< 1 Sama’ila 2 >
1 Sai Hannatu ta yi addu’a ta ce, “Zuciyata tana farin ciki a cikin Ubangiji; a cikin Ubangiji an sa ina jin daɗi ƙwarai. Na buɗe bakina na yi wa abokan gābana dariya. Kai! Ina murna domin ka cece ni!
Hannah prayed and said, “My heart exults in Yahweh. My horn is exalted in Yahweh. My mouth boasts over my enemies, because I rejoice in your salvation.
2 “Babu wani mai tsarki kamar Ubangiji babu wani, in ban da kai; babu wani dutse kamar Allahnmu.
There is no one holy like Yahweh, for there is none besides you; there is no rock like our God.
3 “Ka daina maganganu na girman kai ka kuma daina faɗin kalmomin ɗaga kai; gama Ubangiji Allah ne masani daga gare shi kuma ana auna ayyuka.
Boast no more so very proudly; let no arrogance come out of your mouth. For Yahweh is a God of knowledge; by him actions are weighed.
4 “An kakkarya bakkuna masu yaƙi, amma su da ka raunana an ba su makaman ƙarfi.
The bow of the mighty men are broken, but those who stumble put on strength like a belt.
5 Waɗanda a dā suna da abinci sosai; yanzu suna ƙodago saboda abinci, masu fama da yunwa kuwa sun daina jin yunwa. Ita da take bakararriya, ta haifi’ya’ya bakwai amma ita da tana da’ya’ya da yawa, ta zama mai baƙin ciki.
Those who were full have hired themselves out for bread; those who were hungry have stopped being hungry. Even the barren one gives birth to seven, but the woman who has many children languishes.
6 “Ubangiji ne ke kawo mutuwa, yă kuma rayar yana kai ga kabari, yă kuma tā da. (Sheol )
Yahweh kills and brings to life. He brings down to Sheol and raises up. (Sheol )
7 Ubangiji ne yakan aika da talauci da kuma dukiya; yakan ƙasƙantar yă kuma ɗaukaka.
Yahweh makes some people poor and some rich. He humbles, but he also lifts up.
8 Yakan tā da matalauci daga ƙura, yă kuma ɗaga mai bukata daga tarin toka; yă zaunar da su tare da’ya’yan sarki; yă kuma sa su gāji mulki na ɗaukaka. “Harsashin duniya na Ubangiji ne; a bisansu ne ya kafa duniya.
He raises up the poor out of the dust. He lifts the needy from the ash heap to make them sit with princes and inherit the seat of honor. For the pillars of the earth are Yahweh's and he has set the world upon them.
9 Zai kiyaye ƙafafun masu tsarki, amma mugaye za su lalace cikin duhu. “Ba bisa ga ƙarfi mutum ba ne mutum ke nasara;
He will guard the feet of his faithful people, but the wicked will be put to silence in darkness, for no one will prevail by strength.
10 waɗanda suke gāba da Ubangiji za su hallaka. Zai yi musu tsawa daga sama, Ubangiji zai hukunta dukan duniya. “Zai ba wa sarkinsa ƙarfi, yă kuma ɗaukaka shafaffensa.”
Those who oppose Yahweh will be broken to pieces; he will thunder against them from heaven. Yahweh will judge the ends of the earth; he will give strength to his king and exalt the horn of his anointed.”
11 Sa’an nan, Elkana ya koma gida a Rama amma yaron ya yi hidima a gaban Ubangiji a ƙarƙashin Eli firist.
Then Elkanah went to Ramah, to his house. The child served Yahweh in the presence of Eli the priest.
12 ’Ya’yan Eli firist, mutane ne masu mugunta. Ba su ɗauki Ubangiji a bakin kome ba.
Now the sons of Eli were worthless men. They did not know Yahweh.
13 Al’ada ce ga firistoci da mutane cewa in wani ya miƙa hadaya, yayinda nama yake kan wuta, bawan firist zai zo da babban cokali mai yatsu,
The custom of the priests with the people was that when any man offered a sacrifice, the priest's servant would come with a three-pronged fork in his hand, while the meat was boiling.
14 zai soka cokali mai yatsun a tukunyar, ko butar da ake dafan naman. Duk abin da cokali mai yatsun ya cako daga tukunyar, ya zama na firist. Haka aka yi ta yi wa Isra’ilawan da suka zo miƙa hadaya a Shilo.
He would stick it into the pan, or kettle, or cauldron, or pot. All that the fork brought up the priest would take for himself. They did this in Shiloh with all the Israelites that came there.
15 Tun ma kafin a ƙona kitse, bawan firist yakan zo yă ce wa mutumin da yake miƙa hadaya, “Ka ba wa firist nama domin yă gasa, ba zai karɓi dafaffen nama daga wurinka ba, sai ɗanye.”
Worse, before they burned the fat, the priest's servant came, and said to the man who was sacrificing, “Give meat to roast for the priest; for he will not accept boiled meat from you, but only raw.”
16 In kuwa mutumin ya ce masa, “Bari kitse yă ƙone tukuna, sa’an nan ka ɗiba duk abin da kake so.” Sai bawan yă ce masa, “A’a, ka ba ni yanzu, in ka ƙi kuwa zan ɗiba ƙarfi da yaji.”
If the man said to him, “They must burn the fat first, and then take as much as you want.” Then he would say, “No, you will give it me now; if not, I will take it by force.”
17 Wannan zunubin samarin ya yi muni ƙwarai a gaban Ubangiji, domin sun wulaƙanta hadayar Ubangiji, ƙwarai da gaske.
The sin of these young men was very great before Yahweh, for they despised Yahweh's offering.
18 Amma yaron nan Sama’ila, yana hidima a gaban Ubangiji yana sanye da efod na lilin.
But Samuel served Yahweh as a child clothed with a linen ephod.
19 Kowace shekara mahaifiyarsa takan ɗinka’yar taguwa ta kai masa sa’ad da ita da mijinta suka je miƙa hadaya ta shekara.
His mother would make him a little robe and bring it to him from year to year, when she came up with her husband to offer the yearly sacrifice.
20 Eli yakan sa wa Elkana da matarsa albarka, yă ce, Ubangiji yă ba ka waɗansu’ya’ya ta wurin matan nan, maimakon wanda ta roƙa daga Ubangiji, ta kuma ba da shi ga Ubangiji. Bayan haka sai su koma gida.
Eli would bless Elkanah and his wife and say, “May Yahweh give you more children by this woman because of the request she made of Yahweh.” Then they would return to their own home.
21 Hannatu kuwa ta sami alfarma daga Ubangiji. Ta yi ciki. Ana cikin haka Sama’ila kuwa sai girma yake ta yi a gaban Ubangiji.
Yahweh again helped Hannah, and again she became pregnant. She bore three sons and two daughters. Meanwhile, the child Samuel grew before Yahweh.
22 To, Eli kuwa ya tsufa ƙwarai, yana kuma jin labari duk abin da’ya’yansa suke yi wa dukan Isra’ila, da yadda suke lalata da matan da suke hidima a bakin ƙofar Tentin Sujada.
Now Eli was very old; he heard all that his sons were doing to all Israel, and how they slept with the women who served at the entrance to the tent of meeting.
23 Saboda haka ya ce musu, “Don me kuke yin waɗannan abubuwa? Na sami labari daga wurin mutane a kan duk ayyukan muguntanku.
He said to them, “Why do you such things? For I hear of your evil actions from all these people.”
24 A’a,’ya’yana ba labari mai kyau nake ji cikin mutanen Ubangiji ba.
No, my sons; for it is not a good report that I hear. You make Yahweh's people disobey.
25 In mutum ya yi wa wani laifi Allah yakan kāre shi; amma in mutum ya yi wa Ubangiji zunubi wa zai kāre shi?” Duk da haka,’ya’yansa ba su kula da gargaɗin mahaifinsu ba, domin nufin Ubangiji ne yă hallaka su.
“If one man sins against another, God will judge him; but if a man sins against Yahweh, who will speak for him?” But they would not listen to the voice of their father, because Yahweh intended to kill them.
26 Yaron nan Sama’ila ya dinga girma cikin kwarjini da cikin tagomashi a gaba Ubangiji da mutane.
The child Samuel grew up, and increased in favor with Yahweh and also with men.
27 Wani mutum ya zo wurin Eli ya ce masa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ashe ban bayana kaina sosai ga mahaifinka lokacin da yake a Masar a ƙarƙashin Fir’auna ba?
Now a man of God came to Eli and said to him, “Yahweh says, 'Did I not reveal myself to the house of your ancestor, when they were in Egypt in bondage to Pharaoh's house?
28 Na zaɓi mahaifinka daga cikin dukan kabilar Isra’ila yă zama firist nawa don yă yi hidima a bagade, don yă ƙona turare mai ƙanshi, don kuma yă sanya doguwar riga a gabana. Na kuma ba wa iyalin mahaifinka dukan hadaya ta ƙonawa da Isra’ila suka miƙa.
I chose him out of all the tribes of Israel to be my priest, to go up to my altar, and to burn incense, to wear an ephod before me. I gave to the house of your ancestor all the offerings of the people of Israel made with fire.
29 Don me kuke rena hadayata da sadakokina da na ƙayyade domin mazaunina? Don me kake girmama’ya’yanka fiye da ni ta wurin cinye sashe mafi kyau na kowane hadayar da mutanena Isra’ila suka miƙa?’
Why, then, do you scorn my sacrifices and offerings that I required in the place where I live? Why do you honor your sons above me by making yourselves fat with the best of every offering of my people Israel?'
30 “Saboda haka Ubangiji Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na yi alkawari cewa gidanka da gidan mahaifinka za su yi mini hidima a gabana har abada.’ Amma, yanzu Allah ya ce, ba zai yiwu ba; waɗanda suke girmama ni; Ni ma zan girmama su. Amma waɗanda suke ƙasƙantar da ni, haka za a ƙasƙantar da su.
For Yahweh, the God of Israel, says, 'I promised that your house, and the house of your ancestor, should walk before me forever.' But now Yahweh says, 'Far be it from me to do this, for I will honor those who honor me, but those who despise me will be lightly esteemed.
31 Lokaci yana zuwa sa’ad da zan rage ƙarfinka da ƙarfin iyalin gidan mahaifinka. Domin kada a sāke samun tsohon mutum a zuriyarka.
See, the days are coming when I will cut off your strength and the strength of your father's house, so that there will no longer be any old man in your house.
32 Za ka zama da ɓacin rai a mazaunina ko da yake za a yi wa Isra’ila alheri. A zuriyarka ba za a taɓa samun tsohon mutum ba.
You will see distress in the place where I live. Although good will be given to Israel, there will no longer be any old man in your house.
33 Kowannenku da ban kashe daga hidima a bagadena ba, za a bar shi don yă cika idanunka da hawaye da kuma baƙin ciki, dukan sauran zuriyarka kuwa za su mutu a ƙuruciyarsu.
Any one of you that I do not cut off from my altar, I will cause your eyes to fail, and I will cause grief for your life. All the men born in your family will die.
34 “‘Abin da kuma ya faru da’ya’yanka biyu Hofni da Finehas zai zama alama a gare ka; saboda mutuwarsu za tă zama a rana ɗaya.
This will be the sign for you that will come on your two sons, on Hophni and Phinehas: They will both die on the same day.
35 Zan tayar wa kaina amintaccen firist wanda zai aikata abin da nake so yă yi, zan kuwa ba shi zuriya da koyaushe za su yi aiki a gaban zaɓaɓɓen sarkina.
I will raise up for myself a faithful priest who will do what is in my heart and in my soul. I will build him a sure house; and he will walk before my anointed king forever.
36 Sa’an nan duk wanda ya rage a zuriyarka zai zo yă durƙusa a gabansa yă roƙi kuɗi da abinci, zai kuma roƙa a yardar masa yă taimaki firistoci da aiki domin yă sami abin da zai ci.’”
Everyone who is left in your house will come and bow down to him, asking for a piece of silver and a loaf of bread, and will say, “Please assign me to one of the priests' positions so I can eat a piece of bread.”'”