< 1 Sama’ila 19 >
1 Shawulu ya gaya wa ɗansa Yonatan da ma’aikatansa su kashe Dawuda. Amma Yonatan yana son Dawuda sosai.
USawuli wasekhuluma kuJonathani indodana yakhe lakuzo zonke inceku zakhe ukuthi babulale uDavida. Kodwa uJonathani indodana kaSawuli wayemthanda kakhulukazi uDavida.
2 Sai ya gargaɗe shi ya ce, “Mahaifina Shawulu yana neman hanyar da zai kashe ka. Ka kula da kanka gobe da safe, ka tafi wani wuri ka ɓuya.
UJonathani wasemtshela uDavida esithi: USawuli ubaba udinga ukukubulala; ngakho-ke ake uzinanzelele ekuseni, uhlale ekusithekeni, ucatshe.
3 Zan je in tsaya da mahaifina a fili inda kake, zan yi masa magana game da kai. Zan kuma gaya maka abin da na ji.”
Mina-ke ngizaphuma ngime eceleni kukababa emmangweni lapho okhona, mina ngizakhuluma ngawe kubaba; lengikubonayo ngizakutshela.
4 Yonatan ya yi magana mai kyau a kan Dawuda a wajen mahaifinsa ya ce, “Kada sarki yă yi wani mummunan abu wa bawansa Dawuda, gama bai yi maka wani abu marar kyau ba. Abin da ya yi ya amfane ka ƙwarai da gaske.
UJonathani wasekhuluma okuhle ngoDavida kuSawuli uyise, wathi kuye: Inkosi kayingayoni inceku yayo, imelane loDavida, ngoba kakonanga wena, langokunjalo imisebenzi yakhe ilungile kakhulu kuwe.
5 Ya yi kasai da ransa sa’ad da ya kashe Bafilistin nan. Ubangiji ya ba wa dukan Isra’ila babban nasara, ka gani, ka kuma yi farin ciki. Don me za ka ci mutuncin amintaccen mutum kamar Dawuda ta wurin kashe shi ba tare da wani dalili ba?”
Ngoba wafaka impilo yakhe esandleni sakhe watshaya umFilisti; leNkosi yenzela uIsrayeli wonke usindiso olukhulu. Wakubona, wathokoza. Pho, uzalonelani igazi elingelacala ngokubulala uDavida kungelasizatho?
6 Shawulu ya saurari Yonatan sai ya rantse ya ce, “Muddin Ubangiji yana a raye, ba za a kashe Dawuda ba.”
USawuli waselilalela ilizwi likaJonathani, uSawuli wafunga wathi: Kuphila kukaJehova, kayikubulawa.
7 Ta haka Yonatan ya kira Dawuda ya gaya masa dukan maganarsu. Ya kawo shi wurin Shawulu, Dawuda kuwa ya zauna tare da Shawulu kamar dā.
UJonathani wasembiza uDavida, uJonathani wamtshela wonke lawomazwi. UJonathani wasemletha uDavida kuSawuli, njalo wayephambi kwakhe njengakuqala.
8 Wani yaƙi ya sāke tashi, Dawuda kuwa ya fita ya yaƙi Filistiyawa, ya kai musu hari mai tsanani, sai da suka gudu a gabansa.
Kwabuya kwaba khona impi; uDavida wasephuma walwa lamaFilisti, wawatshaya ngokutshaya okukhulu aze ambalekela.
9 Amma mugun ruhu daga Ubangiji ya sauko wa Shawulu yayinda yana zaune a cikin gidansa da māshi a hannunsa. Yayinda Dawuda yake bugan molo,
Njalo umoya omubi ovela eNkosini wawuphezu kukaSawuli ehlezi endlini yakhe, lomkhonto usesandleni sakhe; loDavida wayetshaya ichacho ngesandla sakhe.
10 Shawulu ya yi ƙoƙari yă kafe shi da bango da māshinsa, amma Dawuda ya goce sa’ad da Shawulu jefa māshin a bango. A daren nan Dawuda ya nemi hanya ya gudu.
USawuli wasedinga ukummbandakanya uDavida ngitsho emdulini ngomkhonto; kodwa waphunyuka ebukhoneni bukaSawuli, owahlaba umkhonto emdulini. UDavida wabaleka waphepha ngalobobusuku.
11 Shawulu ya aiki mutane zuwa gidan Dawuda su yi gadin gidan, su kuma kashe Dawuda. Amma Mikal matar Dawuda ta gargaɗe Dawuda, ta ce, “In ba ka gudu a daren nan ba, kashegari za a kashe ka.”
USawuli wasethuma izithunywa endlini kaDavida ukuze zimqaphele zimbulale ekuseni. UMikhali umkakhe wasemtshela uDavida esithi: Uba ungasindisi impilo yakho ngalobubusuku, kusasa uzabulawa.
12 Haka kuwa Mikal ta sauko da Dawuda ta taga ya gudu, ya tsere.
Ngakho uMikhali wasemehlisa uDavida ngewindi, wasehamba wabaleka waphepha.
13 Sai Mikal ta ɗauki gunki ta kwantar da shi a gādo, ta sa masa gashin akuya a kansa, sai ta rufe da mayafi.
UMikhali wasethatha isithombe, wasifaka embhedeni, wabeka umqamelo woboya bembuzi endaweni yekhanda laso, wasembesa ngelembu.
14 Da Shawulu ya aiki mutane su kama Dawuda. Mikal ta ce, “Ba shi da lafiya.”
Lapho uSawuli ethuma izithunywa ukuthatha uDavida, wathi: Uyagula.
15 Sai Shawulu ya sāke aiki mutanen su ga Dawuda, ya ce musu, “Ku kawo shi a gādonsa domin in kashe shi.”
USawuli wasethuma izithunywa ukumbona uDavida esithi: Menyuseleni kimi ngombheda ukuze ngimbulale.
16 Amma da mutanen suka shiga sai suka ga gunkin a gadon, a wajen kan kuwa akwai gashin akuya.
Lapho izithunywa zingena, khangela-ke, kwakulesithombe embhedeni, lomqamelo woboya bembuzi endaweni yekhanda laso.
17 Shawulu ya ce wa Mikal, “Don me kika ruɗe ni har kika bar maƙiyina ya gudu ya tsere?” Mikal ta ce masa, “Ya ce mini, ‘Idan ban bar shi ya tafi ba, zai kashe ni?’”
USawuli wasesithi kuMikhali: Ungikhohliseleni kanje, wayekela isitha sami sahamba saphepha? UMikhali wasesithi kuSawuli: Yena uthe kimi: Ngiyekela ngihambe; ngizakubulalelani?
18 Da Dawuda ya gudu ya tsere, sai ya tafi wurin Sama’ila a Rama ya gaya masa dukan abin da Shawulu ya yi masa. Da shi da Sama’ila suka tafi Nayiwot suka zauna a can.
Ngokunjalo uDavida wabaleka waphunyuka, wafika kuSamuweli eRama; wamtshela konke uSawuli ayekwenze kuye. Yena loSamuweli basebesiyahlala eNayothi.
19 Shawulu ya sami labari cewa, “Dawuda yana Nayiwot a Rama.”
USawuli wasebikelwa kwathiwa: Khangela, uDavida useNayothi eRama.
20 Sai ya aiki mutane su je su kamo Dawuda, amma da suka ga ƙungiyar annabawa suna annabci tare da Sama’ila shugabansu a tsaye, sai Ruhun Allah ya sauko wa mutanen Shawulu, su ma suka fara yin annabci.
USawuli wasethuma izithunywa ukumthatha uDavida; lapho zibona ixuku labaprofethi beprofetha, loSamuweli emi engumkhokheli phezu kwabo, uMoya kaNkulunkulu waba phezu kwezithunywa zikaSawuli, lazo zaseziprofetha.
21 Shawulu ya sami labari game da wannan, sai ya sāke aiken waɗansu da yawa. Su ma suka shiga yin annabci. Shawulu ya sāke aiken mutane sau na uku, su kuma suka shiga yin annabci.
Lapho ebikelwa uSawuli, wathuma ezinye izithunywa, zona lazo zaprofetha. USawuli wasephinda ethuma izithunywa ngokwesithathu, zona lazo zaprofetha.
22 A ƙarshe, shi da kansa ya tashi ya tafi Rama. Ya bi ta babban rijiyar ruwan Seku. A can ya yi tambaya ya ce, “Ina Sama’ila da Dawuda suke?” Suka ce, “Suna cikin Nayiwot a Rama.”
Laye wasesiya eRama, wafika emthonjeni omkhulu oseSeku, wabuza wathi: Bangaphi oSamuweli loDavida? Kwathiwa: Khangela, eNayothi eRama.
23 Saboda haka Shawulu ya tafi Nayiwot a Rama, amma Ruhun Allah ya sauko masa, shi ma ya yi tafiya yana annabci har sai da ya isa Nayiwot.
Wasesiya khona eNayothi eRama; loMoya kaNkulunkulu waba phezu kwakhe laye; wahamba ehamba eprofetha waze wafika eNayothi eRama.
24 Ya tuttuɓe rigunarsa, ya kuma yi annabci a gaban Sama’ila. Ya kwanta tsirara dukan yini da dukan dare. Abin da ya sa ke nan mutane suke cewa, “Shawulu ma yana cikin annabawa ne?”
Laye wasekhulula izigqoko zakhe, laye waprofetha phambi kukaSamuweli, walala phansi enqunu lonke lolosuku labo bonke lobobusuku. Yikho besithi: USawuli laye uphakathi kwabaprofethi yini?