شد که هر‌که درخانه تو باقی ماند، آمده، نزد او به جهت پاره‌ای نقره و قرص نانی تعظیم خواهد نمود و خواهدگفت: تمنا اینکه مرا به یکی از وظایف کهانت بگذار تا لقمه‌ای نان بخورم.»۳۶

< 1 Sama’ila 2 >