< 1 Sama’ila 2 >

1 Sai Hannatu ta yi addu’a ta ce, “Zuciyata tana farin ciki a cikin Ubangiji; a cikin Ubangiji an sa ina jin daɗi ƙwarai. Na buɗe bakina na yi wa abokan gābana dariya. Kai! Ina murna domin ka cece ni!
Then Hannah prayed, saying, “I rejoice in [what] you, [, have done]. I am strong [MET] because I belong to you. I (laugh at/ridicule) my enemies, because you, Yahweh have rescued me [from being taunted by them].
2 “Babu wani mai tsarki kamar Ubangiji babu wani, in ban da kai; babu wani dutse kamar Allahnmu.
There is no one who is holy like you, Yahweh. There is no other god like you. There is no one like you, our God, who can protect us [as though you were putting us beneath] a huge rock [where we can hide from danger].
3 “Ka daina maganganu na girman kai ka kuma daina faɗin kalmomin ɗaga kai; gama Ubangiji Allah ne masani daga gare shi kuma ana auna ayyuka.
[You people who oppose God], stop boasting! Yahweh is a God who knows [everything], and he will evaluate/judge everyone’s actions. So don’t speak so arrogantly!
4 “An kakkarya bakkuna masu yaƙi, amma su da ka raunana an ba su makaman ƙarfi.
Yahweh, you break the bows/weapons of mighty soldiers, and you give strength to those who stumble [because of being weak].
5 Waɗanda a dā suna da abinci sosai; yanzu suna ƙodago saboda abinci, masu fama da yunwa kuwa sun daina jin yunwa. Ita da take bakararriya, ta haifi’ya’ya bakwai amma ita da tana da’ya’ya da yawa, ta zama mai baƙin ciki.
Many people who previously had plenty to eat, now have to work for other people [to earn money] to buy food, but many who were always hungry are not hungry any more. The woman who did not have any children before, now has given birth to many/seven children, and the woman who had many children before, now is very lonely [because they have all died].
6 “Ubangiji ne ke kawo mutuwa, yă kuma rayar yana kai ga kabari, yă kuma tā da. (Sheol h7585)
Yahweh, you cause some people to die, and you restore some people who are almost dead. For some people, [it seems that they will soon] go to where the dead people are, but you cause them to become healthy again. (Sheol h7585)
7 Ubangiji ne yakan aika da talauci da kuma dukiya; yakan ƙasƙantar yă kuma ɗaukaka.
Yahweh, you cause some people to be poor and you cause some people to be rich, you humble some people and you honor some people.
8 Yakan tā da matalauci daga ƙura, yă kuma ɗaga mai bukata daga tarin toka; yă zaunar da su tare da’ya’yan sarki; yă kuma sa su gāji mulki na ɗaukaka. “Harsashin duniya na Ubangiji ne; a bisansu ne ya kafa duniya.
[Sometimes] you lift poor people up so that they are no longer [despondent, sitting in the dust, ] or sitting on heaps of ashes; you cause them to sit next to princes; you cause them to sit on chairs/thrones where people who are highly honored sit. Yahweh, you are the one who laid the foundations of the earth, and you have set the whole world on those foundations.
9 Zai kiyaye ƙafafun masu tsarki, amma mugaye za su lalace cikin duhu. “Ba bisa ga ƙarfi mutum ba ne mutum ke nasara;
You will protect your loyal/faithful people [SYN], but you will cause the wicked to die [EUP] and descend to the dark [place where dead people are]. We do not defeat [our enemies] by our own strength;
10 waɗanda suke gāba da Ubangiji za su hallaka. Zai yi musu tsawa daga sama, Ubangiji zai hukunta dukan duniya. “Zai ba wa sarkinsa ƙarfi, yă kuma ɗaukaka shafaffensa.”
Yahweh, you will break into pieces those who oppose you. You will cause thunder in the sky to show that you (oppose/are angry with) them. Yahweh, you will judge [people everywhere, even those who live in] the most remote places on the earth. You will give strength to the king whom you will appoint, and give him great power [over his enemies].”
11 Sa’an nan, Elkana ya koma gida a Rama amma yaron ya yi hidima a gaban Ubangiji a ƙarƙashin Eli firist.
Then Elkanah [and his family] returned to Ramah, but Samuel, the little boy, stayed to help Eli the priest serve Yahweh.
12 ’Ya’yan Eli firist, mutane ne masu mugunta. Ba su ɗauki Ubangiji a bakin kome ba.
Eli’s two [, who were also priests, ] were very wicked. They did not revere (OR, respect/obey) Yahweh.
13 Al’ada ce ga firistoci da mutane cewa in wani ya miƙa hadaya, yayinda nama yake kan wuta, bawan firist zai zo da babban cokali mai yatsu,
While the people were boiling the meat from their sacrifices [in the huge pot at the temple], one of Eli’s sons, [would send his servant to come with a large three-pronged fork in his hand].
14 zai soka cokali mai yatsun a tukunyar, ko butar da ake dafan naman. Duk abin da cokali mai yatsun ya cako daga tukunyar, ya zama na firist. Haka aka yi ta yi wa Isra’ilawan da suka zo miƙa hadaya a Shilo.
[He] would stick the fork into [the meat in] the pot, and whatever meat fastened onto the fork, he would take [and give it] to the priest who sent him. Eli’s sons did this to all the Israeli people who came to Shiloh [to offer sacrifices].
15 Tun ma kafin a ƙona kitse, bawan firist yakan zo yă ce wa mutumin da yake miƙa hadaya, “Ka ba wa firist nama domin yă gasa, ba zai karɓi dafaffen nama daga wurinka ba, sai ɗanye.”
Furthermore, before the fat [on the meat] was [cut off and] and burned [as a sacrifice to Yahweh], the servant of the priest would [sometimes] come to the man who was making the sacrifice and say to him, “Give me some meat [now to take] to the priest for him to roast! He wants raw meat; he does not want boiled meat.”
16 In kuwa mutumin ya ce masa, “Bari kitse yă ƙone tukuna, sa’an nan ka ɗiba duk abin da kake so.” Sai bawan yă ce masa, “A’a, ka ba ni yanzu, in ka ƙi kuwa zan ɗiba ƙarfi da yaji.”
If the man said to the servant, “Let the priests [cut off and] burn the fat first; then you can take what you want,” the servant would reply, “No, give it to me now; if you do not give it to me, I will take it forcefully!”
17 Wannan zunubin samarin ya yi muni ƙwarai a gaban Ubangiji, domin sun wulaƙanta hadayar Ubangiji, ƙwarai da gaske.
Yahweh considered that the young [sons of Eli] were committing a very great sin, because they were treating very disrespectfully the offerings that were being given to Yahweh.
18 Amma yaron nan Sama’ila, yana hidima a gaban Ubangiji yana sanye da efod na lilin.
As for Samuel, who was still a very young boy, he continued to do work for Yahweh, wearing a little sacred linen vest [like the Supreme Priest wore].
19 Kowace shekara mahaifiyarsa takan ɗinka’yar taguwa ta kai masa sa’ad da ita da mijinta suka je miƙa hadaya ta shekara.
Each year his mother made a [new] little robe for him and took it to him when she went up [to Shiloh] with her husband to offer a sacrifice.
20 Eli yakan sa wa Elkana da matarsa albarka, yă ce, Ubangiji yă ba ka waɗansu’ya’ya ta wurin matan nan, maimakon wanda ta roƙa daga Ubangiji, ta kuma ba da shi ga Ubangiji. Bayan haka sai su koma gida.
Then Eli would [ask God to] bless Elkanah and his wife, and he would say to Elkanah, “I hope/desire that Yahweh will enable your wife to give birth to other children, to take the place of the one whom she dedicated to Yahweh.” Then Elkanah and his family would return home.
21 Hannatu kuwa ta sami alfarma daga Ubangiji. Ta yi ciki. Ana cikin haka Sama’ila kuwa sai girma yake ta yi a gaban Ubangiji.
And Yahweh was very kind to Hannah, and enabled her to give birth to three [other] sons and two daughters. Their son Samuel grew up while he was doing work for Yahweh [in the Sacred Tent].
22 To, Eli kuwa ya tsufa ƙwarai, yana kuma jin labari duk abin da’ya’yansa suke yi wa dukan Isra’ila, da yadda suke lalata da matan da suke hidima a bakin ƙofar Tentin Sujada.
Eli became very old. He often heard about all the [evil] things that his sons were doing to the Israeli people. He heard that they [sometimes] (slept with/had sex with) the women who worked at the entrance to the tent where [God] spoke to [his people].
23 Saboda haka ya ce musu, “Don me kuke yin waɗannan abubuwa? Na sami labari daga wurin mutane a kan duk ayyukan muguntanku.
He said to them, “(It is terrible that you do such things!/Why do you do such things?) [RHQ] Many people keep telling me about the evil things that you do.
24 A’a,’ya’yana ba labari mai kyau nake ji cikin mutanen Ubangiji ba.
My sons, stop it! The reports [about you] that the people who belong to Yahweh tell others are terrible [EUP]!
25 In mutum ya yi wa wani laifi Allah yakan kāre shi; amma in mutum ya yi wa Ubangiji zunubi wa zai kāre shi?” Duk da haka,’ya’yansa ba su kula da gargaɗin mahaifinsu ba, domin nufin Ubangiji ne yă hallaka su.
If one person sins against another person, God can (intercede/act as a referee) between them. But if someone sins against Yahweh, no one can [RHQ] (intercede/act as a referee) between them!” But Eli’s sons would not listen to what their father said. This was because Yahweh had decided [that someone should] them.
26 Yaron nan Sama’ila ya dinga girma cikin kwarjini da cikin tagomashi a gaba Ubangiji da mutane.
The boy Samuel continued to grow up, and the things that he did pleased Yahweh and the people.
27 Wani mutum ya zo wurin Eli ya ce masa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ashe ban bayana kaina sosai ga mahaifinka lokacin da yake a Masar a ƙarƙashin Fir’auna ba?
One day, a prophet came to Eli and told him, “This is what Yahweh has told me: ‘When your ancestors were slaves of the king of Egypt, I appeared to Aaron.
28 Na zaɓi mahaifinka daga cikin dukan kabilar Isra’ila yă zama firist nawa don yă yi hidima a bagade, don yă ƙona turare mai ƙanshi, don kuma yă sanya doguwar riga a gabana. Na kuma ba wa iyalin mahaifinka dukan hadaya ta ƙonawa da Isra’ila suka miƙa.
From all the tribes of the Israeli people, I chose him [and his male descendants] to be priests for me. I appointed them to go up to my altar, to burn incense, to wear a sacred apron [as they worked] for me. And I declared that they could take [and eat some of the meat] that the Israeli people burned [on the altar].
29 Don me kuke rena hadayata da sadakokina da na ƙayyade domin mazaunina? Don me kake girmama’ya’yanka fiye da ni ta wurin cinye sashe mafi kyau na kowane hadayar da mutanena Isra’ila suka miƙa?’
So why do you show disrespect for the sacrifices and offerings that I commanded [the people to bring] to me [RHQ]? You are honoring your sons more than you are honoring me, by allowing them to get fat from eating the best parts of all the sacrifices that the Israeli people bring to me!’
30 “Saboda haka Ubangiji Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na yi alkawari cewa gidanka da gidan mahaifinka za su yi mini hidima a gabana har abada.’ Amma, yanzu Allah ya ce, ba zai yiwu ba; waɗanda suke girmama ni; Ni ma zan girmama su. Amma waɗanda suke ƙasƙantar da ni, haka za a ƙasƙantar da su.
“Therefore, this is what Yahweh, the God whom we Israelis [worship], declares: ‘I definitely promised that Aaron and his descendants would continue to serve [IDM] me forever.’ But now I declare this: ‘It will not continue like that! I will honor those who honor me, but I will despise those who despise me.
31 Lokaci yana zuwa sa’ad da zan rage ƙarfinka da ƙarfin iyalin gidan mahaifinka. Domin kada a sāke samun tsohon mutum a zuriyarka.
Listen carefully! There will soon be a time when I will cause all the strong [young men] in your family to die. The result will be that no men in your family will [live long enough to] become old men.
32 Za ka zama da ɓacin rai a mazaunina ko da yake za a yi wa Isra’ila alheri. A zuriyarka ba za a taɓa samun tsohon mutum ba.
You will be distressed and envious as you see the blessings that I will give to [the other people in] Israel. And [I repeat that] no men in your family will ever live long enough to become old men.
33 Kowannenku da ban kashe daga hidima a bagadena ba, za a bar shi don yă cika idanunka da hawaye da kuma baƙin ciki, dukan sauran zuriyarka kuwa za su mutu a ƙuruciyarsu.
There is one of your descendants whom I will spare, and not prevent him from serving me as a priest. But he will become blind, and then he will always be sad and grieving. But all your other descendants will die violently.
34 “‘Abin da kuma ya faru da’ya’yanka biyu Hofni da Finehas zai zama alama a gare ka; saboda mutuwarsu za tă zama a rana ɗaya.
And your two sons, Hophni and Phinehas, will both die on the same day. And that will prove to you [that all that I have said will come true/happen].
35 Zan tayar wa kaina amintaccen firist wanda zai aikata abin da nake so yă yi, zan kuwa ba shi zuriya da koyaushe za su yi aiki a gaban zaɓaɓɓen sarkina.
‘have chosen another man to be my priest. He is one who will serve me faithfully: He will do everything I want [DOU] him to do. And I will enable him to have many descendants [IDM] who will be priests and will always serve me by helping the king whom I will choose.
36 Sa’an nan duk wanda ya rage a zuriyarka zai zo yă durƙusa a gabansa yă roƙi kuɗi da abinci, zai kuma roƙa a yardar masa yă taimaki firistoci da aiki domin yă sami abin da zai ci.’”
All of your descendants who remain alive will have to go to that priest and ask him to give them money and food, and they will each have to say, “Please allow me to help the other priests, in order that I may [earn some money to] buy some food.”’”

< 1 Sama’ila 2 >