< 1 Sama’ila 17 >
1 To, fa, Filistiyawa suka tattara mayaƙansu suka haɗu a Soko cikin Yahuda domin yaƙi. Suka yi sansani a Efes-Dammim, tsakanin Soko da Azeka.
And the Philistines gathered together their hosts, unto battle, and they were gathered together unto Socoh, which belongeth unto Judah, —and they encamped between Socoh and Azekah in Ephes-dammim;
2 Shawulu da Isra’ilawa suka taru suka yi sansani a Kwarin Ela suka ja dāgā don su yi yaƙi da Filistiyawa.
and, Saul and the men of Israel, gathered themselves together, and encamped in the vale of Elah, and set the army in array against the Philistines.
3 Filistiyawa suka zauna a tudu guda, Isra’ilawa kuma suka zauna a ɗaya tudun. Kwari yana a tsakaninsu.
And, the Philistines, were standing near the hill on one side, and, the Israelites, were standing near the hill on the other side, —while, the valley, was between them.
4 Wani jarumin da ake kira Goliyat wanda ya fito daga Gat, ya fita daga sansanin Filistiyawa. Tsawonsa ya fi ƙafa tara.
And there came forth a champion out of the camp of the Philistines, Goliath, his name, from Gath, —his height, six cubits and a span;
5 Ya sa hular kwanon da aka yi da tagulla, da rigar ƙarfe mai sulke, nauyin rigar ya kai shekel dubu biyar.
with a helmet of bronze on his head, and, with a scaly coat of mail, was he clad, —the weight of the coat, being five thousand shekels of bronze;
6 A ƙafafunsa kuwa ya sa ƙarafar tagulla, rataye a bayansa kuma māshi ne na tagulla.
and, greaves of bronze, on his feet, —and, a javelin of bronze, between his shoulders;
7 Ƙotar kibiyarsa kuwa kamar sandar saƙar igiya take, ƙarfen kibiyar kuma nauyinsa ya kai shekel ɗari shida. Mai riƙe masa garkuwa yana tafe a gabansa.
and, the shaft of his spear, was like a weaver’s beam, and, the flashing head of his spear, was six hundred shekels of iron, —and, his shield-bearer, was coming on before him.
8 Goliyat ya tsaya ya tā da murya wa hafsoshin Isra’ila ya ce, “Me ya sa kuka fito kuna layi don yaƙi? Ni ba Bafilistin ba ne? Ku kuma ba bayin Shawulu ba ne? Ku zaɓi waninku yă zo nan.
And he took his stand, and cried unto the ranks of Israel, and said unto them, Wherefore should ye come out, to set in array for battle? Am not, I, a Philistine, while, ye, are servants unto Saul? Choose you a man, and let him come down unto me:
9 In zai iya yin faɗa har yă kashe ni, to, za mu zama bayinku. Amma in na fi ƙarfinsa na kashe shi, to, sai ku zama bayinmu, ku kuma yi mana bauta.”
If he prevail in fighting with me, and smite me, then will we become your servants, —but, if, I, prevail over him, and smite him, then shall ye become our servants, and serve, us.
10 Sai Bafilistin ya ce, “A wannan rana, na kalubalanci sojojin Isra’ila, ku ba ni mutum ɗaya mu yi faɗa.”
And the Philistine said—I, reproach the ranks of Israel, this day, —give me a man, that we may fight together.
11 Da jin maganganun Bafilistin, sai Shawulu da dukan Isra’ila suka damu suka kuma ji tsoro.
When Saul and all Israel heard these words of the Philistine, they were dismayed, and feared exceedingly.
12 To, Dawuda dai ɗan wani mutumin Efratawa ne mai suna Yesse, shi mutumin Betlehem ne a cikin Yahudiya. Yesse yana da yara maza takwas, a zamanin Shawulu kuwa, Yesse ya riga ya tsufa.
Now, David, was the son of that Ephrathite of Bethlehem-judah, whose, name, was Jesse, and, who, had eight sons, —and, the man, in the days of Saul was old, advanced in years.
13 Manyan’ya’yansa maza uku, sun bi Shawulu wajen yaƙi. Ɗansa na fari shi ne Eliyab, na biyu shi ne Abinadab, na uku kuwa shi ne Shamma.
And the three eldest sons of Jesse had followed Saul to the battle, —and, the names of his three sons who went into the battle, were Eliab the firstborn, and, the next to him, Abinadab, and, the third, Shammah.
14 Dawuda shi ne ɗan autansu. Manyan’yan mazan nan uku suka bi Shawulu.
But, as for David, he, was the youngest, —and, the three eldest, followed Saul;
15 Amma Dawuda yakan tafi sansanin Shawulu lokaci-lokaci yă kuma koma Betlehem don yă yi kiwon tumakin mahaifinsa.
whereas, David, kept going and returning from Saul, —to tend his father’s sheep at Bethlehem.
16 Kwana arba’in cif, Bafilistin nan ya yi ta fitowa kowane safe da kuma kowace yamma.
And the Philistine drew near morning and evening, —and presented himself forty days.
17 Yesse ya ce wa ɗansa Dawuda, “Ka ɗauki wannan gasasshen hatsi da waɗannan curin burodi goma, ka kai wa’yan’uwanka a sansani da sauri.
And Jesse said unto David his son, Take, I pray thee, unto thy brethren—this ephah of parched corn, and these ten loaves, —and run to the camp unto thy brethren;
18 Ka haɗa da waɗannan cuku guda goma, ka kai wa komandan rundunarsu. Ka ga lafiyar’yan’uwanka, ka kawo mini labari daga wurinsu.
also these ten slices of soft cheese, shalt thou take to the captain of their thousand, —and, as for thy brethren, give good heed to their welfare, their pledge, also shalt thou receive.
19 Suna tare da Shawulu da kuma dukan mutanen Isra’ila a Kwarin Ela, suna can suna yaƙi da Filistiyawa.”
Now, Saul, and they, and all the men of Israel, were in the vale of Elah, ready to fight with the Philistines.
20 Kashegari da sassafe, Dawuda ya tashi ya bar tumakinsa wa wani yă lura da su, sai ya ɗauki kayansa, ya kama hanya kamar yadda Yesse ya umarce shi. Ya isa sansanin daidai sa’ad da rundunar tana fitowa zuwa bakin dāgā, suna kirarin yaƙi.
So then David rose up early in the morning, and entrusted the sheep to a keeper, and took up [the provisions] and went his way, as Jesse had commanded him, —and came into the circular rampart, as, the force, was going forth into the ranks, and shouted for the fight.
21 Isra’ila da Filistiyawa suka ja dāgā suna fuskantar junansu.
So Israel and the Philistines set in array for battle, army against army.
22 Dawuda ya bar kayansa a wajen wani mai lura da kaya, sai ya ruga zuwa bakin dāgā yă gai da’yan’uwansa.
Then David entrusted the provisions that were upon him to the care of the keeper of the stores, and ran unto the ranks, —and came and asked for the welfare of his brethren.
23 Da yana magana da su sai Goliyat, jarumin nan Bafilistin daga Gat ya fito daga rundunar Filistiyawa, ya tā da murya kamar yadda ya saba. Dawuda kuwa ya ji shi.
Now, as he was speaking with them, lo! the champion coming up, Goliath the Philistine, by name, of Gath, [coming up] out of the ranks of the Philistines, and he spake according to these words, —and David heard [them].
24 Da Isra’ilawa suka ga mutumin, sai dukansu suka gudu saboda tsananin tsoro.
Now, all the men of Israel, when they saw the man, fled from before him, and feared exceedingly.
25 Isra’ilawa suka yi ta cewa, “Kun ga yadda wannan mutum yana ta fitowa? Yana fitowa ne don yă kalubalanci Isra’ila. Sarki zai sāka wa mutumin da ya kashe wannan da dukiya mai yawa. Zai kuma ba shi’yarsa yă aura, yă cire suna mahaifinsa daga biyan kuɗin haraji cikin Isra’ila.”
And the men of Israel said—Have ye seen this man that is coming up? For, to reproach Israel, is he coming. So then it shall be, that, the man that shall smite him, the same, will the king enrich with great riches, and, his own daughter, will give him, and, his father’s house, will he make free in Israel.
26 Dawuda ya tambayi mutanen da suke tsaye kusa da shi ya ce, “Me za a yi wa wanda ya kashe Bafilistin nan, ya kuma cire wannan kunya daga Isra’ila? Wane ne wannan bafilistin marar kaciya da yake kalubalantar rundunar yaƙi na Allah mai rai?”
Then spake David unto the men that were standing by him, saying, What shall be done to the man that shall smite yonder Philistine, and so shall take away reproach from off Israel? For who is this uncircumcised Philistine that he hath reproached the ranks of a Living God?
27 Sai suka sāke gaya masa abin da suka faɗa cewa, “Ga abin da zai faru da wanda ya kashe shi.”
And the people answered him, according to this word saying, —So, shall it be done to the man that shall smite him.
28 Da wansa Eliyab, ya ji yana magana da mutanen, sai ransa ya ɓace ƙwarai saboda fushi, sai ya ce wa Dawuda, “Me ka zo yi a nan? Wa kuma ka bar wa’yan tumakin a jeji? Na san ka da taurinkai, da kuma mugun hali. Ka zo nan ne don ka yi kallon yaƙi kawai.”
Now Eliab his eldest brother heard when he spake unto the men, —then was kindled the anger of Eliab against David, and he said—Wherefore is it that thou hast come down? and to whom hast thou entrusted those few sheep in the wilderness? I, know thy pride, and the foolishness of thy heart, for, to see the battle, hast thou come down.
29 Dawuda ya ce, “To, yanzu me na yi? Ba zan ma yi magana ba?”
And David said, What have I done, now? Was there not, a cause?
30 Sai ya juya wajen wani kuma ya sāke kawo zancen, mutanen kuwa suka amsa masa kamar dā.
Then turned he from him unto another, and said—according to this word, —and the people returned him an answer, like the first.
31 Aka ji abin da Dawuda ya ce, aka kuwa gaya wa Shawulu, Shawulu kuma ya aika a kawo shi.
And the words which David spake were overheard, —and, when they told them before Saul, he summoned him.
32 Da Shawulu ya tambayi Dawuda, sai Dawuda ya ce masa, “Kada kowa yă damu saboda wannan Bafilistin. Bawanka zai je yă yi faɗa da shi.”
And David said unto Saul, Let not the heart of my lord fail, because of him, —thy servant, will go, and fight with this Philistine.
33 Shawulu ya ce, “Ba za ka iya yin faɗa da wannan Bafilistin ba, ya daɗe yana yaƙi, ya yi yaƙi tun yana saurayi. Ga shi kuwa kai ɗan yaro ne kawai.”
And Saul said unto David—Thou art not able to go against this Philistine, to fight with him, —for, a youth, art, thou, but, he, a man of war, from his youth.
34 Amma Dawuda ya ce wa Shawulu, “Bawanka yana kiwon tumakin mahaifinsa. Sa’ad da zaki ko beyar ta zo ta kama tunkiya, ta tafi da ita.
Then said David unto Saul, Thy servant used to tend his father’s sheep, —and there would come a lion, or a bear, and carry off a lamb out of the flock;
35 Nakan bi ta a baya in buga ta in kuma ƙwato tunkiyar daga bakinta. In kuma ta taso mini, nakan cafke ta a gashinta in buga ta in kashe.
and I would go out after him, and smite him, and rescue it out of his mouth, —and, if he rose against me, I would catch him by his beard, and smite him, and slay him.
36 Bawanka ya kashe zaki da beyar, wannan Bafilistin marar kaciya zai zama kamar ɗaya daga cikinsu, domin ya rena rundunar Allah mai rai.
Thy servant could slay, either a lion or a bear, —and, this uncircumcised Philistine, shall become, as one of them, for he hath reproached the ranks of a Living God.
37 Ubangiji wanda ya cece ni daga kumbar zaki da kuma kumbar beyar, zai cece ni daga hannun wannan Bafilistin.” Shawulu ya ce wa Dawuda, “Je ka, Ubangiji yă kasance tare da kai.”
And David said, Yahweh, who hath rescued me out of the power of the lion, and out of the power of the bear, he, will rescue us out of the hand of this Philistine. Then said Saul unto David—Go! and, Yahweh, will be with thee.
38 Sai Shawulu ya kawo kayan yaƙinsa ya sa wa Dawuda. Ya sa masa hular kwanon da aka yi da tagulla a kansa, ya kuma sa masa rigar ƙarfensa.
And Saul clad David with his own military coat, and set a helmet of bronze upon his head, —and clad him with a coat of mail.
39 Dawuda ya ɗaura māshin Shawulu a sulken, ya yi ƙoƙari yă zaga, sai ya ji ba zai iya ba saboda bai saba ba. Ya cewa Shawulu, “Ba zan iya tafiya da waɗannan ba, domin ban saba ba.” Don haka ya tuɓe su.
And David girded his sword above his military coat, but was reluctant to go, for he had not proved them, —so David said unto Saul—I cannot go in these, for I have not proved them. And David put them off him.
40 Sai ya ɗauki sandansa, ya zaɓi duwatsu guda biyar masu sulɓi daga cikin rafi, ya sa su a’yar jakarsa ta makiyaya; ya kuma ɗauki majajjawarsa, ya tafi, yă fuskanci Bafilistin.
Then took he his stick in his hand, and chose him five smooth stones out of the torrent-bed, and put them in the shepherd’s-pouch which he had—even in the wallet, and had his sling in his hand, —and so drew near unto the Philistine.
41 Ana ciki haka, sai Bafilistin nan shi ma ya fita yana gusowa zuwa wurin Dawuda. Mai riƙe masa garkuwar yaƙi kuwa yana tafe a gabansa.
And the Philistine came on and on, and drew near unto David, —and the man carrying the shield was before him.
42 Bafilistin ya dubi Dawuda daga sama har ƙasa, ya gan dai ɗan yaro ne kawai, kyakkyawa kuma mai ƙoshin lafiya, sai ya rena shi.
And, when the Philistine looked about, and saw David, he disdained him, —for he was a youth, and ruddy, a stripling of fair countenance.
43 Ya ce masa, “Kana tsammani ni kare ne da za ka zo mini da sanda?” Sai ya la’anci Dawuda da sunayen allolin Filistiyawa.
Then said the Philistine unto David, A dog, am, I, that thou art coming unto me, with sticks? And the Philistine cursed David, by his god.
44 Ya ce, “Zo nan, ni kuwa zan ba da naman jikinka ga tsuntsayen sama da namun jeji su ci.”
And the Philistine said unto David, —Come, unto me, that I may give thy flesh to the birds of heaven, and to the beasts of the field.
45 Dawuda ya ce wa Bafilistin, “Kana zuwa ka yaƙe ni da māshi da takobi da kere, amma ni ina zuwa in yaƙe ka a cikin sunan Ubangiji Maɗaukaki, Allah na rundunar Isra’ila, wanda ka rena.
Then said David unto the Philistine—Thou, art coming unto me with sword, and with spear, and with javelin, —but, I, am coming unto thee in the name of Yahweh of hosts, God of the ranks of Israel which thou hast reproached.
46 Yau nan, Ubangiji zai bashe ka a hannuna, zan kuwa kashe ka, in datse kanka. Yau, zan ba da gawawwakin rundunar Filistiyawa ga tsuntsayen sama da namun jeji, da haka duniya za tă sani lalle akwai Allah a cikin Isra’ila.
This day, will Yahweh deliver thee into my hand, and I will smite thee, and take thy head from off thee, and will give thy dead body and the dead bodies of the host of Philistines, this day, unto the birds of heaven, and unto the wild beasts of the earth, —that all the earth may know that Israel hath a God;
47 Duk waɗanda suka taru a nan za su san cewa ba da māshi ko takobi ne Ubangiji yake ceto ba, gama yaƙin nan na Ubangiji ne, shi kuwa zai bashe ku duka a hannuwanmu.”
and that all this gathered host may know that, not with sword and with spear, doth Yahweh save, —for, unto Yahweh, belongeth the battle, and he will deliver you into our hand.
48 Yayinda Bafilistin yana matsowa kusa domin yă fāɗa wa Dawuda, sai Dawuda ya ruga a guje zuwa bakin dāgā don yă same shi.
And it came to pass, when the Philistine arose, and came and drew near to meet David, that David hasted, and ran toward the ranks to meet the Philistine.
49 Ya sa hannu a jakarsa ya ɗauki dutse, ya sa cikin majajjawa ya wurga, dutsen kuwa ya bugi Bafilistin a goshi, dutsen ya shiga cikin goshinsa, sai Bafilistin ya fāɗi rubda ciki.
And David thrust his hand into his pouch, and took from thence a stone, and slang it, and smote the Philistine, in his forehead, —that the stone sank into his forehead, and he fell upon his face, to the earth.
50 Da majajjawa da dutse kawai Dawuda ya ci nasara a kan Bafilistin. Ya buge shi, ya kashe shi ba tare da takobi a hannunsa ba.
Thus David prevailed over the Philistine, with the sling and with the stone, and smote the Philistine, and slew him, —but, sword, was there none in the hand of David.
51 Dawuda ya ruga ya tsaya a bisan Bafilistin, ya zare takobin Bafilistin daga kubensa, ya datse masa kai da shi. Da Filistiyawa suka ga jaruminsu ya mutu, sai suka juya suka gudu.
So David ran, and stood by the Philistine, and took his sword and drew it out of the sheath thereof, and slew him, and cut off, therewith, his head, —and, when the Philistines saw that their hero was slain, they fled.
52 Mutanen Isra’ila da na Yahuda suka rugo gaba da babbar murya, suka fafari Filistiyawa har zuwa mashigin Gat da kuma ƙofofin Ekron. Gawawwakin Filistiyawa suka bazu a hanyar Sha’arayim zuwa Gat da kuma Ekron.
Then arose the men of Israel and Judah, and shouted, and pursued the Philistines, as far as the entrance into Gath, and as far as the gates of Ekron, —and the slain of the Philistines fell in the way to the two gates, even as far as Gath and as far as Ekron.
53 Da Isra’ilawa suka komo daga bin Filistiyawa sai suka washe sansanin Filistiyawa.
And the sons of Israel returned from hotly pursuing the Philistines, —and plundered their camps.
54 Dawuda ya ɗauki kan Bafilistin zuwa Urushalima. Sai Dawuda ya ajiye kayan yaƙin Bafilistin a tentinsa.
And David took the head of the Philistine, and brought it into Jerusalem, —but, his armour, put he into his tent.
55 Yayinda Shawulu yake kallon Dawuda sa’ad da za shi yă yaƙi Bafilistin, sai ya tambayi Abner, komandan rundunarsa ya ce, “Abner, ɗan wane ne wannan saurayi?” Abner ya ce ran sarki yă daɗe, “Ban sani ba.”
And, when Saul saw David going forth to meet the Philistine, he said unto Abner, prince of the host, Whose son is the young man, Abner? And Abner said, By the life of thy soul, O king! I know not.
56 Sarki ya ce, “Ka tambaya mini ko yaron wane ne wannan saurayi.”
Then said the king, —Ask, thou, whose son the stripling is?
57 Dawuda yana dawowa daga karkashe Filistiyawa ke nan, sai Abner ya kai shi gaban Shawulu, riƙe da kan Bafilistin.
And, when David returned from smiting the Philistine, Abner took him, and brought him before Saul, —with the head of the Philistine in his hand.
58 Sai Shawulu ya ce, “Kai ɗan wane ne, saurayi?” Dawuda ya ce, “Ni ɗan bawanka Yesse ne, na Betlehem.”
And Saul said unto him, Whose son art, thou, O young man? And David said, Son of thy servant Jesse, the Bethlehemite.