< 1 Sama’ila 18 >

1 Bayan da Dawuda ya gama magana da Shawulu, sai Yonatan ɗan Shawulu ya ji zuciyarsa tana son Dawuda sosai. Yonatan kuwa yana ƙaunar Dawuda kamar ransa.
Or il arriva qu'aussitôt que David eut achevé de parler à Saül, l'âme de Jonathan fut liée à l'âme de [David], tellement que Jonathan l'aima comme son âme.
2 Tun daga wannan rana Shawulu ya zaunar da Dawuda tare da shi, bai bar shi ya koma gidan mahaifinsa ba.
Ce jour-là donc Saül le prit, et ne lui permit plus de retourner en la maison de son père.
3 Yonatan kuma ya yi yarjejjeniya da Dawuda saboda yana ƙaunarsa kamar ransa.
Et Jonathan fit alliance avec David, parce qu'il l'aimait comme son âme.
4 Yonatan ya tuɓe doguwar taguwarsa da ya sa, ya ba wa Dawuda, tare da sulkensa, har ma da māshi da kibiyarsa, da kuma bel nasa.
Et Jonathan se dépouilla du manteau qu'il portait, et le donna à David, avec ses vêtements, même jusqu'à son épée, son arc, et son baudrier.
5 Duk abin da Shawulu ya aiki Dawuda yă yi yakan yi shi cikin aminci, har Shawulu ya ba shi babban makami a rundunarsa. Wannan ya faranta wa dukan mutane zuciya har ma da ma’aikatan Shawulu.
Et David était employé aux affaires; [et] partout où Saül l'envoyait, il réussissait; de sorte que Saül l'établit sur des gens de guerre, et il fut agréable à tout le peuple, et même aux serviteurs de Saül.
6 Yayinda mutane suke dawowa gida bayan da Dawuda ya kashe Bafilistin, mata suka fito daga dukan biranen Isra’ila don su sadu da Sarki Shawulu, suna waƙoƙi da raye-raye masu farin ciki, da ganguna da sarewa.
Or il arriva que comme ils revenaient, et que David retournait de la défaite du Philistin, il sortit des femmes de toutes les villes d'Israël, en chantant et dansant au devant du Roi Saül, avec des tambours, avec joie, et avec des cymbales.
7 Suna rawa suna cewa, “Shawulu ya kashe dubbansa, Dawuda kuwa ya kashe dubun dubbai.”
Et les femmes qui jouaient [des instruments] s'entre répondaient, et disaient: Saül a frappé ses mille, et David ses dix mille.
8 Shawulu kuwa ya ji fushi, wannan magana ba tă yi masa daɗi ba, ya yi tunani ya ce, “Suna yabon Dawuda cewa ya kashe dubun dubbai amma ni dubbai kawai. Me ya rage masa yanzu, in ba mulki ba?”
Et Saül fut fort irrité, et cette parole lui déplut, et il dit: Elles en ont donné dix mille à David, et à moi, mille; il ne lui manque donc plus que le Royaume.
9 Tun daga wannan lokaci zuwa gaba, Shawulu ya dinga kishin Dawuda.
Depuis ce jour-là Saül avait l'œil sur David.
10 Kashegari, mugun ruhu daga Allah ya fāɗo wa Shawulu da tsanani. Yana annabci a gidansa, Dawuda kuwa yana bugan molo kamar yadda ya saba. Shawulu yana riƙe da māshi a hannunsa.
Et il arriva, dès le lendemain que l'esprit malin [envoyé] de Dieu saisit Saül, et il faisait le Prophète au milieu de la maison, et David joua de sa main, comme les autres jours, et Saül avait une hallebarde en sa main.
11 Da ƙarfi yana magana da kansa yana cewa, “Zan kafe Dawuda da bango.” Amma Dawuda ya bauɗe masa sau biyu.
Et Saül lança la hallebarde, disant en soi-même: Je frapperai David, et la muraille; mais David se détourna de devant lui par deux fois.
12 Shawulu ya ji tsoron Dawuda don Ubangiji yana tare da shi, amma Ubangiji ya riga ya bar Shawulu.
Saül donc avait peur de la présence de David, parce que l'Eternel était avec David, et qu'il s'était rétiré d'avec Saül.
13 Saboda haka Shawulu bai yarda Dawuda yă zauna tare da shi ba, amma ya maishe shi shugaban sojoji dubu. Dawuda kuwa ya riƙa bi da su yana kaiwa yana kuma da tare da su.
C'est pourquoi Saül éloigna [David] de lui, et l'établit capitaine de mille [hommes]; et [David] allait et venait devant le peuple.
14 A kome da Dawuda ya yi yakan yi nasara gama Ubangiji yana tare da shi.
Et David réussissait en tout ce qu'il entreprenait, car l'Eternel était avec lui.
15 Da Shawulu ya ga yadda yake cin nasara, sai ya ji tsoronsa.
Saül donc voyant que David prospérait beaucoup, le craignit.
16 Amma dukan Isra’ila da Yahuda suka ƙaunaci Dawuda gama yana bin da su a yaƙe-yaƙensu.
Mais tout Israël et Juda aimaient David, parce qu'il allait et venait devant eux.
17 Shawulu ya ce wa Dawuda, “Ga diyata Merab zan ba ka ka aura, kai dai ka yi mini aiki da himma, ka kuma yi yaƙe-yaƙen Ubangiji.” Saboda Shawulu ya ce wa kansa, “Ba zan ɗaga hannuna a kansa ba, Filistiyawa ne za su yi wannan.”
Et Saül dit à David: Voici, je te donnerai Mérab ma fille aînée pour femme; sois-moi seulement un fils vertueux, et conduis les batailles de l'Eternel; car Saül disait: Que ma main ne soit point sur lui, mais que la main des Philistins soit sur lui.
18 Amma Dawuda ya ce wa Shawulu, “Wane ni, wa ya san iyayena ko kabilar iyayena a Isra’ila da zan zama surukin sarki?”
Et David répondit à Saül: Qui suis-je, et quelle est ma vie, [et] la famille de mon père en Israël, que je sois gendre du Roi?
19 Da lokaci ya kai da Merab’yar Shawulu za tă yi aure da Dawuda, sai aka aurar da ita wa Adriyel na Mehola.
Or il arriva qu'au temps qu'on devait donner Mérab fille de Saül à David, on la donna pour femme à Hadrièl Méholathite.
20 Mikal’yar Shawulu kuwa tana ƙaunar Dawuda sosai. Da aka gaya wa Shawulu labarin, sai ya yi farin ciki, ya yi tunani ya ce,
Mais Mical [l'autre] fille de Saül aima David; ce qu'on rapporta à Saül, et la chose lui plut.
21 “Zan ba shi ita tă zama masa tarko, da haka Filistiyawa za su same shi.” Shawulu ya ce wa Dawuda, “Yanzu kana da dama sau na biyu ka zama surukina.”
Et Saül dit: Je la lui donnerai afin qu'elle lui soit en piège, et que par ce moyen la main des Philistins soit sur lui. Saül donc dit à David: Tu seras aujourd'hui mon gendre par [l'une de] mes deux [filles].
22 Sai Shawulu ya umarci ma’aikatansa cewa, “Ku yi magana da Dawuda asirce ku ce, ‘Duba, sarki yana farin ciki da kai, dukan ma’aikatansa kuma suna sonka, ka yarda ka zama surukinsa.’”
Et Saül commanda à ses serviteurs de parler à David en secret, et de lui dire: Voici, le Roi prend plaisir en toi, et tous ses serviteurs t'aiment; sois donc maintenant gendre du Roi.
23 Suka sāke yi wa Dawuda wannan magana amma Dawuda ya ce, “Kuna tsammani abu mai sauƙi ne mutum yă zama surukin sarki? Ni talaka ne, kuma ba sananne ba.”
Les serviteurs donc de Saül redirent toutes ces paroles à David, et David dit: Pensez-vous que ce soit peu de chose d'être gendre du Roi, vu que je suis un pauvre homme, et de nulle estime?
24 Da ma’aikatan Shawulu suka gaya masa abin da Dawuda ya faɗa.
Et les serviteurs de Saül lui rapportèrent cela, [et lui] dirent: David a tenu de tels discours.
25 Sai Shawulu ya ce, “Ku gaya wa Dawuda, ‘Sarki ba ya bukatan kuɗin auren’yarsa, sai dai loɓar Filistiyawa domin ramako a kan abokan gābansa.’” Shawulu yana shiri ne domin Dawuda yă fāɗa a hannun Filistiyawa.
Et Saül dit: Vous parlerez ainsi à David: Le Roi ne demande d'autre douaire, que cent prépuces de Philistins, afin que le Roi soit vengé de ses ennemis. Or Saül avait dessein de faire tomber David entre les mains des Philistins.
26 Da ma’aikatan suka gaya wa Dawuda waɗannan abubuwa, sai ya yi murna don zai zama surukin sarki. Amma kafin lokacin yă cika,
Et les serviteurs de Saül rapportèrent tous ces discours à David; et la chose lui plut, pour être gendre du Roi. Et avant que les jours fussent accomplis,
27 Dawuda da mutanensa suka fita suka kashe Filistiyawa ɗari biyu, suka kawo loɓar suka miƙa wa sarki, domin yă zama surukin sarki. Sai Shawulu ya ba da’yarsa Mikal aure ga Dawuda.
David se leva, et s'en alla, lui et ses gens, et frappa deux cents hommes des Philistins; et David apporta leurs prépuces, et on les livra bien comptés au Roi, afin qu'il fût gendre du Roi. Et Saül lui donna pour femme Mical sa fille.
28 Da Shawulu ya gane Ubangiji yana tare da Dawuda,’yarsa Mikal kuma tana ƙaunarsa,
Alors Saül aperçut et connut que l'Eternel était avec David; et Mical fille de Saül l'aimait.
29 sai Shawulu ya ƙara jin tsoron Dawuda har ya zama maƙiyinsa a dukan sauran rayuwarsa.
Et Saül continua de craindre David, encore plus [qu'auparavant], tellement que Saül fut toujours ennemi de David.
30 Manyan sojojin Filistiyawa suka yi ta fita suna yaƙi da Isra’ilawa, amma kullum Dawuda yakan sami nasara fiye da sauran manyan sojojin Shawulu. Ta haka ya yi suna ƙwarai.
Or les capitaines des Philistins sortirent [en campagne], et dès qu'ils furent sortis, David réussit mieux que tous les serviteurs de Saül; et son nom fut en fort grande estime.

< 1 Sama’ila 18 >