< 1 Sama’ila 18 >

1 Bayan da Dawuda ya gama magana da Shawulu, sai Yonatan ɗan Shawulu ya ji zuciyarsa tana son Dawuda sosai. Yonatan kuwa yana ƙaunar Dawuda kamar ransa.
And it comes to pass, when he finishes to speak to Saul, that the soul of Jonathan has been bound to the soul of David, and Jonathan loves him as his own soul.
2 Tun daga wannan rana Shawulu ya zaunar da Dawuda tare da shi, bai bar shi ya koma gidan mahaifinsa ba.
And Saul takes him on that day, and has not permitted him to return to the house of his father.
3 Yonatan kuma ya yi yarjejjeniya da Dawuda saboda yana ƙaunarsa kamar ransa.
And Jonathan makes—David also—a covenant, because he loves him as his own soul,
4 Yonatan ya tuɓe doguwar taguwarsa da ya sa, ya ba wa Dawuda, tare da sulkensa, har ma da māshi da kibiyarsa, da kuma bel nasa.
and Jonathan strips himself of the upper robe which [is] on him, and gives it to David, and his long robe, even to his sword, and to his bow, and to his girdle.
5 Duk abin da Shawulu ya aiki Dawuda yă yi yakan yi shi cikin aminci, har Shawulu ya ba shi babban makami a rundunarsa. Wannan ya faranta wa dukan mutane zuciya har ma da ma’aikatan Shawulu.
And David goes out wherever Saul sends him; he acted wisely, and Saul sets him over the men of war, and it is good in the eyes of all the people, and also in the eyes of the servants of Saul.
6 Yayinda mutane suke dawowa gida bayan da Dawuda ya kashe Bafilistin, mata suka fito daga dukan biranen Isra’ila don su sadu da Sarki Shawulu, suna waƙoƙi da raye-raye masu farin ciki, da ganguna da sarewa.
And it comes to pass, in their coming in, in David’s returning from striking the Philistine, that the women come out from all the cities of Israel to sing—also the dancers—to meet Saul the king, with tambourines, with joy, and with three-stringed instruments;
7 Suna rawa suna cewa, “Shawulu ya kashe dubbansa, Dawuda kuwa ya kashe dubun dubbai.”
and the women answer—those playing, and say, “Saul has struck among his thousands, And David among his myriads.”
8 Shawulu kuwa ya ji fushi, wannan magana ba tă yi masa daɗi ba, ya yi tunani ya ce, “Suna yabon Dawuda cewa ya kashe dubun dubbai amma ni dubbai kawai. Me ya rage masa yanzu, in ba mulki ba?”
And it is exceedingly displeasing to Saul, and this thing is evil in his eyes, and he says, “They have given myriads to David, and they have given the thousands to me, and what more [is there] for him but the kingdom?”
9 Tun daga wannan lokaci zuwa gaba, Shawulu ya dinga kishin Dawuda.
And Saul is eyeing David from that day and from then on.
10 Kashegari, mugun ruhu daga Allah ya fāɗo wa Shawulu da tsanani. Yana annabci a gidansa, Dawuda kuwa yana bugan molo kamar yadda ya saba. Shawulu yana riƙe da māshi a hannunsa.
And it comes to pass, on the next day, that the spirit of sadness [from] God prospers over Saul, and he prophesies in the midst of the house, and David is playing with his hand, as [he did] day by day, and the javelin [is] in the hand of Saul,
11 Da ƙarfi yana magana da kansa yana cewa, “Zan kafe Dawuda da bango.” Amma Dawuda ya bauɗe masa sau biyu.
and Saul casts the javelin and says, “I strike through David, even through the wall”; and David turns around out of his presence twice.
12 Shawulu ya ji tsoron Dawuda don Ubangiji yana tare da shi, amma Ubangiji ya riga ya bar Shawulu.
And Saul is afraid of the presence of David, for YHWH has been with him, and He has turned aside from Saul;
13 Saboda haka Shawulu bai yarda Dawuda yă zauna tare da shi ba, amma ya maishe shi shugaban sojoji dubu. Dawuda kuwa ya riƙa bi da su yana kaiwa yana kuma da tare da su.
and Saul turns him aside from him, and appoints him to himself [for] head of one thousand, and he goes out and comes in, before the people.
14 A kome da Dawuda ya yi yakan yi nasara gama Ubangiji yana tare da shi.
And David is acting wisely in all his ways, and YHWH [is] with him,
15 Da Shawulu ya ga yadda yake cin nasara, sai ya ji tsoronsa.
and Saul sees that he is acting very wisely, and is afraid of him,
16 Amma dukan Isra’ila da Yahuda suka ƙaunaci Dawuda gama yana bin da su a yaƙe-yaƙensu.
and all Israel and Judah love David when he is going out and coming in before them.
17 Shawulu ya ce wa Dawuda, “Ga diyata Merab zan ba ka ka aura, kai dai ka yi mini aiki da himma, ka kuma yi yaƙe-yaƙen Ubangiji.” Saboda Shawulu ya ce wa kansa, “Ba zan ɗaga hannuna a kansa ba, Filistiyawa ne za su yi wannan.”
And Saul says to David, “Behold, my elder daughter Merab—I give her to you for a wife; only, be for a son of valor to me, and fight the battles of YHWH”; and Saul said, “Do not let my hand be on him, but let the hand of the Philistines be on him.”
18 Amma Dawuda ya ce wa Shawulu, “Wane ni, wa ya san iyayena ko kabilar iyayena a Isra’ila da zan zama surukin sarki?”
And David says to Saul, “Who [am] I? And what [is] my life—the family of my father in Israel—that I am son-in-law of the king?”
19 Da lokaci ya kai da Merab’yar Shawulu za tă yi aure da Dawuda, sai aka aurar da ita wa Adriyel na Mehola.
And it comes to pass, at the time of the giving of Merab daughter of Saul to David, that she has been given to Adriel the Meholathite for a wife.
20 Mikal’yar Shawulu kuwa tana ƙaunar Dawuda sosai. Da aka gaya wa Shawulu labarin, sai ya yi farin ciki, ya yi tunani ya ce,
And Michal daughter of Saul loves David, and they declare [it] to Saul, and the thing is right in his eyes,
21 “Zan ba shi ita tă zama masa tarko, da haka Filistiyawa za su same shi.” Shawulu ya ce wa Dawuda, “Yanzu kana da dama sau na biyu ka zama surukina.”
and Saul says, “I give her to him, and she is for a snare to him, and the hand of the Philistines is on him”; and Saul says to David, “By the second—you become my son-in-law today.”
22 Sai Shawulu ya umarci ma’aikatansa cewa, “Ku yi magana da Dawuda asirce ku ce, ‘Duba, sarki yana farin ciki da kai, dukan ma’aikatansa kuma suna sonka, ka yarda ka zama surukinsa.’”
And Saul commands his servants, “Speak to David gently, saying, Behold, the king has delighted in you, and all his servants have loved you, and now, be son-in-law of the king.”
23 Suka sāke yi wa Dawuda wannan magana amma Dawuda ya ce, “Kuna tsammani abu mai sauƙi ne mutum yă zama surukin sarki? Ni talaka ne, kuma ba sananne ba.”
And the servants of Saul speak these words in the ears of David, and David says, “Is it a light thing in your eyes to be son-in-law of the king—and I a poor man, and lightly esteemed?”
24 Da ma’aikatan Shawulu suka gaya masa abin da Dawuda ya faɗa.
And the servants of Saul declare [it] to him, saying, “David has spoken according to these words.”
25 Sai Shawulu ya ce, “Ku gaya wa Dawuda, ‘Sarki ba ya bukatan kuɗin auren’yarsa, sai dai loɓar Filistiyawa domin ramako a kan abokan gābansa.’” Shawulu yana shiri ne domin Dawuda yă fāɗa a hannun Filistiyawa.
And Saul says, “Thus you say to David, There is no delight for the king in dowry, but in one hundred foreskins of the Philistines—to be avenged on the enemies of the king”; and Saul thought to cause David to fall by the hand of the Philistines.
26 Da ma’aikatan suka gaya wa Dawuda waɗannan abubuwa, sai ya yi murna don zai zama surukin sarki. Amma kafin lokacin yă cika,
And his servants declare these words to David, and the thing is right in the eyes of David, to be son-in-law of the king; and the days have not been full,
27 Dawuda da mutanensa suka fita suka kashe Filistiyawa ɗari biyu, suka kawo loɓar suka miƙa wa sarki, domin yă zama surukin sarki. Sai Shawulu ya ba da’yarsa Mikal aure ga Dawuda.
and David rises and goes, he and his men, and strikes two hundred men among the Philistines, and David brings in their foreskins, and they set them before the king, to be son-in-law of the king; and Saul gives his daughter Michal to him for a wife.
28 Da Shawulu ya gane Ubangiji yana tare da Dawuda,’yarsa Mikal kuma tana ƙaunarsa,
And Saul sees and knows that YHWH [is] with David, and Michal daughter of Saul has loved him,
29 sai Shawulu ya ƙara jin tsoron Dawuda har ya zama maƙiyinsa a dukan sauran rayuwarsa.
and Saul adds to be afraid of the presence of David still; and Saul is an enemy of David [for] all the days.
30 Manyan sojojin Filistiyawa suka yi ta fita suna yaƙi da Isra’ilawa, amma kullum Dawuda yakan sami nasara fiye da sauran manyan sojojin Shawulu. Ta haka ya yi suna ƙwarai.
And the princes of the Philistines come out, and it comes to pass from the time of their coming out, David has acted more wisely than any of the servants of Saul, and his name is very precious.

< 1 Sama’ila 18 >