< 1 Sama’ila 18 >

1 Bayan da Dawuda ya gama magana da Shawulu, sai Yonatan ɗan Shawulu ya ji zuciyarsa tana son Dawuda sosai. Yonatan kuwa yana ƙaunar Dawuda kamar ransa.
Kad je David završio razgovor sa Šaulom, Jonatanova se duša prikloni Davidovoj duši i Jonatan ga zavolje kao samoga sebe.
2 Tun daga wannan rana Shawulu ya zaunar da Dawuda tare da shi, bai bar shi ya koma gidan mahaifinsa ba.
Šaul zadrža Davida onoga istog dana kod sebe i nije mu dao da se vrati kući svoga oca.
3 Yonatan kuma ya yi yarjejjeniya da Dawuda saboda yana ƙaunarsa kamar ransa.
I Jonatan sklopi savez s Davidom jer ga je ljubio kao samoga sebe.
4 Yonatan ya tuɓe doguwar taguwarsa da ya sa, ya ba wa Dawuda, tare da sulkensa, har ma da māshi da kibiyarsa, da kuma bel nasa.
I skide Jonatan plašt koji je imao na sebi i dade ga Davidu; tako i svoju odoru, čak i svoj mač, svoj luk i svoj pojas.
5 Duk abin da Shawulu ya aiki Dawuda yă yi yakan yi shi cikin aminci, har Shawulu ya ba shi babban makami a rundunarsa. Wannan ya faranta wa dukan mutane zuciya har ma da ma’aikatan Shawulu.
Na svim svojim pohodima, kamo ga je god slao Šaul, David bijaše sretne ruke i Šaul ga postavi na čelo svojim ratnicima; omilje on svemu narodu, pa i Šaulovim dvoranima.
6 Yayinda mutane suke dawowa gida bayan da Dawuda ya kashe Bafilistin, mata suka fito daga dukan biranen Isra’ila don su sadu da Sarki Shawulu, suna waƙoƙi da raye-raye masu farin ciki, da ganguna da sarewa.
Za njihova povratka, kad se David vraćao ubivši Filistejca, izađoše žene iz svih gradova Izraelovih u susret kralju Šaulu veselo kličući, pjevajući i plešući uza zvuke bubnjeva i cimbala.
7 Suna rawa suna cewa, “Shawulu ya kashe dubbansa, Dawuda kuwa ya kashe dubun dubbai.”
Žene su plešući pjevale: “Pobi Šaul svoje tisuće, David na desetke tisuća.”
8 Shawulu kuwa ya ji fushi, wannan magana ba tă yi masa daɗi ba, ya yi tunani ya ce, “Suna yabon Dawuda cewa ya kashe dubun dubbai amma ni dubbai kawai. Me ya rage masa yanzu, in ba mulki ba?”
Šaul se vrlo ražestio, nije mu bila draga ta pjesma. Zato reče: “Davidu su dale desetke tisuća, a meni samo tisuće! Još mu samo treba kraljevstvo!”
9 Tun daga wannan lokaci zuwa gaba, Shawulu ya dinga kishin Dawuda.
I od toga dana Šaul poprijeko gledaše Davida.
10 Kashegari, mugun ruhu daga Allah ya fāɗo wa Shawulu da tsanani. Yana annabci a gidansa, Dawuda kuwa yana bugan molo kamar yadda ya saba. Shawulu yana riƙe da māshi a hannunsa.
Sutradan zao duh Božji napade Šaula, tako da je bjesnio po kući. David je rukom udarao u harfu kao drugih dana, a Šaul je u ruci imao koplje.
11 Da ƙarfi yana magana da kansa yana cewa, “Zan kafe Dawuda da bango.” Amma Dawuda ya bauɗe masa sau biyu.
I Šaul baci koplje govoreći u sebi: “Sad ću pribiti Davida uza zid!” Ali mu se David izmače dva puta.
12 Shawulu ya ji tsoron Dawuda don Ubangiji yana tare da shi, amma Ubangiji ya riga ya bar Shawulu.
Šaul se poče bojati Davida, jer je Jahve bio s njim a od Šaula je odstupio.
13 Saboda haka Shawulu bai yarda Dawuda yă zauna tare da shi ba, amma ya maishe shi shugaban sojoji dubu. Dawuda kuwa ya riƙa bi da su yana kaiwa yana kuma da tare da su.
Zato ga Šaul ukloni iz svoje blizine i postavi ga za tisućnika: on je izlazio i vraćao se na čelu naroda.
14 A kome da Dawuda ya yi yakan yi nasara gama Ubangiji yana tare da shi.
David je imao uspjeha na svim svojim putovima jer Jahve bijaše s njim.
15 Da Shawulu ya ga yadda yake cin nasara, sai ya ji tsoronsa.
Kad je Šaul vidio da David ima mnogo uspjeha, obuze ga strah od njega.
16 Amma dukan Isra’ila da Yahuda suka ƙaunaci Dawuda gama yana bin da su a yaƙe-yaƙensu.
Ali svemu Izraelu i Judi omilje David jer ih je on vodio na svim njihovim putovima.
17 Shawulu ya ce wa Dawuda, “Ga diyata Merab zan ba ka ka aura, kai dai ka yi mini aiki da himma, ka kuma yi yaƙe-yaƙen Ubangiji.” Saboda Shawulu ya ce wa kansa, “Ba zan ɗaga hannuna a kansa ba, Filistiyawa ne za su yi wannan.”
Šaul reče Davidu: “Evo svoju najstariju kćer Merabu dat ću ti za ženu, samo mi budi hrabar i vodi Jahvine bojeve!” Mišljaše Šaul: “Neću da padne od moje ruke, nego filistejska ruka neka se digne na njega!”
18 Amma Dawuda ya ce wa Shawulu, “Wane ni, wa ya san iyayena ko kabilar iyayena a Isra’ila da zan zama surukin sarki?”
A David odgovori: “Tko sam ja i što znači moj život, što li kuća oca mojega u Izraelu da budem kraljev zet?”
19 Da lokaci ya kai da Merab’yar Shawulu za tă yi aure da Dawuda, sai aka aurar da ita wa Adriyel na Mehola.
I kad dođe vrijeme da Šaulova kći Meraba pođe za Davida, dadoše je za ženu Adrielu iz Mehole.
20 Mikal’yar Shawulu kuwa tana ƙaunar Dawuda sosai. Da aka gaya wa Shawulu labarin, sai ya yi farin ciki, ya yi tunani ya ce,
Ali je Davida ljubila Šaulova kći Mikala; kad su to javili Šaulu, bilo mu je pravo.
21 “Zan ba shi ita tă zama masa tarko, da haka Filistiyawa za su same shi.” Shawulu ya ce wa Dawuda, “Yanzu kana da dama sau na biyu ka zama surukina.”
Reče on u sebi: “Dat ću mu je, ali će mu ona biti zamka i ruka filistejska dići će se na njega.” (Šaul je po drugi put rekao Davidu: “Danas ćeš mi biti zet.”)
22 Sai Shawulu ya umarci ma’aikatansa cewa, “Ku yi magana da Dawuda asirce ku ce, ‘Duba, sarki yana farin ciki da kai, dukan ma’aikatansa kuma suna sonka, ka yarda ka zama surukinsa.’”
Tada Šaul zapovjedi svojim slugama ovako: “Razgovarajte se s Davidom tajno i recite mu: 'Gle, omilio si kralju i svi te njegovi dvorani vole; zato budi kraljev zet.'”
23 Suka sāke yi wa Dawuda wannan magana amma Dawuda ya ce, “Kuna tsammani abu mai sauƙi ne mutum yă zama surukin sarki? Ni talaka ne, kuma ba sananne ba.”
I Šaulove sluge ponoviše te riječi Davidu, ali im David odgovori: “Zar je u vašim očima malenkost postati kraljev zet? Ja sam samo siromah i mali čovjek!”
24 Da ma’aikatan Shawulu suka gaya masa abin da Dawuda ya faɗa.
Šaulove sluge dojaviše to Šaulu govoreći: “Evo riječi što ih je rekao David.”
25 Sai Shawulu ya ce, “Ku gaya wa Dawuda, ‘Sarki ba ya bukatan kuɗin auren’yarsa, sai dai loɓar Filistiyawa domin ramako a kan abokan gābansa.’” Shawulu yana shiri ne domin Dawuda yă fāɗa a hannun Filistiyawa.
A Šaul odgovori: “Ovako recite Davidu: 'Kralj ne traži nikakva ženidbenog dara nego samo sto filistejskih obrezaka da se osveti kraljevim neprijateljima.'” Šaul mišljaše da će tako Davida gurnuti u ruke Filistejcima.
26 Da ma’aikatan suka gaya wa Dawuda waɗannan abubuwa, sai ya yi murna don zai zama surukin sarki. Amma kafin lokacin yă cika,
Šaulove sluge dojaviše te riječi Davidu, a njemu bijaše po volji da postane kraljev zet. Još prije nego što je isteklo vrijeme,
27 Dawuda da mutanensa suka fita suka kashe Filistiyawa ɗari biyu, suka kawo loɓar suka miƙa wa sarki, domin yă zama surukin sarki. Sai Shawulu ya ba da’yarsa Mikal aure ga Dawuda.
spremi se David i krenu sa svojim ljudima te ubi Filistejcima dvije stotine ljudi; i donese njihove obreske i predade ih kralju na broj da bi postao njegov zet. Tada mu Šaul dade svoju kćer Mikalu za ženu.
28 Da Shawulu ya gane Ubangiji yana tare da Dawuda,’yarsa Mikal kuma tana ƙaunarsa,
Šaul je jasno vidio da je Jahve s Davidom i da ga ljubi sav dom Izraelov.
29 sai Shawulu ya ƙara jin tsoron Dawuda har ya zama maƙiyinsa a dukan sauran rayuwarsa.
I Šaul se još većma poboja Davida i posta neprijatelj Davidu zauvijek.
30 Manyan sojojin Filistiyawa suka yi ta fita suna yaƙi da Isra’ilawa, amma kullum Dawuda yakan sami nasara fiye da sauran manyan sojojin Shawulu. Ta haka ya yi suna ƙwarai.
A filistejski su knezovi izlazili u boj, ali koliko su god puta izlazili, David je imao više uspjeha nego svi Šaulovi dvorani; i tako ime njegovo posta vrlo slavno.

< 1 Sama’ila 18 >