< 1 Sama’ila 19 >

1 Shawulu ya gaya wa ɗansa Yonatan da ma’aikatansa su kashe Dawuda. Amma Yonatan yana son Dawuda sosai.
I Saul govori Jonatanu sinu svojemu i svijem slugama svojim da ubiju Davida; ali Jonatan sin Saulov ljubljaše veoma Davida.
2 Sai ya gargaɗe shi ya ce, “Mahaifina Shawulu yana neman hanyar da zai kashe ka. Ka kula da kanka gobe da safe, ka tafi wani wuri ka ɓuya.
I javi Jonatan Davidu i reèe mu: Saul otac moj traži da te ubije; nego se èuvaj sjutra, skloni se gdjegod i prikrij se.
3 Zan je in tsaya da mahaifina a fili inda kake, zan yi masa magana game da kai. Zan kuma gaya maka abin da na ji.”
A ja æu izaæi i stajaæu pored oca svojega u polju gdje ti budeš, i govoriæu o tebi s ocem svojim, i što doznam javiæu ti.
4 Yonatan ya yi magana mai kyau a kan Dawuda a wajen mahaifinsa ya ce, “Kada sarki yă yi wani mummunan abu wa bawansa Dawuda, gama bai yi maka wani abu marar kyau ba. Abin da ya yi ya amfane ka ƙwarai da gaske.
I Jonatan progovori za Davida Saulu ocu svojemu, i reèe mu: da se ne ogriješi car o slugu svojega Davida, jer se on nije ogriješio o tebe, nego je još vrlo dobro za te što je èinio.
5 Ya yi kasai da ransa sa’ad da ya kashe Bafilistin nan. Ubangiji ya ba wa dukan Isra’ila babban nasara, ka gani, ka kuma yi farin ciki. Don me za ka ci mutuncin amintaccen mutum kamar Dawuda ta wurin kashe shi ba tare da wani dalili ba?”
Jer nije mario za život svoj i pobio je Filisteje, i Gospod uèini spasenje veliko svemu Izrailju; vidio si i radovao si se; pa zašto bi se ogriješio o krv pravu i ubio Davida ni za što?
6 Shawulu ya saurari Yonatan sai ya rantse ya ce, “Muddin Ubangiji yana a raye, ba za a kashe Dawuda ba.”
I posluša Saul Jonatana, i zakle se Saul: tako živ bio Gospod, neæe poginuti.
7 Ta haka Yonatan ya kira Dawuda ya gaya masa dukan maganarsu. Ya kawo shi wurin Shawulu, Dawuda kuwa ya zauna tare da Shawulu kamar dā.
Tada Jonatan dozva Davida, i kaza mu Jonatan sve ovo; i dovede Jonatan Davida k Saulu, i opet bi pred njim kao preðe.
8 Wani yaƙi ya sāke tashi, Dawuda kuwa ya fita ya yaƙi Filistiyawa, ya kai musu hari mai tsanani, sai da suka gudu a gabansa.
I nasta opet rat, i David izide i pobi se s Filistejima, i razbi ih veoma, te bježaše od njega.
9 Amma mugun ruhu daga Ubangiji ya sauko wa Shawulu yayinda yana zaune a cikin gidansa da māshi a hannunsa. Yayinda Dawuda yake bugan molo,
Potom zli duh Gospodnji napade Saula kad sjeðaše kod kuæe i držaše koplje u ruci, a David udaraše rukom o gusle.
10 Shawulu ya yi ƙoƙari yă kafe shi da bango da māshinsa, amma Dawuda ya goce sa’ad da Shawulu jefa māshin a bango. A daren nan Dawuda ya nemi hanya ya gudu.
I Saul šæaše Davida kopljem prikovati za zid, ali se on izmaèe Saulu, te koplje udari u zid, a David pobježe i izbavi se onu noæ.
11 Shawulu ya aiki mutane zuwa gidan Dawuda su yi gadin gidan, su kuma kashe Dawuda. Amma Mikal matar Dawuda ta gargaɗe Dawuda, ta ce, “In ba ka gudu a daren nan ba, kashegari za a kashe ka.”
A Saul posla ljude ka kuæi Davidovoj da ga èuvaju i ujutru ubiju. A to javi Davidu žena njegova Mihala govoreæi: ako noæas ne izbaviš duše svoje, ujutru æeš poginuti.
12 Haka kuwa Mikal ta sauko da Dawuda ta taga ya gudu, ya tsere.
Tada Mihala spusti Davida kroz prozor, te otide i pobježe i izbavi se.
13 Sai Mikal ta ɗauki gunki ta kwantar da shi a gādo, ta sa masa gashin akuya a kansa, sai ta rufe da mayafi.
A Mihala uze lik, i metnu ga u postelju, i metnu mu pod glavu uzglavlje od kostrijeti, i pokri ga haljinom.
14 Da Shawulu ya aiki mutane su kama Dawuda. Mikal ta ce, “Ba shi da lafiya.”
I kad Saul posla ljude da uhvate Davida, ona reèe: bolestan je.
15 Sai Shawulu ya sāke aiki mutanen su ga Dawuda, ya ce musu, “Ku kawo shi a gādonsa domin in kashe shi.”
A Saul posla opet ljude da vide Davida govoreæi: donesite mi ga u postelji da ga pogubim.
16 Amma da mutanen suka shiga sai suka ga gunkin a gadon, a wajen kan kuwa akwai gashin akuya.
A kad doðoše poslani, gle, lik u postelji i uzglavlje od kostrijeti pod glavom mu.
17 Shawulu ya ce wa Mikal, “Don me kika ruɗe ni har kika bar maƙiyina ya gudu ya tsere?” Mikal ta ce masa, “Ya ce mini, ‘Idan ban bar shi ya tafi ba, zai kashe ni?’”
I reèe Saul Mihali: što me tako prevari i pusti neprijatelja mojega da uteèe? A Mihala reèe Saulu: on mi reèe: pusti me, ili æu te ubiti.
18 Da Dawuda ya gudu ya tsere, sai ya tafi wurin Sama’ila a Rama ya gaya masa dukan abin da Shawulu ya yi masa. Da shi da Sama’ila suka tafi Nayiwot suka zauna a can.
Tako David uteèe i izbavi se, i doðe k Samuilu u Ramu, i pripovjedi mu sve što mu je uèinio Saul. I otidoše on i Samuilo, i ostaše u Najotu.
19 Shawulu ya sami labari cewa, “Dawuda yana Nayiwot a Rama.”
A Saulu doðe glas i rekoše mu: eno Davida u Najotu u Rami.
20 Sai ya aiki mutane su je su kamo Dawuda, amma da suka ga ƙungiyar annabawa suna annabci tare da Sama’ila shugabansu a tsaye, sai Ruhun Allah ya sauko wa mutanen Shawulu, su ma suka fara yin annabci.
Tada posla Saul ljude da uhvate Davida; i oni vidješe zbor proroka gdje prorokuju a Samuilo im starješina. I duh Gospodnji doðe na poslanike Saulove, te i oni prorokovahu.
21 Shawulu ya sami labari game da wannan, sai ya sāke aiken waɗansu da yawa. Su ma suka shiga yin annabci. Shawulu ya sāke aiken mutane sau na uku, su kuma suka shiga yin annabci.
A kad to javiše Saulu, on posla druge poslanike, ali i oni prorokovahu; te Saul opet posla treæe poslanike, ali i oni prorokovahu.
22 A ƙarshe, shi da kansa ya tashi ya tafi Rama. Ya bi ta babban rijiyar ruwan Seku. A can ya yi tambaya ya ce, “Ina Sama’ila da Dawuda suke?” Suka ce, “Suna cikin Nayiwot a Rama.”
Tada sam poðe u Ramu, i kad doðe na veliki studenac koji je u Sokotu, zapita govoreæi: gdje je Samuilo i David? I rekoše mu: eno ih u Najotu u Rami.
23 Saboda haka Shawulu ya tafi Nayiwot a Rama, amma Ruhun Allah ya sauko masa, shi ma ya yi tafiya yana annabci har sai da ya isa Nayiwot.
I poðe u Najot u Rami; ali i na njega siðe duh Božji, te iduæi dalje prorokovaše dokle doðe u Najot u Rami.
24 Ya tuttuɓe rigunarsa, ya kuma yi annabci a gaban Sama’ila. Ya kwanta tsirara dukan yini da dukan dare. Abin da ya sa ke nan mutane suke cewa, “Shawulu ma yana cikin annabawa ne?”
Pa skide i on haljine svoje sa sebe, i prorokova i on pred Samuilom, i padnuvši ležaše go vas onaj dan i svu noæ. Stoga se govori: eda li je i Saul meðu prorocima?

< 1 Sama’ila 19 >