< 1 Sama’ila 18 >

1 Bayan da Dawuda ya gama magana da Shawulu, sai Yonatan ɗan Shawulu ya ji zuciyarsa tana son Dawuda sosai. Yonatan kuwa yana ƙaunar Dawuda kamar ransa.
Lorsqu'il eut fini de parler à Saül, l'âme de Jonathan s'unit à l'âme de David, et Jonathan l'aima comme sa propre âme.
2 Tun daga wannan rana Shawulu ya zaunar da Dawuda tare da shi, bai bar shi ya koma gidan mahaifinsa ba.
Saül le prit ce jour-là et ne voulut plus le laisser rentrer dans la maison de son père.
3 Yonatan kuma ya yi yarjejjeniya da Dawuda saboda yana ƙaunarsa kamar ransa.
Alors Jonathan et David firent alliance, car il l'aimait comme son âme.
4 Yonatan ya tuɓe doguwar taguwarsa da ya sa, ya ba wa Dawuda, tare da sulkensa, har ma da māshi da kibiyarsa, da kuma bel nasa.
Jonathan se dépouilla de la robe qu'il portait et la donna à David avec ses vêtements, y compris son épée, son arc et sa ceinture.
5 Duk abin da Shawulu ya aiki Dawuda yă yi yakan yi shi cikin aminci, har Shawulu ya ba shi babban makami a rundunarsa. Wannan ya faranta wa dukan mutane zuciya har ma da ma’aikatan Shawulu.
David allait partout où Saül l'envoyait et se conduisait avec sagesse, et Saül l'établit à la tête des hommes de guerre. C'était bon aux yeux de tout le peuple, et aussi aux yeux des serviteurs de Saül.
6 Yayinda mutane suke dawowa gida bayan da Dawuda ya kashe Bafilistin, mata suka fito daga dukan biranen Isra’ila don su sadu da Sarki Shawulu, suna waƙoƙi da raye-raye masu farin ciki, da ganguna da sarewa.
Au retour de David, après avoir abattu le Philistin, les femmes sortirent de toutes les villes d'Israël, chantant et dansant, pour aller au-devant du roi Saül, avec des tambourins, de la joie et des instruments de musique.
7 Suna rawa suna cewa, “Shawulu ya kashe dubbansa, Dawuda kuwa ya kashe dubun dubbai.”
Les femmes chantaient entre elles en jouant, et disaient, « Saül a tué ses milliers d'hommes, et David ses dix mille. »
8 Shawulu kuwa ya ji fushi, wannan magana ba tă yi masa daɗi ba, ya yi tunani ya ce, “Suna yabon Dawuda cewa ya kashe dubun dubbai amma ni dubbai kawai. Me ya rage masa yanzu, in ba mulki ba?”
Saül était très en colère, et cette parole lui déplaisait. Il dit: « Ils ont crédité David de dix mille hommes, et ils ne m'ont crédité que de mille. Que peut-il avoir de plus que le royaume? »
9 Tun daga wannan lokaci zuwa gaba, Shawulu ya dinga kishin Dawuda.
Saül surveilla David à partir de ce jour-là.
10 Kashegari, mugun ruhu daga Allah ya fāɗo wa Shawulu da tsanani. Yana annabci a gidansa, Dawuda kuwa yana bugan molo kamar yadda ya saba. Shawulu yana riƙe da māshi a hannunsa.
Le lendemain, un mauvais esprit de Dieu s'abattit puissamment sur Saül, qui prophétisa au milieu de la maison. David jouait avec sa main, comme il le faisait chaque jour. Saül avait sa lance à la main;
11 Da ƙarfi yana magana da kansa yana cewa, “Zan kafe Dawuda da bango.” Amma Dawuda ya bauɗe masa sau biyu.
et Saül lança la lance, car il disait: « Je vais clouer David au mur! » David s'échappa deux fois de sa présence.
12 Shawulu ya ji tsoron Dawuda don Ubangiji yana tare da shi, amma Ubangiji ya riga ya bar Shawulu.
Saül eut peur de David, car Yahvé était avec lui et s'était éloigné de Saül.
13 Saboda haka Shawulu bai yarda Dawuda yă zauna tare da shi ba, amma ya maishe shi shugaban sojoji dubu. Dawuda kuwa ya riƙa bi da su yana kaiwa yana kuma da tare da su.
C'est pourquoi Saül l'éloigna de sa présence, et l'établit chef de mille hommes; il sortit et entra devant le peuple.
14 A kome da Dawuda ya yi yakan yi nasara gama Ubangiji yana tare da shi.
David se conduisit avec sagesse dans toutes ses voies, et l'Éternel était avec lui.
15 Da Shawulu ya ga yadda yake cin nasara, sai ya ji tsoronsa.
Lorsque Saül vit qu'il se conduisait avec beaucoup de sagesse, il le craignit.
16 Amma dukan Isra’ila da Yahuda suka ƙaunaci Dawuda gama yana bin da su a yaƙe-yaƙensu.
Mais tout Israël et tout Juda aimaient David, car il sortait et entrait devant eux.
17 Shawulu ya ce wa Dawuda, “Ga diyata Merab zan ba ka ka aura, kai dai ka yi mini aiki da himma, ka kuma yi yaƙe-yaƙen Ubangiji.” Saboda Shawulu ya ce wa kansa, “Ba zan ɗaga hannuna a kansa ba, Filistiyawa ne za su yi wannan.”
Saül dit à David: « Voici ma fille aînée Merab. Je te la donne pour femme. Seulement, sois vaillant pour moi, et combats les batailles de Yahvé. » Car Saül dit: « Que ma main ne soit pas sur lui, mais que la main des Philistins soit sur lui. »
18 Amma Dawuda ya ce wa Shawulu, “Wane ni, wa ya san iyayena ko kabilar iyayena a Isra’ila da zan zama surukin sarki?”
David dit à Saül: « Qui suis-je, et quelle est ma vie, ou la famille de mon père en Israël, pour que je sois gendre du roi? »
19 Da lokaci ya kai da Merab’yar Shawulu za tă yi aure da Dawuda, sai aka aurar da ita wa Adriyel na Mehola.
Mais au moment où Merab, la fille de Saül, aurait dû être donnée à David, elle fut donnée pour femme à Adriel, le Méholathite.
20 Mikal’yar Shawulu kuwa tana ƙaunar Dawuda sosai. Da aka gaya wa Shawulu labarin, sai ya yi farin ciki, ya yi tunani ya ce,
Mical, fille de Saül, aimait David. On le dit à Saül, et la chose lui plut.
21 “Zan ba shi ita tă zama masa tarko, da haka Filistiyawa za su same shi.” Shawulu ya ce wa Dawuda, “Yanzu kana da dama sau na biyu ka zama surukina.”
Saül dit: Je la lui donnerai, afin qu'elle soit un piège pour lui et que la main des Philistins soit contre lui. Saül dit donc une seconde fois à David: « Tu seras aujourd'hui mon gendre. »
22 Sai Shawulu ya umarci ma’aikatansa cewa, “Ku yi magana da Dawuda asirce ku ce, ‘Duba, sarki yana farin ciki da kai, dukan ma’aikatansa kuma suna sonka, ka yarda ka zama surukinsa.’”
Saül donna cet ordre à ses serviteurs: « Parle secrètement à David, et dis-lui: « Voici que le roi prend plaisir à te voir, et que tous ses serviteurs t'aiment. Maintenant, sois le gendre du roi. »
23 Suka sāke yi wa Dawuda wannan magana amma Dawuda ya ce, “Kuna tsammani abu mai sauƙi ne mutum yă zama surukin sarki? Ni talaka ne, kuma ba sananne ba.”
Les serviteurs de Saül prononcèrent ces paroles aux oreilles de David. David répondit: « Cela vous paraît-il léger d'être le gendre du roi, puisque je suis un homme pauvre et peu connu? »
24 Da ma’aikatan Shawulu suka gaya masa abin da Dawuda ya faɗa.
Les serviteurs de Saül lui dirent: « David a parlé ainsi. »
25 Sai Shawulu ya ce, “Ku gaya wa Dawuda, ‘Sarki ba ya bukatan kuɗin auren’yarsa, sai dai loɓar Filistiyawa domin ramako a kan abokan gābansa.’” Shawulu yana shiri ne domin Dawuda yă fāɗa a hannun Filistiyawa.
Saül dit: « Dis à David: « Le roi ne désire pas d'autre dot que cent prépuces de Philistins, pour se venger des ennemis du roi ». Saül pensait maintenant faire tomber David par la main des Philistins.
26 Da ma’aikatan suka gaya wa Dawuda waɗannan abubuwa, sai ya yi murna don zai zama surukin sarki. Amma kafin lokacin yă cika,
Lorsque ses serviteurs rapportèrent ces paroles à David, celui-ci se réjouit d'être le gendre du roi. Avant l'échéance,
27 Dawuda da mutanensa suka fita suka kashe Filistiyawa ɗari biyu, suka kawo loɓar suka miƙa wa sarki, domin yă zama surukin sarki. Sai Shawulu ya ba da’yarsa Mikal aure ga Dawuda.
David se leva et partit, lui et ses hommes, et il tua deux cents hommes des Philistins. David apporta leurs prépuces, et on les donna en nombre au roi, afin qu'il soit le gendre du roi. Et Saül lui donna pour femme sa fille Mical.
28 Da Shawulu ya gane Ubangiji yana tare da Dawuda,’yarsa Mikal kuma tana ƙaunarsa,
Saül voyait et savait que l'Éternel était avec David, et Mical, la fille de Saül, l'aimait.
29 sai Shawulu ya ƙara jin tsoron Dawuda har ya zama maƙiyinsa a dukan sauran rayuwarsa.
Saül eut encore plus peur de David, et Saül fut sans cesse l'ennemi de David.
30 Manyan sojojin Filistiyawa suka yi ta fita suna yaƙi da Isra’ilawa, amma kullum Dawuda yakan sami nasara fiye da sauran manyan sojojin Shawulu. Ta haka ya yi suna ƙwarai.
Et les princes des Philistins sortirent; et chaque fois qu'ils sortirent, David se conduisit plus sagement que tous les serviteurs de Saül, de sorte que son nom fut hautement estimé.

< 1 Sama’ila 18 >