< 1 Sama’ila 18 >

1 Bayan da Dawuda ya gama magana da Shawulu, sai Yonatan ɗan Shawulu ya ji zuciyarsa tana son Dawuda sosai. Yonatan kuwa yana ƙaunar Dawuda kamar ransa.
Et il arriva, lorsqu’il eut achevé de parler à Saül, que l’âme de Jonathas s’attacha étroitement à l’âme de David, et Jonathas l’aima comme son âme.
2 Tun daga wannan rana Shawulu ya zaunar da Dawuda tare da shi, bai bar shi ya koma gidan mahaifinsa ba.
Et Saül le prit en ce jour-là, et il ne lui accorda pas de retourner dans la maison de son père.
3 Yonatan kuma ya yi yarjejjeniya da Dawuda saboda yana ƙaunarsa kamar ransa.
Or David et Jonathas firent alliance; car Jonathas l’aimait comme son âme.
4 Yonatan ya tuɓe doguwar taguwarsa da ya sa, ya ba wa Dawuda, tare da sulkensa, har ma da māshi da kibiyarsa, da kuma bel nasa.
Aussi Jonathas se dépouilla de la tunique dont il était revêtu, et il la donna à David avec le reste de ses vêtements, jusqu’à son glaive et son arc, et jusqu’à son baudrier.
5 Duk abin da Shawulu ya aiki Dawuda yă yi yakan yi shi cikin aminci, har Shawulu ya ba shi babban makami a rundunarsa. Wannan ya faranta wa dukan mutane zuciya har ma da ma’aikatan Shawulu.
David allait aussi partout où l’envoyait Saul, et il se conduisait prudemment; de plus, il le préposa sur les hommes de guerre, et il était agréable aux yeux de tout le peuple, et surtout en la présence des serviteurs de Saul.
6 Yayinda mutane suke dawowa gida bayan da Dawuda ya kashe Bafilistin, mata suka fito daga dukan biranen Isra’ila don su sadu da Sarki Shawulu, suna waƙoƙi da raye-raye masu farin ciki, da ganguna da sarewa.
Or, lorsque David revint, après avoir tué le Philistin, les femmes sortirent de toutes les villes d’Israël, chantant et formant des danses, au-devant du roi Saül, avec des tambours de réjouissance, et avec des sistres.
7 Suna rawa suna cewa, “Shawulu ya kashe dubbansa, Dawuda kuwa ya kashe dubun dubbai.”
Et elles chantaient, jouant et disant: Saül en a tué mille, et David dix mille.
8 Shawulu kuwa ya ji fushi, wannan magana ba tă yi masa daɗi ba, ya yi tunani ya ce, “Suna yabon Dawuda cewa ya kashe dubun dubbai amma ni dubbai kawai. Me ya rage masa yanzu, in ba mulki ba?”
Mais Saül fut très irrité, et cette parole déplut à ses yeux, et il dit: Elles ont donné dix mille hommes à David, et à moi, elles m’en ont donné mille; que lui reste-t-il à avoir, si ce n’est la royauté?
9 Tun daga wannan lokaci zuwa gaba, Shawulu ya dinga kishin Dawuda.
Ainsi Saül, depuis ce jour-là, ne regarda jamais plus David d’un bon œil.
10 Kashegari, mugun ruhu daga Allah ya fāɗo wa Shawulu da tsanani. Yana annabci a gidansa, Dawuda kuwa yana bugan molo kamar yadda ya saba. Shawulu yana riƙe da māshi a hannunsa.
Mais après le jour suivant, l’esprit malin, envoyé de Dieu, saisit Saül, et il prophétisait au milieu de sa maison; mais David touchait la harpe de sa main comme tous les jours; et Saül tenait sa lance,
11 Da ƙarfi yana magana da kansa yana cewa, “Zan kafe Dawuda da bango.” Amma Dawuda ya bauɗe masa sau biyu.
Et il la jeta, pensant qu’il pourrait percer David avec la muraille; et David se détourna de devant lui par deux fois.
12 Shawulu ya ji tsoron Dawuda don Ubangiji yana tare da shi, amma Ubangiji ya riga ya bar Shawulu.
Alors Saül craignit David, parce que le Seigneur était avec David, tandis qu’il s’était retiré de lui.
13 Saboda haka Shawulu bai yarda Dawuda yă zauna tare da shi ba, amma ya maishe shi shugaban sojoji dubu. Dawuda kuwa ya riƙa bi da su yana kaiwa yana kuma da tare da su.
Saül l’éloigna donc de lui, et il le fit tribun sur mille hommes; et il sortait et il entrait en la présence du peuple.
14 A kome da Dawuda ya yi yakan yi nasara gama Ubangiji yana tare da shi.
En toutes ses voies aussi, David agissait prudemment, et le Seigneur était avec lui.
15 Da Shawulu ya ga yadda yake cin nasara, sai ya ji tsoronsa.
C’est pourquoi Saül vit qu’il était très prudent, et il commença à se garder de lui.
16 Amma dukan Isra’ila da Yahuda suka ƙaunaci Dawuda gama yana bin da su a yaƙe-yaƙensu.
Mais tout Israël et Juda aimait David; car c’était lui qui entrait et sortait devant eux.
17 Shawulu ya ce wa Dawuda, “Ga diyata Merab zan ba ka ka aura, kai dai ka yi mini aiki da himma, ka kuma yi yaƙe-yaƙen Ubangiji.” Saboda Shawulu ya ce wa kansa, “Ba zan ɗaga hannuna a kansa ba, Filistiyawa ne za su yi wannan.”
Et Saul dit à David: Voici ma fille aînée Mérob; c’est elle que je te donnerai pour femme; seulement sois courageux, et combats les combats du Seigneur. Or, Saül pensait en lui-même, disant: Que ma main ne soit pas contre lui, mais que la main des Philistins soit sur lui.
18 Amma Dawuda ya ce wa Shawulu, “Wane ni, wa ya san iyayena ko kabilar iyayena a Isra’ila da zan zama surukin sarki?”
Mais David répondit à Saül: Qui suis-je, moi, ou quelle est ma vie, ou quelle est la parenté de mon père en Israël, pour que je devienne gendre du roi?
19 Da lokaci ya kai da Merab’yar Shawulu za tă yi aure da Dawuda, sai aka aurar da ita wa Adriyel na Mehola.
Or, le temps vint que Mérob, fille de Saul, devait être donnée à David, et elle fut donnée pour femme à Hadriel, le Molathite.
20 Mikal’yar Shawulu kuwa tana ƙaunar Dawuda sosai. Da aka gaya wa Shawulu labarin, sai ya yi farin ciki, ya yi tunani ya ce,
Mais Michol, la seconde fille de Saül, aima David. Et on l’annonça à Saül, et cela lui plut.
21 “Zan ba shi ita tă zama masa tarko, da haka Filistiyawa za su same shi.” Shawulu ya ce wa Dawuda, “Yanzu kana da dama sau na biyu ka zama surukina.”
Et Saül dit: Je la lui donnerai, afin qu’elle devienne sa ruine, et que la main des Philistins soit sur lui. Saül dit donc à David: C’est à deux conditions que tu seras mon gendre aujourd’hui.
22 Sai Shawulu ya umarci ma’aikatansa cewa, “Ku yi magana da Dawuda asirce ku ce, ‘Duba, sarki yana farin ciki da kai, dukan ma’aikatansa kuma suna sonka, ka yarda ka zama surukinsa.’”
Alors Saül commanda à ses serviteurs: Parlez à David, sans que je paraisse, disant: Voilà que tu plais au roi, et tous ses serviteurs t’aiment. Maintenant donc sois le gendre du roi.
23 Suka sāke yi wa Dawuda wannan magana amma Dawuda ya ce, “Kuna tsammani abu mai sauƙi ne mutum yă zama surukin sarki? Ni talaka ne, kuma ba sananne ba.”
Et les serviteurs de Saül dirent aux oreilles de David toutes ces paroles. Et David répondit: Croyez-vous que ce soit peu, d’être le gendre du roi? Pour moi, je suis un homme pauvre et de nulle considération.
24 Da ma’aikatan Shawulu suka gaya masa abin da Dawuda ya faɗa.
Et les serviteurs de Saül le rapportèrent, disant: Telles sont les paroles qu’a dites David.
25 Sai Shawulu ya ce, “Ku gaya wa Dawuda, ‘Sarki ba ya bukatan kuɗin auren’yarsa, sai dai loɓar Filistiyawa domin ramako a kan abokan gābansa.’” Shawulu yana shiri ne domin Dawuda yă fāɗa a hannun Filistiyawa.
Mais Saül répondit: C’est ainsi que vous parlerez à David: Le roi n’a pas besoin de douaire, mais seulement de cent prépuces de Philistins, afin que vengeance soit faite des ennemis du roi. Mais Saül pensait livrer David aux mains des Philistins.
26 Da ma’aikatan suka gaya wa Dawuda waɗannan abubuwa, sai ya yi murna don zai zama surukin sarki. Amma kafin lokacin yă cika,
Et lorsque les serviteurs de Saül eurent rapporté à David les paroles que Saul avait dites, le discours plut à David, puisqu’il devenait gendre du roi.
27 Dawuda da mutanensa suka fita suka kashe Filistiyawa ɗari biyu, suka kawo loɓar suka miƙa wa sarki, domin yă zama surukin sarki. Sai Shawulu ya ba da’yarsa Mikal aure ga Dawuda.
Aussi, après peu de jours, David, se levant, s’en alla avec les hommes qui étaient sous lui; et il tua parmi les Philistins deux cents hommes, et il apporta leurs prépuces, et les compta au roi, afin qu’il fût son gendre. C’est pourquoi Saül lui donna Michol sa fille pour femme.
28 Da Shawulu ya gane Ubangiji yana tare da Dawuda,’yarsa Mikal kuma tana ƙaunarsa,
Et Saül vit et comprit que le Seigneur était avec David. Pour Michol, fille de Saül, elle aimait David.
29 sai Shawulu ya ƙara jin tsoron Dawuda har ya zama maƙiyinsa a dukan sauran rayuwarsa.
Et Saül commença à craindre davantage David; et Saül devint ennemi de David tous les jours.
30 Manyan sojojin Filistiyawa suka yi ta fita suna yaƙi da Isra’ilawa, amma kullum Dawuda yakan sami nasara fiye da sauran manyan sojojin Shawulu. Ta haka ya yi suna ƙwarai.
Et les princes des Philistins sortirent; mais dès le commencement de leur sortie, David se conduisait plus prudemment que tous les serviteurs de Saül, et son nom devint très célèbre.

< 1 Sama’ila 18 >