< 1 Sama’ila 19 >
1 Shawulu ya gaya wa ɗansa Yonatan da ma’aikatansa su kashe Dawuda. Amma Yonatan yana son Dawuda sosai.
Tad Sauls runāja ar savu dēlu Jonatānu un ar visiem saviem kalpiem, ka tie Dāvidu nokautu. Bet Jonatānam, Saula dēlam, bija labs prāts uz Dāvidu.
2 Sai ya gargaɗe shi ya ce, “Mahaifina Shawulu yana neman hanyar da zai kashe ka. Ka kula da kanka gobe da safe, ka tafi wani wuri ka ɓuya.
Un Jonatāns Dāvidam to teica sacīdams: mans tēvs Sauls tevi meklē nokaut; nu tad, sargies jel rītu un paslēpies.
3 Zan je in tsaya da mahaifina a fili inda kake, zan yi masa magana game da kai. Zan kuma gaya maka abin da na ji.”
Bet es iziešu un stāvēšu savam tēvam sānis laukā, kur tu būsi, un runāšu ar savu tēvu tevis pēc un redzēšu, kas tur būs, un tev to sacīšu.
4 Yonatan ya yi magana mai kyau a kan Dawuda a wajen mahaifinsa ya ce, “Kada sarki yă yi wani mummunan abu wa bawansa Dawuda, gama bai yi maka wani abu marar kyau ba. Abin da ya yi ya amfane ka ƙwarai da gaske.
Tad Jonatāns runāja labu no Dāvida uz savu tēvu Saulu un uz to sacīja: lai ķēniņš neapgrēkojās pret savu kalpu Dāvidu, jo viņš pret tevi nav grēkojis, un viņa darbi tev nāk varen ļoti par labu.
5 Ya yi kasai da ransa sa’ad da ya kashe Bafilistin nan. Ubangiji ya ba wa dukan Isra’ila babban nasara, ka gani, ka kuma yi farin ciki. Don me za ka ci mutuncin amintaccen mutum kamar Dawuda ta wurin kashe shi ba tare da wani dalili ba?”
Jo viņš savu dzīvību ir licis savā rokā un to Fīlistu kāvis, un Tas Kungs ir devis lielu pestīšanu visam Israēlim. To tu esi redzējis un priecājies, kāpēc tad tu gribētu apgrēkoties pret nenoziedzīgām asinīm, Dāvidu bez vainas nokaudams.
6 Shawulu ya saurari Yonatan sai ya rantse ya ce, “Muddin Ubangiji yana a raye, ba za a kashe Dawuda ba.”
Un Sauls paklausīja Jonatāna balsij, un Sauls nozvērējās: tik tiešām ka Tas Kungs dzīvo, tam nebūs nokautam tapt.
7 Ta haka Yonatan ya kira Dawuda ya gaya masa dukan maganarsu. Ya kawo shi wurin Shawulu, Dawuda kuwa ya zauna tare da Shawulu kamar dā.
Un Jonatāns aicināja Dāvidu, un Jonatāns sacīja Dāvidam visus šos vārdus. Un Jonatāns veda Dāvidu Saula priekšā, un viņš bija šī priekšā kā citkārt.
8 Wani yaƙi ya sāke tashi, Dawuda kuwa ya fita ya yaƙi Filistiyawa, ya kai musu hari mai tsanani, sai da suka gudu a gabansa.
Tad atkal karš cēlās, un Dāvids izgāja un karoja ar Fīlistiem un tos kāva ar lielu kaušanu, un tie bēga viņa priekšā.
9 Amma mugun ruhu daga Ubangiji ya sauko wa Shawulu yayinda yana zaune a cikin gidansa da māshi a hannunsa. Yayinda Dawuda yake bugan molo,
Bet ļauns gars no Tā Kunga nāca pār Saulu, un tas sēdēja savā namā, un viņa šķēps bija viņa rokā, un Dāvids spēlēja uz stīgām ar roku.
10 Shawulu ya yi ƙoƙari yă kafe shi da bango da māshinsa, amma Dawuda ya goce sa’ad da Shawulu jefa māshin a bango. A daren nan Dawuda ya nemi hanya ya gudu.
Tad Sauls gribēja Dāvidu nodurt ar to šķēpu pie sienas, bet šis novērsās no Saula, un tas šķēps ieskrēja sienā; un Dāvids bēga un izbēga tai pašā naktī.
11 Shawulu ya aiki mutane zuwa gidan Dawuda su yi gadin gidan, su kuma kashe Dawuda. Amma Mikal matar Dawuda ta gargaɗe Dawuda, ta ce, “In ba ka gudu a daren nan ba, kashegari za a kashe ka.”
Tad Sauls sūtīja vīrus Dāvida namā viņu sargāt un rītu nokaut. Bet Mikale, viņa sieva, to viņam teica un sacīja: ja tu šo nakti savu dzīvību neglābsi, tad tu rītu tapsi nokauts.
12 Haka kuwa Mikal ta sauko da Dawuda ta taga ya gudu, ya tsere.
Un Mikale nolaida Dāvidu pa logu zemē, un tas nogāja un bēga un izglābās.
13 Sai Mikal ta ɗauki gunki ta kwantar da shi a gādo, ta sa masa gashin akuya a kansa, sai ta rufe da mayafi.
Un Mikale ņēma vienu tēlu un to lika uz gultu, un vienu kazu spalvas audumu tam lika galvgalā un to apsedza ar deķi.
14 Da Shawulu ya aiki mutane su kama Dawuda. Mikal ta ce, “Ba shi da lafiya.”
Un Sauls sūtīja vīrus, Dāvidu atvest, bet tā sacīja: viņš ir slims.
15 Sai Shawulu ya sāke aiki mutanen su ga Dawuda, ya ce musu, “Ku kawo shi a gādonsa domin in kashe shi.”
Tad Sauls sūtīja vīrus, Dāvidu aplūkot un sacīja: atnesiet to ar gultu pie manis, ka tas top nokauts.
16 Amma da mutanen suka shiga sai suka ga gunkin a gadon, a wajen kan kuwa akwai gashin akuya.
Kad nu tie vīri ienāca, redzi, tad tēls bija gultā, un kazu spalvas audums viņa galvgalā.
17 Shawulu ya ce wa Mikal, “Don me kika ruɗe ni har kika bar maƙiyina ya gudu ya tsere?” Mikal ta ce masa, “Ya ce mini, ‘Idan ban bar shi ya tafi ba, zai kashe ni?’”
Tad Sauls sacīja uz Mikali: kāpēc tu mani tā esi pievīlusi un manu ienaidnieku atlaidusi, ka tas ir aizbēdzis? Bet Mikale sacīja uz Saulu: viņš uz mani sacīja: atlaid mani, kāpēc man tevi būs nokaut?
18 Da Dawuda ya gudu ya tsere, sai ya tafi wurin Sama’ila a Rama ya gaya masa dukan abin da Shawulu ya yi masa. Da shi da Sama’ila suka tafi Nayiwot suka zauna a can.
Tā Dāvids bēga un izglābās un nāca pie Samuēla uz Rāmatu, un stāstīja tam visu, ko Sauls tam bija darījis, un gāja līdz ar Samuēli un palika Najotā.
19 Shawulu ya sami labari cewa, “Dawuda yana Nayiwot a Rama.”
Un Saulam teica un sacīja: redzi, Dāvids ir Najotā pie Rāmatas.
20 Sai ya aiki mutane su je su kamo Dawuda, amma da suka ga ƙungiyar annabawa suna annabci tare da Sama’ila shugabansu a tsaye, sai Ruhun Allah ya sauko wa mutanen Shawulu, su ma suka fara yin annabci.
Tad Sauls sūtīja vīrus, Dāvidu atvest. Kad tie nu redzēja vienu praviešu pulku runājam praviešu vārdus un Samuēli pie viņiem stāvam par uzraugu, tad Dieva Gars nāca par Saula vīriem, ka tie arī praviešu vārdus runāja.
21 Shawulu ya sami labari game da wannan, sai ya sāke aiken waɗansu da yawa. Su ma suka shiga yin annabci. Shawulu ya sāke aiken mutane sau na uku, su kuma suka shiga yin annabci.
Un kad tas Saulam tapa sacīts, tad viņš sūtīja citus vīrus, - un arī tie runāja praviešu vārdus. Tad Sauls sūtīja vēl trešos vīrus, - tie arīdzan runāja praviešu vārdus.
22 A ƙarshe, shi da kansa ya tashi ya tafi Rama. Ya bi ta babban rijiyar ruwan Seku. A can ya yi tambaya ya ce, “Ina Sama’ila da Dawuda suke?” Suka ce, “Suna cikin Nayiwot a Rama.”
Tad viņš arī pats gāja uz Rāmatu un nāca pie tās lielās akas, kas bija pie Sehus, un vaicāja sacīdams: kur ir Samuēls un Dāvids? Un viņam sacīja: redzi, Najotā pie Rāmatas.
23 Saboda haka Shawulu ya tafi Nayiwot a Rama, amma Ruhun Allah ya sauko masa, shi ma ya yi tafiya yana annabci har sai da ya isa Nayiwot.
Tad viņš gāja uz turieni, uz Najotu pie Rāmatas. Un Dieva Gars nāca arī uz viņu un tas gāja praviešu vārdus runādams, kamēr viņš nāca uz Najotu pie Rāmatas.
24 Ya tuttuɓe rigunarsa, ya kuma yi annabci a gaban Sama’ila. Ya kwanta tsirara dukan yini da dukan dare. Abin da ya sa ke nan mutane suke cewa, “Shawulu ma yana cikin annabawa ne?”
Un arī viņš tur novilka savas drēbes un runāja praviešu vārdus Samuēla priekšā, un viņš krita kails pie zemes cauru dienu un cauru nakti. Tāpēc saka: vai Sauls arī starp praviešiem?