< 1 Sama’ila 17 >

1 To, fa, Filistiyawa suka tattara mayaƙansu suka haɗu a Soko cikin Yahuda domin yaƙi. Suka yi sansani a Efes-Dammim, tsakanin Soko da Azeka.
Now the Philistines gathering together their troops to battle, assembled at Socho of Juda, and camped between Socho and Azeca in the borders of Dommim.
2 Shawulu da Isra’ilawa suka taru suka yi sansani a Kwarin Ela suka ja dāgā don su yi yaƙi da Filistiyawa.
And Saul and the children of Israel being gathered together came to the valley of Terebinth, and they set the army in array to fight against the Philistines.
3 Filistiyawa suka zauna a tudu guda, Isra’ilawa kuma suka zauna a ɗaya tudun. Kwari yana a tsakaninsu.
And the Philistines stood on a mountain on the one side, and Israel stood on a mountain on the other side: and there was a valley between them.
4 Wani jarumin da ake kira Goliyat wanda ya fito daga Gat, ya fita daga sansanin Filistiyawa. Tsawonsa ya fi ƙafa tara.
And there went out a man baseborn from the camp of the Philistines named Goliath, of Geth, whose height was six cubits and a span:
5 Ya sa hular kwanon da aka yi da tagulla, da rigar ƙarfe mai sulke, nauyin rigar ya kai shekel dubu biyar.
And he had a helmet of brass upon his head, and he was clothed with a coat of mail with scales, and the weight of his coat of mail was five thousand sicles of brass:
6 A ƙafafunsa kuwa ya sa ƙarafar tagulla, rataye a bayansa kuma māshi ne na tagulla.
And he had greaves of brass on his legs, and a buckler of brass covered his shoulders.
7 Ƙotar kibiyarsa kuwa kamar sandar saƙar igiya take, ƙarfen kibiyar kuma nauyinsa ya kai shekel ɗari shida. Mai riƙe masa garkuwa yana tafe a gabansa.
And the staff of his spear was like a weaver’s beam, and the head of his spear weighed six hundred sicles of iron: and his armourbearer went before him.
8 Goliyat ya tsaya ya tā da murya wa hafsoshin Isra’ila ya ce, “Me ya sa kuka fito kuna layi don yaƙi? Ni ba Bafilistin ba ne? Ku kuma ba bayin Shawulu ba ne? Ku zaɓi waninku yă zo nan.
And standing he cried out to the bands of Israel, and said to them: Why are you come out prepared to fight? am not I a Philistine, and you the servants of Saul? Choose out a man of you, and let him come down and fight hand to hand.
9 In zai iya yin faɗa har yă kashe ni, to, za mu zama bayinku. Amma in na fi ƙarfinsa na kashe shi, to, sai ku zama bayinmu, ku kuma yi mana bauta.”
If he be able to fight with me, and kill me, we will be servants to you: but if I prevail against him, and kill him, you shall be servants, and shall serve us.
10 Sai Bafilistin ya ce, “A wannan rana, na kalubalanci sojojin Isra’ila, ku ba ni mutum ɗaya mu yi faɗa.”
And the Philistine said: I have defied the bands of Israel this day: Give me a man, and let him fight with me hand to hand.
11 Da jin maganganun Bafilistin, sai Shawulu da dukan Isra’ila suka damu suka kuma ji tsoro.
And Saul and all the Israelites hearing these words of the Philistine were dismayed, and greatly afraid.
12 To, Dawuda dai ɗan wani mutumin Efratawa ne mai suna Yesse, shi mutumin Betlehem ne a cikin Yahudiya. Yesse yana da yara maza takwas, a zamanin Shawulu kuwa, Yesse ya riga ya tsufa.
Now David was the son of that Ephrathite of Bethlehem Juda before mentioned, whose name was Isai, who had eight sons, and was an old man in the days of Saul, and of great age among men.
13 Manyan’ya’yansa maza uku, sun bi Shawulu wajen yaƙi. Ɗansa na fari shi ne Eliyab, na biyu shi ne Abinadab, na uku kuwa shi ne Shamma.
And his three eldest sons followed Saul to the battle: and the names of his three sons that went to the battle, were Eliab the firstborn, and the second Abinadab, and the third Samma.
14 Dawuda shi ne ɗan autansu. Manyan’yan mazan nan uku suka bi Shawulu.
But David was the youngest. So the three eldest having followed Saul,
15 Amma Dawuda yakan tafi sansanin Shawulu lokaci-lokaci yă kuma koma Betlehem don yă yi kiwon tumakin mahaifinsa.
David went, and returned from Saul, to feed his father’s flock at Bethlehem.
16 Kwana arba’in cif, Bafilistin nan ya yi ta fitowa kowane safe da kuma kowace yamma.
Now the Philistine came out morning and evening, and presented himself forty days.
17 Yesse ya ce wa ɗansa Dawuda, “Ka ɗauki wannan gasasshen hatsi da waɗannan curin burodi goma, ka kai wa’yan’uwanka a sansani da sauri.
And Isai said to David his son: Take for thy brethren an ephi of frumenty, and these ten loaves, and run to the camp to thy brethren.
18 Ka haɗa da waɗannan cuku guda goma, ka kai wa komandan rundunarsu. Ka ga lafiyar’yan’uwanka, ka kawo mini labari daga wurinsu.
And carry these ten little cheeses to the tribune: and go see thy brethren, if they are well: and learn with whom they are placed.
19 Suna tare da Shawulu da kuma dukan mutanen Isra’ila a Kwarin Ela, suna can suna yaƙi da Filistiyawa.”
But Saul, and they, and all the children of Israel were in the valley of Terebinth fighting against the Philistines.
20 Kashegari da sassafe, Dawuda ya tashi ya bar tumakinsa wa wani yă lura da su, sai ya ɗauki kayansa, ya kama hanya kamar yadda Yesse ya umarce shi. Ya isa sansanin daidai sa’ad da rundunar tana fitowa zuwa bakin dāgā, suna kirarin yaƙi.
David therefore arose in the morning, and gave the charge of the flock to the keeper: and went away loaded as Isai had commanded him. And he came to the place of Magala, and to the army, which was going out to fight, and shouted for the battle.
21 Isra’ila da Filistiyawa suka ja dāgā suna fuskantar junansu.
For Israel had put themselves in array, and the Philistines who stood against them were prepared.
22 Dawuda ya bar kayansa a wajen wani mai lura da kaya, sai ya ruga zuwa bakin dāgā yă gai da’yan’uwansa.
And David leaving the vessels which he had brought, under the care of the keeper of the baggage, ran to the place of the battle and asked if all things went well with his brethren.
23 Da yana magana da su sai Goliyat, jarumin nan Bafilistin daga Gat ya fito daga rundunar Filistiyawa, ya tā da murya kamar yadda ya saba. Dawuda kuwa ya ji shi.
And as he talked with them, that baseborn man whose name was Goliath, the Philistine, of Geth, shewed himself coming up from the camp of the Philistines: and he spoke according to the same words, and David heard them.
24 Da Isra’ilawa suka ga mutumin, sai dukansu suka gudu saboda tsananin tsoro.
And all the Israelites when they saw the man, fled from his face, fearing him exceedingly.
25 Isra’ilawa suka yi ta cewa, “Kun ga yadda wannan mutum yana ta fitowa? Yana fitowa ne don yă kalubalanci Isra’ila. Sarki zai sāka wa mutumin da ya kashe wannan da dukiya mai yawa. Zai kuma ba shi’yarsa yă aura, yă cire suna mahaifinsa daga biyan kuɗin haraji cikin Isra’ila.”
And some one of Israel said: Have you seen this man that is come up, for he is come up to defy Israel. And the man that shall slay him, the king will enrich with great riches, and will give him his daughter, and will make his father’s house free from tribute in Israel.
26 Dawuda ya tambayi mutanen da suke tsaye kusa da shi ya ce, “Me za a yi wa wanda ya kashe Bafilistin nan, ya kuma cire wannan kunya daga Isra’ila? Wane ne wannan bafilistin marar kaciya da yake kalubalantar rundunar yaƙi na Allah mai rai?”
And David spoke to the men that stood by him, saying: What shall be given to the man that shall kill this Philistine, and shall take away the reproach from Israel? for who is this uncircumcised Philistine, that he should defy the armies of the living God?
27 Sai suka sāke gaya masa abin da suka faɗa cewa, “Ga abin da zai faru da wanda ya kashe shi.”
And the people answered him the same words saying: These things shall be given to the man that shall slay him.
28 Da wansa Eliyab, ya ji yana magana da mutanen, sai ransa ya ɓace ƙwarai saboda fushi, sai ya ce wa Dawuda, “Me ka zo yi a nan? Wa kuma ka bar wa’yan tumakin a jeji? Na san ka da taurinkai, da kuma mugun hali. Ka zo nan ne don ka yi kallon yaƙi kawai.”
Now when Eliab his eldest brother heard this, when he was speaking with others, he was angry with David, and said: Why earnest thou hither? and why didst thou leave those few sheep in the desert? I know thy pride, and the wickedness of thy heart: that thou art come down to see the battle.
29 Dawuda ya ce, “To, yanzu me na yi? Ba zan ma yi magana ba?”
And David said: What have I done? is there not cause to speak?
30 Sai ya juya wajen wani kuma ya sāke kawo zancen, mutanen kuwa suka amsa masa kamar dā.
And he turned a little aside from him to another: and said the same word. And the people answered him as before.
31 Aka ji abin da Dawuda ya ce, aka kuwa gaya wa Shawulu, Shawulu kuma ya aika a kawo shi.
And the words which David spoke were heard, and were rehearsed before Saul.
32 Da Shawulu ya tambayi Dawuda, sai Dawuda ya ce masa, “Kada kowa yă damu saboda wannan Bafilistin. Bawanka zai je yă yi faɗa da shi.”
And when he was brought to him, he said to him: Let not any man’s heart be dismayed in him: I thy servant will go, and will fight against the Philistine.
33 Shawulu ya ce, “Ba za ka iya yin faɗa da wannan Bafilistin ba, ya daɗe yana yaƙi, ya yi yaƙi tun yana saurayi. Ga shi kuwa kai ɗan yaro ne kawai.”
And Saul said to David: Thou art not able to withstand this Philistine, nor to fight against him: for thou art but a boy, but he is a warrior from his youth.
34 Amma Dawuda ya ce wa Shawulu, “Bawanka yana kiwon tumakin mahaifinsa. Sa’ad da zaki ko beyar ta zo ta kama tunkiya, ta tafi da ita.
And David said to Saul: Thy servant kept his father’s sheep, and there came a lion, or a bear, and took a ram out of the midst of the flock:
35 Nakan bi ta a baya in buga ta in kuma ƙwato tunkiyar daga bakinta. In kuma ta taso mini, nakan cafke ta a gashinta in buga ta in kashe.
And I pursued after them, and struck them, and delivered it out of their mouth: and they rose up against me, and I caught them by the throat, and I strangled and killed them.
36 Bawanka ya kashe zaki da beyar, wannan Bafilistin marar kaciya zai zama kamar ɗaya daga cikinsu, domin ya rena rundunar Allah mai rai.
For I thy servant have killed both a lion and a bear: and this uncircumcised Philistine shall be also as one of them. I will go now, and take away the reproach of the people: for who is this uncircumcised Philistine, who hath dared to curse the army of the living God?
37 Ubangiji wanda ya cece ni daga kumbar zaki da kuma kumbar beyar, zai cece ni daga hannun wannan Bafilistin.” Shawulu ya ce wa Dawuda, “Je ka, Ubangiji yă kasance tare da kai.”
And David said: The Lord who delivered me out of the paw of the lion, and out of the paw of the bear, he will deliver me out of the hand of this Philistine. And Saul said to David: Go, and the Lord be with thee.
38 Sai Shawulu ya kawo kayan yaƙinsa ya sa wa Dawuda. Ya sa masa hular kwanon da aka yi da tagulla a kansa, ya kuma sa masa rigar ƙarfensa.
And Saul clothed David with his garments, and put a helmet of brass upon his head, and armed him with a coat of mail.
39 Dawuda ya ɗaura māshin Shawulu a sulken, ya yi ƙoƙari yă zaga, sai ya ji ba zai iya ba saboda bai saba ba. Ya cewa Shawulu, “Ba zan iya tafiya da waɗannan ba, domin ban saba ba.” Don haka ya tuɓe su.
And David having girded his sword upon his armour, began to try if he could walk in armour: for he was not accustomed to it. And David said to Saul: I cannot go thus, for I am not used to it. And he laid them off,
40 Sai ya ɗauki sandansa, ya zaɓi duwatsu guda biyar masu sulɓi daga cikin rafi, ya sa su a’yar jakarsa ta makiyaya; ya kuma ɗauki majajjawarsa, ya tafi, yă fuskanci Bafilistin.
And he took his staff, which he had always in his hands: and chose him five smooth stones out of the brook, and put them into the shepherd’s scrip, which he had with him, and he took a sling in his hand, and went forth against the Philistine.
41 Ana ciki haka, sai Bafilistin nan shi ma ya fita yana gusowa zuwa wurin Dawuda. Mai riƙe masa garkuwar yaƙi kuwa yana tafe a gabansa.
And the Philistine came on, and drew nigh against David, and his armourbearer before him.
42 Bafilistin ya dubi Dawuda daga sama har ƙasa, ya gan dai ɗan yaro ne kawai, kyakkyawa kuma mai ƙoshin lafiya, sai ya rena shi.
And when the Philistine looked, and beheld David, he despised him. For he was a young man, ruddy, and of a comely countenance.
43 Ya ce masa, “Kana tsammani ni kare ne da za ka zo mini da sanda?” Sai ya la’anci Dawuda da sunayen allolin Filistiyawa.
And the Philistine said to David: Am I a dog, that thou comest to me with a staff? And the Philistine cursed David by his gods.
44 Ya ce, “Zo nan, ni kuwa zan ba da naman jikinka ga tsuntsayen sama da namun jeji su ci.”
And he said to David: Come to me, and I will give thy flesh to the birds of the air, and to the beasts of the earth.
45 Dawuda ya ce wa Bafilistin, “Kana zuwa ka yaƙe ni da māshi da takobi da kere, amma ni ina zuwa in yaƙe ka a cikin sunan Ubangiji Maɗaukaki, Allah na rundunar Isra’ila, wanda ka rena.
And David said to the Philistine: Thou comest to me with a sword, and with a spear, and with a shield: but I come to thee in the name of the Lord of hosts, the God of the armies of Israel, which thou hast defied.
46 Yau nan, Ubangiji zai bashe ka a hannuna, zan kuwa kashe ka, in datse kanka. Yau, zan ba da gawawwakin rundunar Filistiyawa ga tsuntsayen sama da namun jeji, da haka duniya za tă sani lalle akwai Allah a cikin Isra’ila.
This day, and the Lord will deliver thee into my hand, and I will slay thee, and take away thy head from thee: and I will give the carcasses of the army of the Philistines this day to the birds of the air, and to the beasts of the earth: that all the earth may know that there is a God in Israel.
47 Duk waɗanda suka taru a nan za su san cewa ba da māshi ko takobi ne Ubangiji yake ceto ba, gama yaƙin nan na Ubangiji ne, shi kuwa zai bashe ku duka a hannuwanmu.”
And all this assembly shall know, that the Lord saveth not with sword and spear: for it is his battle, and he will deliver you into our hands.
48 Yayinda Bafilistin yana matsowa kusa domin yă fāɗa wa Dawuda, sai Dawuda ya ruga a guje zuwa bakin dāgā don yă same shi.
And when the Philistine arose and was coming, and drew nigh to meet David, David made haste, and ran to the fight to meet the Philistine.
49 Ya sa hannu a jakarsa ya ɗauki dutse, ya sa cikin majajjawa ya wurga, dutsen kuwa ya bugi Bafilistin a goshi, dutsen ya shiga cikin goshinsa, sai Bafilistin ya fāɗi rubda ciki.
And he put his hand into his scrip, and took a stone, and cast it with the sling, and fetching it about struck the Philistine in the forehead: and the stone was fixed in his forehead, and he fell on his face upon the earth.
50 Da majajjawa da dutse kawai Dawuda ya ci nasara a kan Bafilistin. Ya buge shi, ya kashe shi ba tare da takobi a hannunsa ba.
And David prevailed over the Philistine, with a sling and a stone, and he struck, and slew the Philistine. And as David had no sword in his hand,
51 Dawuda ya ruga ya tsaya a bisan Bafilistin, ya zare takobin Bafilistin daga kubensa, ya datse masa kai da shi. Da Filistiyawa suka ga jaruminsu ya mutu, sai suka juya suka gudu.
He ran, and stood over the Philistine, and took his sword, and drew it out of the sheath, and slew him, and cut off his head. And the Philistines seeing that their champion was dead, fled away.
52 Mutanen Isra’ila da na Yahuda suka rugo gaba da babbar murya, suka fafari Filistiyawa har zuwa mashigin Gat da kuma ƙofofin Ekron. Gawawwakin Filistiyawa suka bazu a hanyar Sha’arayim zuwa Gat da kuma Ekron.
And the men of Israel and Juda rising up shouted, and pursued after the Philistines till they came to the valley and to the gates of Accaron, and there fell many wounded of the Philistines in the way of Saraim, and as far as Geth, and as far as Accaron.
53 Da Isra’ilawa suka komo daga bin Filistiyawa sai suka washe sansanin Filistiyawa.
And the children of Israel returning, after they had pursued the Philistines, fell upon their camp.
54 Dawuda ya ɗauki kan Bafilistin zuwa Urushalima. Sai Dawuda ya ajiye kayan yaƙin Bafilistin a tentinsa.
And David taking the head of the Philistine brought it to Jerusalem: but his armour he put in his tent.
55 Yayinda Shawulu yake kallon Dawuda sa’ad da za shi yă yaƙi Bafilistin, sai ya tambayi Abner, komandan rundunarsa ya ce, “Abner, ɗan wane ne wannan saurayi?” Abner ya ce ran sarki yă daɗe, “Ban sani ba.”
Now at the time that Saul saw David going out against the Philistines, he said to Abner the captain of the army: Of what family is this young man descended, Abner? And Abner said: As thy soul liveth, O king, I know not.
56 Sarki ya ce, “Ka tambaya mini ko yaron wane ne wannan saurayi.”
And the king said: Inquire thou, whose son this man is.
57 Dawuda yana dawowa daga karkashe Filistiyawa ke nan, sai Abner ya kai shi gaban Shawulu, riƙe da kan Bafilistin.
And when David was returned, after the Philistine was slain, Abner took him, and brought him in before Saul, with the head of the Philistine in his hand.
58 Sai Shawulu ya ce, “Kai ɗan wane ne, saurayi?” Dawuda ya ce, “Ni ɗan bawanka Yesse ne, na Betlehem.”
And Saul said to him: Young man, of what family art thou? And David said: I am the son of thy servant Isai the Bethlehemite.

< 1 Sama’ila 17 >