< 1 Sama’ila 17 >

1 To, fa, Filistiyawa suka tattara mayaƙansu suka haɗu a Soko cikin Yahuda domin yaƙi. Suka yi sansani a Efes-Dammim, tsakanin Soko da Azeka.
Forsothe Filisteis gaderiden her cumpenyes in to batel, and camen togidere in Socoth of Juda, and settiden tentis bitwixe Socoth and Azecha, in the coostis of Domyn.
2 Shawulu da Isra’ilawa suka taru suka yi sansani a Kwarin Ela suka ja dāgā don su yi yaƙi da Filistiyawa.
Sotheli Saul and the men of Israel weren gaderid, and camen in to the valey of Terebynte, and dressiden scheltrun to fiyte ayens Filisteis.
3 Filistiyawa suka zauna a tudu guda, Isra’ilawa kuma suka zauna a ɗaya tudun. Kwari yana a tsakaninsu.
And Filisteis stoden aboue the hil on this part, and Israel stood on the hil on the tother part of the valey, that was bitwixe hem.
4 Wani jarumin da ake kira Goliyat wanda ya fito daga Gat, ya fita daga sansanin Filistiyawa. Tsawonsa ya fi ƙafa tara.
And a man, `sone of a widewe, whos fadir was vncerteyn, yede out of the `castels of Filisteis, Goliath bi name of Geth, of sixe cubitis heiy and a spanne; and a brasun basynet on his heed;
5 Ya sa hular kwanon da aka yi da tagulla, da rigar ƙarfe mai sulke, nauyin rigar ya kai shekel dubu biyar.
and he was clothid with `an haburioun hokid, ether mailid; forsothe the weiyte of his haburioun was fyue thousynde siclis of bras;
6 A ƙafafunsa kuwa ya sa ƙarafar tagulla, rataye a bayansa kuma māshi ne na tagulla.
and he hadde `bootis of bras in the hipis, and a `scheld of bras hilide hise schuldris.
7 Ƙotar kibiyarsa kuwa kamar sandar saƙar igiya take, ƙarfen kibiyar kuma nauyinsa ya kai shekel ɗari shida. Mai riƙe masa garkuwa yana tafe a gabansa.
Forsothe `the schaft of his spere was as the beem of webbis; forsothe thilke yrun of his spere hadde sixe hundrid siclis of yrun; and his squier yede bifor hym.
8 Goliyat ya tsaya ya tā da murya wa hafsoshin Isra’ila ya ce, “Me ya sa kuka fito kuna layi don yaƙi? Ni ba Bafilistin ba ne? Ku kuma ba bayin Shawulu ba ne? Ku zaɓi waninku yă zo nan.
And he stood, and cried ayens the cumpenyes of armed men of Israel, and seide to hem, Why camen ye redi to batel? Whether Y am not a Filistei, and ye ben the seruauntis of Saul? Chese ye a man of you, and come he doun to syngulere batel;
9 In zai iya yin faɗa har yă kashe ni, to, za mu zama bayinku. Amma in na fi ƙarfinsa na kashe shi, to, sai ku zama bayinmu, ku kuma yi mana bauta.”
if he may fiyte with me, and sleeth me, we schulen be `seruauntis to you; forsothe if Y haue the maystry, and sle hym, ye schulen be boonde, and `ye schulen serue vs.
10 Sai Bafilistin ya ce, “A wannan rana, na kalubalanci sojojin Isra’ila, ku ba ni mutum ɗaya mu yi faɗa.”
And `the Filistei seide, Y haue `seyd schenschip to dai to the cumpenyes of Israel; yyue ye a man, and bigynne he `synguler batel with me.
11 Da jin maganganun Bafilistin, sai Shawulu da dukan Isra’ila suka damu suka kuma ji tsoro.
Sotheli Saul and alle men of Israel herden siche wordis of `the Filistey, and thei weren astonyed, and dredden greetli.
12 To, Dawuda dai ɗan wani mutumin Efratawa ne mai suna Yesse, shi mutumin Betlehem ne a cikin Yahudiya. Yesse yana da yara maza takwas, a zamanin Shawulu kuwa, Yesse ya riga ya tsufa.
Forsothe Dauid was `the sone of a man of Effrata, of whom it is `biforseid, of Bethleem of Juda, to `which man the name was Isay, which hadde eiyte sones; and `the man was eld in the daies of Saul, and of greet age among men.
13 Manyan’ya’yansa maza uku, sun bi Shawulu wajen yaƙi. Ɗansa na fari shi ne Eliyab, na biyu shi ne Abinadab, na uku kuwa shi ne Shamma.
Sotheli thre grettere sones of Ysai yeden after Saul in to batel; and the names of hise thre sones, that yeden to batel, Heliab, the firste gendryd, and the secounde, Amynadab, and the thridde, Samma.
14 Dawuda shi ne ɗan autansu. Manyan’yan mazan nan uku suka bi Shawulu.
Forsothe Dauid was the leeste. Therfor while thre grettere sueden Saul, Dauid yede,
15 Amma Dawuda yakan tafi sansanin Shawulu lokaci-lokaci yă kuma koma Betlehem don yă yi kiwon tumakin mahaifinsa.
and turnede ayen fro Saul, that he schulde kepe the floc of his fadir in Bethleem.
16 Kwana arba’in cif, Bafilistin nan ya yi ta fitowa kowane safe da kuma kowace yamma.
Forsothe the Filistey cam forth in the morewtid, and euentid; and stood `bi fourti daies.
17 Yesse ya ce wa ɗansa Dawuda, “Ka ɗauki wannan gasasshen hatsi da waɗannan curin burodi goma, ka kai wa’yan’uwanka a sansani da sauri.
Sotheli Ysai seide to Dauid his sone, Take thou to thi britheren meete maad of meele, the mesure of ephi, and these ten looues, and renne thou in to the castels to thi britheren;
18 Ka haɗa da waɗannan cuku guda goma, ka kai wa komandan rundunarsu. Ka ga lafiyar’yan’uwanka, ka kawo mini labari daga wurinsu.
and thou schalt bere to the tribune these ten `litil formes of chese; and thou schalt visite thi britheren, whether thei doon riytli, and lurne thou, with whiche men thei ben ordeyned.
19 Suna tare da Shawulu da kuma dukan mutanen Isra’ila a Kwarin Ela, suna can suna yaƙi da Filistiyawa.”
Forsothe Saul, and thei, and alle the sones of Israel in the valei of Terebynte fouyten ayens Filisteis.
20 Kashegari da sassafe, Dawuda ya tashi ya bar tumakinsa wa wani yă lura da su, sai ya ɗauki kayansa, ya kama hanya kamar yadda Yesse ya umarce shi. Ya isa sansanin daidai sa’ad da rundunar tana fitowa zuwa bakin dāgā, suna kirarin yaƙi.
Therfor Dauid roos eerli, and bitook the floc to the kepere, and he yede chargid, as Ysai `hadde comaundid to hym; and he cam to the place Magala, and to the oost, which oost yede out to the batel, and criede in `the batel.
21 Isra’ila da Filistiyawa suka ja dāgā suna fuskantar junansu.
For Israel hadde dressid scheltrun; `but also Filisteis weren maad redi `euen ayens.
22 Dawuda ya bar kayansa a wajen wani mai lura da kaya, sai ya ruga zuwa bakin dāgā yă gai da’yan’uwansa.
Therfor Dauid lefte the vessels, whiche he hadde brouyt, vndur the hond of a kepere `at the fardels, and he ran to the place of batel, and he axyde, if alle thingis weren `doon riytli anentis hise britheren.
23 Da yana magana da su sai Goliyat, jarumin nan Bafilistin daga Gat ya fito daga rundunar Filistiyawa, ya tā da murya kamar yadda ya saba. Dawuda kuwa ya ji shi.
And whanne he spak yit to hem, thilke bastard apperide, Goliath bi name, a Filistei of Geth, and stiede fro the castels of Filisteis; and `while he spak these same wordis, Dauid herde.
24 Da Isra’ilawa suka ga mutumin, sai dukansu suka gudu saboda tsananin tsoro.
And whanne alle men of Israel hadden seyn `the man, thei fledden fro his face, and dredden hym greetli.
25 Isra’ilawa suka yi ta cewa, “Kun ga yadda wannan mutum yana ta fitowa? Yana fitowa ne don yă kalubalanci Isra’ila. Sarki zai sāka wa mutumin da ya kashe wannan da dukiya mai yawa. Zai kuma ba shi’yarsa yă aura, yă cire suna mahaifinsa daga biyan kuɗin haraji cikin Isra’ila.”
And ech man of Israel seide, Whether thou hast seyn this man that stiede? for he stiede to seie schenship to Israel; therfor the kyng schal make riche with greet richessis `the man that sleeth thilke Filistei; and the kyng schal yyue his douyter to that man, and schal make the hows of his fader with out `tribut in Israel.
26 Dawuda ya tambayi mutanen da suke tsaye kusa da shi ya ce, “Me za a yi wa wanda ya kashe Bafilistin nan, ya kuma cire wannan kunya daga Isra’ila? Wane ne wannan bafilistin marar kaciya da yake kalubalantar rundunar yaƙi na Allah mai rai?”
And Dauyd spak to the men that stoden with hym, and seide, What schal be youun to the man that sleeth this Filistei, and doith awei schenschip fro Israel? for who is this Filistei vncircumcidid, that dispiside the scheltruns of God lyuynge?
27 Sai suka sāke gaya masa abin da suka faɗa cewa, “Ga abin da zai faru da wanda ya kashe shi.”
Forsothe the puple tolde to hym the same word, and seide, These thingis schulen be youun to the man that sleeth hym.
28 Da wansa Eliyab, ya ji yana magana da mutanen, sai ransa ya ɓace ƙwarai saboda fushi, sai ya ce wa Dawuda, “Me ka zo yi a nan? Wa kuma ka bar wa’yan tumakin a jeji? Na san ka da taurinkai, da kuma mugun hali. Ka zo nan ne don ka yi kallon yaƙi kawai.”
And whanne Heliab, `his more brother, had herd this, while he spak with othere men, he was wrooth ayens Dauid, and seide, Whi camest thou, and whi `leftist thou tho fewe scheep in deseert? Y knowe thi pride, and the wewardnesse of thin herte; for thou camest doun to se the batel.
29 Dawuda ya ce, “To, yanzu me na yi? Ba zan ma yi magana ba?”
And Dauid seide, What haue Y do? Whether it is not a word?
30 Sai ya juya wajen wani kuma ya sāke kawo zancen, mutanen kuwa suka amsa masa kamar dā.
And Dauid bowide a litil fro hym to another man; and Dauid seide the same word, and the puple answeride to hym al word as bifore.
31 Aka ji abin da Dawuda ya ce, aka kuwa gaya wa Shawulu, Shawulu kuma ya aika a kawo shi.
Forsothe these wordis weren herd, whiche Dauid spak, and weren teld `in the siyt of Saul.
32 Da Shawulu ya tambayi Dawuda, sai Dawuda ya ce masa, “Kada kowa yă damu saboda wannan Bafilistin. Bawanka zai je yă yi faɗa da shi.”
And whanne Dauyd was brouyt to Saul, Dauyd spak to hym, The herte of ony man falle not doun for `that Filistei, Y thi seruaunt schal go, and `Y schal fiyte ayens the Filistei.
33 Shawulu ya ce, “Ba za ka iya yin faɗa da wannan Bafilistin ba, ya daɗe yana yaƙi, ya yi yaƙi tun yana saurayi. Ga shi kuwa kai ɗan yaro ne kawai.”
And Saul seide to Dauid, Thou maist not ayenstonde this Filistei, nether fiyte ayens hym, for thou art a child; forsothe this man is a werriour fro his yong wexynge age.
34 Amma Dawuda ya ce wa Shawulu, “Bawanka yana kiwon tumakin mahaifinsa. Sa’ad da zaki ko beyar ta zo ta kama tunkiya, ta tafi da ita.
And Dauid seide to Saul, Thi seruaunt kepte `the floc of his fadir, and a lioun cam, ether a bere, and took awei a ram fro the myddis of the floc;
35 Nakan bi ta a baya in buga ta in kuma ƙwato tunkiyar daga bakinta. In kuma ta taso mini, nakan cafke ta a gashinta in buga ta in kashe.
Y pursuede, and killide hem, and rauyschide fro `the mouth of hem; and thei risiden ayens me, and I took the nether chaule `of hem, and Y stranglide, and killide hem.
36 Bawanka ya kashe zaki da beyar, wannan Bafilistin marar kaciya zai zama kamar ɗaya daga cikinsu, domin ya rena rundunar Allah mai rai.
For Y thi seruaunt killide bothe a lioun and a bere; therfor and this Filistei vncircumcidid schal be as oon of hem. Now Y schal go, and Y schal do awey the schenschip of the puple; for who is this Filistei vncircumcidid, that was hardi to curse the oost of God lyuynge?
37 Ubangiji wanda ya cece ni daga kumbar zaki da kuma kumbar beyar, zai cece ni daga hannun wannan Bafilistin.” Shawulu ya ce wa Dawuda, “Je ka, Ubangiji yă kasance tare da kai.”
And Dauid seide, The Lord that delyuerede me fro the `mouth of the lioun, and fro the `hond, that is, power, of the bere, he schal delyuere me fro the hond of this Filistei. Forsothe Saul seide to Dauid, Go thou, and the Lord be with thee.
38 Sai Shawulu ya kawo kayan yaƙinsa ya sa wa Dawuda. Ya sa masa hular kwanon da aka yi da tagulla a kansa, ya kuma sa masa rigar ƙarfensa.
And Saul clothide Dauid with hise clothis, and puttide a brasun basynet on his heed, and clothide hym with an haburioun.
39 Dawuda ya ɗaura māshin Shawulu a sulken, ya yi ƙoƙari yă zaga, sai ya ji ba zai iya ba saboda bai saba ba. Ya cewa Shawulu, “Ba zan iya tafiya da waɗannan ba, domin ban saba ba.” Don haka ya tuɓe su.
Therfor Dauid was gird with his swerd on his cloth, and bigan to asaie if he myyte go armed; for he hadde not custom. And Dauid seide to Saul, Y may not go so, for Y haue not vss. And Dauid puttide awei tho,
40 Sai ya ɗauki sandansa, ya zaɓi duwatsu guda biyar masu sulɓi daga cikin rafi, ya sa su a’yar jakarsa ta makiyaya; ya kuma ɗauki majajjawarsa, ya tafi, yă fuskanci Bafilistin.
and he took his staaf, which he hadde euere in the hondis. And he chees to hym fyue clereste stonys, that is, harde, pleyn, and rounde, of the stronde; and he sente tho in to the schepherdis scrippe, which he hadde with hym; and he took the slynge in the hond, and yede forth ayens the Filistei.
41 Ana ciki haka, sai Bafilistin nan shi ma ya fita yana gusowa zuwa wurin Dawuda. Mai riƙe masa garkuwar yaƙi kuwa yana tafe a gabansa.
Sotheli the Filistei yede, `goynge and neiyyng ayens Dauid; and his squyer yede bifor hym.
42 Bafilistin ya dubi Dawuda daga sama har ƙasa, ya gan dai ɗan yaro ne kawai, kyakkyawa kuma mai ƙoshin lafiya, sai ya rena shi.
And whanne `the Filistei hadde biholde Dauid, and hadde seyn hym, he dispiside Dauid; forsothe Dauid was a yong wexynge man, rodi, and feir in siyt.
43 Ya ce masa, “Kana tsammani ni kare ne da za ka zo mini da sanda?” Sai ya la’anci Dawuda da sunayen allolin Filistiyawa.
And `the Filistei, seide to Dauid, Whether Y am a dogge, for thou comest to me with a staf? And `the Filistei curside Dauid in hise goddis; and he seide to Dauid,
44 Ya ce, “Zo nan, ni kuwa zan ba da naman jikinka ga tsuntsayen sama da namun jeji su ci.”
Come thou to me, and Y schal yyue thi fleischis to the `volatilis of heuene, and to the beestis of erthe.
45 Dawuda ya ce wa Bafilistin, “Kana zuwa ka yaƙe ni da māshi da takobi da kere, amma ni ina zuwa in yaƙe ka a cikin sunan Ubangiji Maɗaukaki, Allah na rundunar Isra’ila, wanda ka rena.
Sotheli Dauid seide to `the Filistei, Thou comest to me with swerd, and spere, and scheeld; but Y come to thee in the name of the Lord God of oostis, of God of the cumpanyes of Israel, to whiche thou seidist schenschip to dai.
46 Yau nan, Ubangiji zai bashe ka a hannuna, zan kuwa kashe ka, in datse kanka. Yau, zan ba da gawawwakin rundunar Filistiyawa ga tsuntsayen sama da namun jeji, da haka duniya za tă sani lalle akwai Allah a cikin Isra’ila.
And the Lord schal yyue thee in myn hond, and Y schal sle thee, and Y schal take awey thin heed fro thee; and I schal yyue the deed bodies of the castels of Filisteis `to day to the volatils of heuene, and to the beestis of erthe; that al the erthe wite, that the Lord God is in Israel,
47 Duk waɗanda suka taru a nan za su san cewa ba da māshi ko takobi ne Ubangiji yake ceto ba, gama yaƙin nan na Ubangiji ne, shi kuwa zai bashe ku duka a hannuwanmu.”
and that al this chirche knowe, that the Lord saueth not in swerd nether in spere; for the batel is his, and he schal bitake you in to oure hondis.
48 Yayinda Bafilistin yana matsowa kusa domin yă fāɗa wa Dawuda, sai Dawuda ya ruga a guje zuwa bakin dāgā don yă same shi.
Therfor whanne the Filistei hadde rise, and cam, and neiyede ayens Dauid, Dauid hastide, and ran to batel ayens `the Filistei.
49 Ya sa hannu a jakarsa ya ɗauki dutse, ya sa cikin majajjawa ya wurga, dutsen kuwa ya bugi Bafilistin a goshi, dutsen ya shiga cikin goshinsa, sai Bafilistin ya fāɗi rubda ciki.
And Dauid putte his hond `in to his scrippe, and he took o stoon, and he castide with the slynge, `and ledde aboute, and smoot `the Filistei in the forheed; and the stoon was fastned in his forheed, and he felde doun in to his face on the erthe.
50 Da majajjawa da dutse kawai Dawuda ya ci nasara a kan Bafilistin. Ya buge shi, ya kashe shi ba tare da takobi a hannunsa ba.
And Dauid hadde the maistrie ayens `the Filistei `in a slyng and stoon, and he killide `the Filistei smytun. And whanne Dauid hadde no swerd in the hond,
51 Dawuda ya ruga ya tsaya a bisan Bafilistin, ya zare takobin Bafilistin daga kubensa, ya datse masa kai da shi. Da Filistiyawa suka ga jaruminsu ya mutu, sai suka juya suka gudu.
he ran, and stood on `the Filistei, and took his swerd; and Dauid drow out the swerd of his schethe, and `killide him, and kittide awei his heed. Forsothe the Filisteis sien, that the strongeste of hem was deed, and thei fledden.
52 Mutanen Isra’ila da na Yahuda suka rugo gaba da babbar murya, suka fafari Filistiyawa har zuwa mashigin Gat da kuma ƙofofin Ekron. Gawawwakin Filistiyawa suka bazu a hanyar Sha’arayim zuwa Gat da kuma Ekron.
And the sones of Israel and of Juda risiden to gidere, and crieden, and pursueden Filisteis, `til the while thei camen in to the valei, and `til to the yate of Accaron. And woundid men of Filisteis felden in the weye of Sarym, and `til to Geth, and `til to Accaron.
53 Da Isra’ilawa suka komo daga bin Filistiyawa sai suka washe sansanin Filistiyawa.
And the sones of Israel turneden ayen, aftir that thei hadden pursuede Filisteis, and thei assailiden `the tentis of hem.
54 Dawuda ya ɗauki kan Bafilistin zuwa Urushalima. Sai Dawuda ya ajiye kayan yaƙin Bafilistin a tentinsa.
Forsothe Dauid took the heed of `the Filistei, and brouyte it in to Jerusalem; sotheli he puttide hise armeris in the `tabernacle of the Lord.
55 Yayinda Shawulu yake kallon Dawuda sa’ad da za shi yă yaƙi Bafilistin, sai ya tambayi Abner, komandan rundunarsa ya ce, “Abner, ɗan wane ne wannan saurayi?” Abner ya ce ran sarki yă daɗe, “Ban sani ba.”
Forsothe in that tyme in which Saul siy Dauid goynge out ayens `the Filistei, he seide to Abner, prince of his chiualrie, Abner, of what generacioun `cam forth this yong waxynge man? And Abner seide, Kyng, thi soule lyueth, I knowe not.
56 Sarki ya ce, “Ka tambaya mini ko yaron wane ne wannan saurayi.”
And the kyng seide, Axe thou, whos sone this child is.
57 Dawuda yana dawowa daga karkashe Filistiyawa ke nan, sai Abner ya kai shi gaban Shawulu, riƙe da kan Bafilistin.
And whanne Dauid hadde come ayen, whanne `the Filistei was slayn, Abner took Dauid, and brouyte hym in, hauynge in the hond the heed of `the Filistei, `bifor Saul.
58 Sai Shawulu ya ce, “Kai ɗan wane ne, saurayi?” Dawuda ya ce, “Ni ɗan bawanka Yesse ne, na Betlehem.”
And Saul seide to hym, Of what generacioun art thou, yong waxynge man? And Dauid seide, Y am the sone of thi seruaunt, Isai of Bethleem.

< 1 Sama’ila 17 >