< 1 Sama’ila 18 >

1 Bayan da Dawuda ya gama magana da Shawulu, sai Yonatan ɗan Shawulu ya ji zuciyarsa tana son Dawuda sosai. Yonatan kuwa yana ƙaunar Dawuda kamar ransa.
I kad svrši razgovor sa Saulom, duša Jonatanova prionu za dušu Davidovu, i Jonatan ga zapazi kao svoju dušu.
2 Tun daga wannan rana Shawulu ya zaunar da Dawuda tare da shi, bai bar shi ya koma gidan mahaifinsa ba.
I uze ga Saul taj dan, i ne dade mu da se vrati kuæi oca svojega.
3 Yonatan kuma ya yi yarjejjeniya da Dawuda saboda yana ƙaunarsa kamar ransa.
I Jonatan uèini vjeru s Davidom, jer ga ljubljaše kao svoju dušu.
4 Yonatan ya tuɓe doguwar taguwarsa da ya sa, ya ba wa Dawuda, tare da sulkensa, har ma da māshi da kibiyarsa, da kuma bel nasa.
I skide Jonatan sa sebe plašt, koji nošaše, i dade ga Davidu, i odijelo svoje i maè svoj i luk svoj i pojas svoj.
5 Duk abin da Shawulu ya aiki Dawuda yă yi yakan yi shi cikin aminci, har Shawulu ya ba shi babban makami a rundunarsa. Wannan ya faranta wa dukan mutane zuciya har ma da ma’aikatan Shawulu.
I iðaše David na što ga god Saul pošiljaše, i bijaše sreæan, i postavi ga Saul nad vojnicima, i omilje svemu narodu, pa i slugama Saulovijem.
6 Yayinda mutane suke dawowa gida bayan da Dawuda ya kashe Bafilistin, mata suka fito daga dukan biranen Isra’ila don su sadu da Sarki Shawulu, suna waƙoƙi da raye-raye masu farin ciki, da ganguna da sarewa.
A kad se vraæahu, i kad se David vraæaše ubivši Filistejina, izlaziše žene iz svakoga grada Izrailjeva pjevajuæi i igrajuæi na susret caru Saulu, s bubnjima i s veseljem i guslama.
7 Suna rawa suna cewa, “Shawulu ya kashe dubbansa, Dawuda kuwa ya kashe dubun dubbai.”
I otpijevajuæi žene jedne drugima uza svirke govorahu: Saul zgubi svoju tisuæu, ali David svojih deset tisuæa.
8 Shawulu kuwa ya ji fushi, wannan magana ba tă yi masa daɗi ba, ya yi tunani ya ce, “Suna yabon Dawuda cewa ya kashe dubun dubbai amma ni dubbai kawai. Me ya rage masa yanzu, in ba mulki ba?”
I razgnjevi se Saul vrlo, i ne biše mu po volji te rijeèi, i reèe: Davidu dadoše deset tisuæa, a meni dadoše tisuæu; još mu samo carstvo treba.
9 Tun daga wannan lokaci zuwa gaba, Shawulu ya dinga kishin Dawuda.
I od toga dana Saul gledaše poprijeko Davida.
10 Kashegari, mugun ruhu daga Allah ya fāɗo wa Shawulu da tsanani. Yana annabci a gidansa, Dawuda kuwa yana bugan molo kamar yadda ya saba. Shawulu yana riƙe da māshi a hannunsa.
A sjutradan napade Saula zli duh Božji, te prorokovaše u kuæi, a David mu udaraše rukom svojom u gusle kao prije: a Saulu u ruci bješe koplje.
11 Da ƙarfi yana magana da kansa yana cewa, “Zan kafe Dawuda da bango.” Amma Dawuda ya bauɗe masa sau biyu.
I Saul baci koplje govoreæi: da prikujem Davida za zid. Ali mu se David izmaèe dva puta.
12 Shawulu ya ji tsoron Dawuda don Ubangiji yana tare da shi, amma Ubangiji ya riga ya bar Shawulu.
I Saula bješe strah od Davida, jer Gospod bješe s njim, a od Saula bješe otstupio.
13 Saboda haka Shawulu bai yarda Dawuda yă zauna tare da shi ba, amma ya maishe shi shugaban sojoji dubu. Dawuda kuwa ya riƙa bi da su yana kaiwa yana kuma da tare da su.
Zato ga ukloni Saul od sebe, i postavi ga tisuænikom; i on odlažaše i dolažaše pred narodom.
14 A kome da Dawuda ya yi yakan yi nasara gama Ubangiji yana tare da shi.
I David bijaše sreæan u svemu što èinjaše, jer Gospod bijaše s njim.
15 Da Shawulu ya ga yadda yake cin nasara, sai ya ji tsoronsa.
A Saul videæi da je veoma sreæan, bojaše ga se.
16 Amma dukan Isra’ila da Yahuda suka ƙaunaci Dawuda gama yana bin da su a yaƙe-yaƙensu.
A sav Izrailj i Juda ljubljaše Davida, jer on odlažaše i dolažaše pred njima.
17 Shawulu ya ce wa Dawuda, “Ga diyata Merab zan ba ka ka aura, kai dai ka yi mini aiki da himma, ka kuma yi yaƙe-yaƙen Ubangiji.” Saboda Shawulu ya ce wa kansa, “Ba zan ɗaga hannuna a kansa ba, Filistiyawa ne za su yi wannan.”
I reèe Saul Davidu: evo, kæer svoju stariju Meravu daæu ti za ženu, samo mi budi hrabar i vodi ratove Gospodnje. Jer Saul govoraše: neæu da se digne moja ruka na nj, nego Filistejska ruka neka se digne na nj.
18 Amma Dawuda ya ce wa Shawulu, “Wane ni, wa ya san iyayena ko kabilar iyayena a Isra’ila da zan zama surukin sarki?”
A David reèe Saulu: ko sam ja i kakav je život moj ili dom oca mojega u Izrailju, da budem zet carev?
19 Da lokaci ya kai da Merab’yar Shawulu za tă yi aure da Dawuda, sai aka aurar da ita wa Adriyel na Mehola.
A kad doðe vrijeme da Meravu kæer Saulovu dadu Davidu, dadoše je Adrilu Meolaæaninu za ženu.
20 Mikal’yar Shawulu kuwa tana ƙaunar Dawuda sosai. Da aka gaya wa Shawulu labarin, sai ya yi farin ciki, ya yi tunani ya ce,
Ali Davida ljubljaše Mihala kæi Saulova; a kad to javiše Saulu, bi mu po volji.
21 “Zan ba shi ita tă zama masa tarko, da haka Filistiyawa za su same shi.” Shawulu ya ce wa Dawuda, “Yanzu kana da dama sau na biyu ka zama surukina.”
I reèe Saul: daæu mu je da mu bude zamka i da se diže na nj ruka Filistejska. A Davidu reèe Saul: biæeš mi danas zet s drugom.
22 Sai Shawulu ya umarci ma’aikatansa cewa, “Ku yi magana da Dawuda asirce ku ce, ‘Duba, sarki yana farin ciki da kai, dukan ma’aikatansa kuma suna sonka, ka yarda ka zama surukinsa.’”
I zapovjedi Saul slugama svojim: recite Davidu tajno i govorite: gle, omilio si caru, i sve sluge njegove ljube te; budi sada zet carev.
23 Suka sāke yi wa Dawuda wannan magana amma Dawuda ya ce, “Kuna tsammani abu mai sauƙi ne mutum yă zama surukin sarki? Ni talaka ne, kuma ba sananne ba.”
I sluge Saulove rekoše te rijeèi Davidu, a David reèe: mislite li da je lako biti zet carev? ta ja sam siromah i mali èovjek.
24 Da ma’aikatan Shawulu suka gaya masa abin da Dawuda ya faɗa.
I Saulu javiše ovo sluge njegove govoreæi: ovako reèe David.
25 Sai Shawulu ya ce, “Ku gaya wa Dawuda, ‘Sarki ba ya bukatan kuɗin auren’yarsa, sai dai loɓar Filistiyawa domin ramako a kan abokan gābansa.’” Shawulu yana shiri ne domin Dawuda yă fāɗa a hannun Filistiyawa.
A Saul reèe: ovako recite Davidu: ne traži car uzdarja, nego sto okrajaka Filistejskih, da se car osveti svojim neprijateljima. A Saul mišljaše kako bi David pao u ruke Filistejima.
26 Da ma’aikatan suka gaya wa Dawuda waɗannan abubuwa, sai ya yi murna don zai zama surukin sarki. Amma kafin lokacin yă cika,
I sluge njegove kazaše Davidu te rijeèi, i Davidu bi po volji da postane carev zet. I vrijeme se još ne navrši.
27 Dawuda da mutanensa suka fita suka kashe Filistiyawa ɗari biyu, suka kawo loɓar suka miƙa wa sarki, domin yă zama surukin sarki. Sai Shawulu ya ba da’yarsa Mikal aure ga Dawuda.
A David usta i otide sa svojim ljudima, i pobi dvjesta Filisteja. I donese David okrajke njihove, i dadoše ih na broj caru da bi postao carev zet. I Saul mu dade za ženu Mihalu kæer svoju.
28 Da Shawulu ya gane Ubangiji yana tare da Dawuda,’yarsa Mikal kuma tana ƙaunarsa,
I Saul vidje i pozna da je Gospod sa Davidom; i Mihala kæi Saulova ljubljaše ga.
29 sai Shawulu ya ƙara jin tsoron Dawuda har ya zama maƙiyinsa a dukan sauran rayuwarsa.
A Saul se još veæma poboja Davida; i bijaše Saul jednako neprijatelj Davidu.
30 Manyan sojojin Filistiyawa suka yi ta fita suna yaƙi da Isra’ilawa, amma kullum Dawuda yakan sami nasara fiye da sauran manyan sojojin Shawulu. Ta haka ya yi suna ƙwarai.
A knezovi Filistejski udarahu; i kad god udarahu, David bijaše sreæniji od svijeh sluga Saulovijeh, i ime se njegovo vrlo proslavi.

< 1 Sama’ila 18 >