< 1 Sama’ila 18 >

1 Bayan da Dawuda ya gama magana da Shawulu, sai Yonatan ɗan Shawulu ya ji zuciyarsa tana son Dawuda sosai. Yonatan kuwa yana ƙaunar Dawuda kamar ransa.
After David finished talking with Saul, [he met Saul’s son, Jonathan.] Jonathan [immediately] liked David; in fact, he began to love/like him as much as he loved/liked himself.
2 Tun daga wannan rana Shawulu ya zaunar da Dawuda tare da shi, bai bar shi ya koma gidan mahaifinsa ba.
From that day, Saul kept David with him, and did not let him return home.
3 Yonatan kuma ya yi yarjejjeniya da Dawuda saboda yana ƙaunarsa kamar ransa.
Because Jonathan loved David so much, he made a solemn agreement with David. [They promised each other that they would always be loyal friends].
4 Yonatan ya tuɓe doguwar taguwarsa da ya sa, ya ba wa Dawuda, tare da sulkensa, har ma da māshi da kibiyarsa, da kuma bel nasa.
Jonathan took off his own outer robe and gave it to David. He also gave David his soldier’s tunic, his sword, his bow [and arrows], and his belt.
5 Duk abin da Shawulu ya aiki Dawuda yă yi yakan yi shi cikin aminci, har Shawulu ya ba shi babban makami a rundunarsa. Wannan ya faranta wa dukan mutane zuciya har ma da ma’aikatan Shawulu.
[David went wherever Saul sent him. And] whatever Saul told him to do, David did it very successfully. As a result, Saul appointed David to be a commander in the army. All the officers and other men in the army (approved of/were very pleased with) that.
6 Yayinda mutane suke dawowa gida bayan da Dawuda ya kashe Bafilistin, mata suka fito daga dukan biranen Isra’ila don su sadu da Sarki Shawulu, suna waƙoƙi da raye-raye masu farin ciki, da ganguna da sarewa.
But, when the men in the army were returning home after David had killed Goliath, the women came out from many [HYP] towns in Israel to meet/greet King Saul. They were singing and dancing very joyfully, playing tambourines and lyres.
7 Suna rawa suna cewa, “Shawulu ya kashe dubbansa, Dawuda kuwa ya kashe dubun dubbai.”
As they danced, they sang this song to each other: “Saul has killed 1,000 [enemy soldiers], But David has killed 10,000 [of them].”
8 Shawulu kuwa ya ji fushi, wannan magana ba tă yi masa daɗi ba, ya yi tunani ya ce, “Suna yabon Dawuda cewa ya kashe dubun dubbai amma ni dubbai kawai. Me ya rage masa yanzu, in ba mulki ba?”
[When] Saul [heard them singing that, he] did not like it. He became very angry. He said [to himself], “They are saying that David [killed] 10,000 men, but that I [have killed] only 1,000. Soon they will want to make him their king!” [RHQ]
9 Tun daga wannan lokaci zuwa gaba, Shawulu ya dinga kishin Dawuda.
From that time, Saul watched David very closely because he was suspicious [that David would try to become king].
10 Kashegari, mugun ruhu daga Allah ya fāɗo wa Shawulu da tsanani. Yana annabci a gidansa, Dawuda kuwa yana bugan molo kamar yadda ya saba. Shawulu yana riƙe da māshi a hannunsa.
The next day, an evil spirit sent by God suddenly took control of Saul. He began to act like a madman, inside his house. David was playing the lyre for him, as he did every day. Saul was holding a spear in his hand,
11 Da ƙarfi yana magana da kansa yana cewa, “Zan kafe Dawuda da bango.” Amma Dawuda ya bauɗe masa sau biyu.
and he hurled it [at David], saying to himself, “I will fasten David to the wall with the spear!” He did that two times, but David jumped aside [both times].
12 Shawulu ya ji tsoron Dawuda don Ubangiji yana tare da shi, amma Ubangiji ya riga ya bar Shawulu.
Because [it became evident that] Yahweh had abandoned Saul but [that] he was helping David, Saul was afraid of David.
13 Saboda haka Shawulu bai yarda Dawuda yă zauna tare da shi ba, amma ya maishe shi shugaban sojoji dubu. Dawuda kuwa ya riƙa bi da su yana kaiwa yana kuma da tare da su.
So he appointed David as a commander of 1,000 soldiers and sent David away from him, [hoping that David would be killed in a battle]. But when David led his soldiers [in their battles],
14 A kome da Dawuda ya yi yakan yi nasara gama Ubangiji yana tare da shi.
he always had great success, because Yahweh was helping him.
15 Da Shawulu ya ga yadda yake cin nasara, sai ya ji tsoronsa.
When Saul heard that David [and his soldiers were] very successful, he became more afraid of David.
16 Amma dukan Isra’ila da Yahuda suka ƙaunaci Dawuda gama yana bin da su a yaƙe-yaƙensu.
But all the people of Israel and of Judah loved David, because he led the soldiers very successfully [in the battles].
17 Shawulu ya ce wa Dawuda, “Ga diyata Merab zan ba ka ka aura, kai dai ka yi mini aiki da himma, ka kuma yi yaƙe-yaƙen Ubangiji.” Saboda Shawulu ya ce wa kansa, “Ba zan ɗaga hannuna a kansa ba, Filistiyawa ne za su yi wannan.”
One day Saul said to David, “I am ready to give you my oldest daughter, Merab, to be your wife. I will do that if you serve me bravely by fighting battles for Yahweh [against the Philistines]”. He said that because he thought, “I will not try to get rid of David by myself. I will allow the Philistines to do that.”
18 Amma Dawuda ya ce wa Shawulu, “Wane ni, wa ya san iyayena ko kabilar iyayena a Isra’ila da zan zama surukin sarki?”
But David said to Saul, “I am not [RHQ] a very important person, and my family is not very important, and my clan is not a very important Israeli clan. So I do not deserve to become your son-in-law.” [RHQ]
19 Da lokaci ya kai da Merab’yar Shawulu za tă yi aure da Dawuda, sai aka aurar da ita wa Adriyel na Mehola.
So, when it was time for Merab to be given to David to become his wife, instead, Saul gave her to a man named Adriel, from Meholah [town].
20 Mikal’yar Shawulu kuwa tana ƙaunar Dawuda sosai. Da aka gaya wa Shawulu labarin, sai ya yi farin ciki, ya yi tunani ya ce,
But Saul’s other daughter, Michal, fell in love with David. When they told Saul about that, he was pleased.
21 “Zan ba shi ita tă zama masa tarko, da haka Filistiyawa za su same shi.” Shawulu ya ce wa Dawuda, “Yanzu kana da dama sau na biyu ka zama surukina.”
He thought, “I will let Michal marry him, in order that she may trap him, and the Philistines will be able to kill him.” So he said to David, [“You can marry Michal],” and by saying that, he indicated for the second time that David would become his son-in-law.
22 Sai Shawulu ya umarci ma’aikatansa cewa, “Ku yi magana da Dawuda asirce ku ce, ‘Duba, sarki yana farin ciki da kai, dukan ma’aikatansa kuma suna sonka, ka yarda ka zama surukinsa.’”
Saul told his servants, “Talk to David privately, and say to him, ‘Listen, the king is pleased with you, and all of us his servants love you. So now [we think that] you should [marry Michal and] become the king’s son-in-law.’”
23 Suka sāke yi wa Dawuda wannan magana amma Dawuda ya ce, “Kuna tsammani abu mai sauƙi ne mutum yă zama surukin sarki? Ni talaka ne, kuma ba sananne ba.”
So they told that to David. But David said, “It would be a great honor [RHQ] to become the king’s son-in-law. But [I do not think that I should do that, because] I am only a poor and insignificant man.”
24 Da ma’aikatan Shawulu suka gaya masa abin da Dawuda ya faɗa.
When the servants told Saul what David had said,
25 Sai Shawulu ya ce, “Ku gaya wa Dawuda, ‘Sarki ba ya bukatan kuɗin auren’yarsa, sai dai loɓar Filistiyawa domin ramako a kan abokan gābansa.’” Shawulu yana shiri ne domin Dawuda yă fāɗa a hannun Filistiyawa.
Saul replied, “Go and say to David, ‘[In order for] the king [to allow you to marry Michal, he] wants [you to kill] 100 Philistines [and cut off] their foreskins [and bring the foreskins to him to prove that you have killed them]. In that way he will get revenge on his enemies.’” But what Saul wanted was that the Philistines would kill David [while David was trying to kill them].
26 Da ma’aikatan suka gaya wa Dawuda waɗannan abubuwa, sai ya yi murna don zai zama surukin sarki. Amma kafin lokacin yă cika,
When the servants told that to David, he was very pleased that he could become the king’s son-in-law [by doing that. The king had said how many days he would allow for David to do that]. But before that time ended,
27 Dawuda da mutanensa suka fita suka kashe Filistiyawa ɗari biyu, suka kawo loɓar suka miƙa wa sarki, domin yă zama surukin sarki. Sai Shawulu ya ba da’yarsa Mikal aure ga Dawuda.
David and his men went and killed, [not 100, but] 200 Philistines! He brought their foreskins to Saul, and counted them [while Saul was watching], in order to prove that he had [done what the king required so that he could become Saul’s son-in-law. So then Saul was obligated] to allow David to marry his daughter Michal.
28 Da Shawulu ya gane Ubangiji yana tare da Dawuda,’yarsa Mikal kuma tana ƙaunarsa,
But when Saul realized that Yahweh was helping David, and that his daughter loved David,
29 sai Shawulu ya ƙara jin tsoron Dawuda har ya zama maƙiyinsa a dukan sauran rayuwarsa.
he became more afraid of David. So, as long as Saul lived, he was David’s enemy.
30 Manyan sojojin Filistiyawa suka yi ta fita suna yaƙi da Isra’ilawa, amma kullum Dawuda yakan sami nasara fiye da sauran manyan sojojin Shawulu. Ta haka ya yi suna ƙwarai.
The Philistine armies repeatedly came to fight the Israelis, but every time they fought, David and his soldiers were more successful than any of Saul’s other army commanders. As a result, David became very famous.

< 1 Sama’ila 18 >