< 1 Sama’ila 17 >

1 To, fa, Filistiyawa suka tattara mayaƙansu suka haɗu a Soko cikin Yahuda domin yaƙi. Suka yi sansani a Efes-Dammim, tsakanin Soko da Azeka.
Koro jo-Filistia nochoko jolweny mag-gi mondo gikedi kendo negichokore kama iluongo ni Soko e piny Juda. Negijot Efes-Damin man e kind Soko gi Azeka.
2 Shawulu da Isra’ilawa suka taru suka yi sansani a Kwarin Ela suka ja dāgā don su yi yaƙi da Filistiyawa.
Saulo gi jo-Israel to nochokore mine gibworo e Holo mar Ela kendo negichanore mondo girad gi jo-Filistia.
3 Filistiyawa suka zauna a tudu guda, Isra’ilawa kuma suka zauna a ɗaya tudun. Kwari yana a tsakaninsu.
Jo-Filistia ne ni ewi got moro to jo-Israel bende ne ni e got machielo to holo ne ni e kindgi.
4 Wani jarumin da ake kira Goliyat wanda ya fito daga Gat, ya fita daga sansanin Filistiyawa. Tsawonsa ya fi ƙafa tara.
Thuon ma nyinge Goliath, ma ja-Gath nowuok koa e kambi mar jo-Filistia. Borne ne en fut ochiko.
5 Ya sa hular kwanon da aka yi da tagulla, da rigar ƙarfe mai sulke, nauyin rigar ya kai shekel dubu biyar.
Nosidho ogut mula e wiye kendo norwako koti mar lweny mar mula ma pekne oromo kilo piero abich gi abiriyo,
6 A ƙafafunsa kuwa ya sa ƙarafar tagulla, rataye a bayansa kuma māshi ne na tagulla.
ogwendene to norwakoe mula mothedhi, kendo noliero tongʼ mar mula e ngʼeye.
7 Ƙotar kibiyarsa kuwa kamar sandar saƙar igiya take, ƙarfen kibiyar kuma nauyinsa ya kai shekel ɗari shida. Mai riƙe masa garkuwa yana tafe a gabansa.
Bond tongʼe ne chalo gi lodi, lew tonge to pekne ne romo kilo abiriyo. Jatingʼne okumba notelo nyime.
8 Goliyat ya tsaya ya tā da murya wa hafsoshin Isra’ila ya ce, “Me ya sa kuka fito kuna layi don yaƙi? Ni ba Bafilistin ba ne? Ku kuma ba bayin Shawulu ba ne? Ku zaɓi waninku yă zo nan.
Goliath nochungʼ mokok ne jolweny mag Israel niya, “Angʼo momiyo ubiro kendo uriedo ne lweny? Donge an ja-Filistia, to un, donge un jotich Saulo? Yieruru ngʼato mondo olor obi kama antieni.
9 In zai iya yin faɗa har yă kashe ni, to, za mu zama bayinku. Amma in na fi ƙarfinsa na kashe shi, to, sai ku zama bayinmu, ku kuma yi mana bauta.”
To konyalo kedo koda monega, to wabiro bedo jotiju, to ka ahinge mi anege, to ubiro bedo jotijwa ma tiyonwa.”
10 Sai Bafilistin ya ce, “A wannan rana, na kalubalanci sojojin Isra’ila, ku ba ni mutum ɗaya mu yi faɗa.”
Eka ja-Filistiano nowacho niya, “Kawuononi athiano ne jolweny mag Israel! Miyauru ngʼato mondo wakedgo.”
11 Da jin maganganun Bafilistin, sai Shawulu da dukan Isra’ila suka damu suka kuma ji tsoro.
Kane Saulo gi jo-Israel owinjo weche ja-Filistia, kibaji nogoyogi mi luoro nomakogi.
12 To, Dawuda dai ɗan wani mutumin Efratawa ne mai suna Yesse, shi mutumin Betlehem ne a cikin Yahudiya. Yesse yana da yara maza takwas, a zamanin Shawulu kuwa, Yesse ya riga ya tsufa.
Daudi ne en wuod ja-Efrath miluongo ni Jesse mane oa Bethlehem e piny Juda. Jesse ne nigi yawuowi aboro to e ndalo Saulo ne en ngʼat moti ma hike ngʼeny.
13 Manyan’ya’yansa maza uku, sun bi Shawulu wajen yaƙi. Ɗansa na fari shi ne Eliyab, na biyu shi ne Abinadab, na uku kuwa shi ne Shamma.
Yawuot Jesse adek madongo noluwo Saulo e lweny. Wuowi maduongʼ ne en Eliab, mar ariyo ne Abinadab, to mar adek ne en Shama.
14 Dawuda shi ne ɗan autansu. Manyan’yan mazan nan uku suka bi Shawulu.
Daudi ema ne wuowi matin kuomgi. Yawuowi adek madongo noluwo bangʼ Saulo,
15 Amma Dawuda yakan tafi sansanin Shawulu lokaci-lokaci yă kuma koma Betlehem don yă yi kiwon tumakin mahaifinsa.
to Daudi ne jadok kinde ka kinde koa ir Saulo mondo odhi okwa romb wuon-gi Bethlehem.
16 Kwana arba’in cif, Bafilistin nan ya yi ta fitowa kowane safe da kuma kowace yamma.
Kuom ndalo piero angʼwen ja-Filistiano ne wuok okinyi godhiambo konyisore.
17 Yesse ya ce wa ɗansa Dawuda, “Ka ɗauki wannan gasasshen hatsi da waɗannan curin burodi goma, ka kai wa’yan’uwanka a sansani da sauri.
Koro Jesse nowachone Daudi wuode niya, “Kaw atonga mopongʼ gi bando mobul kod makati apar mondo ireti iterne oweteni e kambigi.
18 Ka haɗa da waɗannan cuku guda goma, ka kai wa komandan rundunarsu. Ka ga lafiyar’yan’uwanka, ka kawo mini labari daga wurinsu.
Kaw bende chak mopoto mongʼin apar mondo itergi ne jatendgi. Nenane kaka oweteni dhi mondo iduogna wach maber moa kuomgi.
19 Suna tare da Shawulu da kuma dukan mutanen Isra’ila a Kwarin Ela, suna can suna yaƙi da Filistiyawa.”
Gin gi Saulo gi jo-Israel duto e holo mar Ela, ka gikedo gi jo-Filistia.”
20 Kashegari da sassafe, Dawuda ya tashi ya bar tumakinsa wa wani yă lura da su, sai ya ɗauki kayansa, ya kama hanya kamar yadda Yesse ya umarce shi. Ya isa sansanin daidai sa’ad da rundunar tana fitowa zuwa bakin dāgā, suna kirarin yaƙi.
Okinyi mangʼich Daudi noweyo rombe gi jokwath, notweyo misike mowuok odhi kaka Jesse nonyise. Nochopo e kambi ka jolweny wuok dhi e paw lweny, ka gigoyo koko kendo gigiyo sigich lweny.
21 Isra’ila da Filistiyawa suka ja dāgā suna fuskantar junansu.
Jo-Israel kod jo-Filistia nochanore koni gi kocha ka gimanyore.
22 Dawuda ya bar kayansa a wajen wani mai lura da kaya, sai ya ruga zuwa bakin dāgā yă gai da’yan’uwansa.
Daudi noweyo gigege gi jarit gik moko moringo odhi ir jolweny mi omoso owetene.
23 Da yana magana da su sai Goliyat, jarumin nan Bafilistin daga Gat ya fito daga rundunar Filistiyawa, ya tā da murya kamar yadda ya saba. Dawuda kuwa ya ji shi.
Kane pod owuoyo kodgi, Goliath mathuon jo-Filistia ma ja-Gath nowuok kuom jolweny kakok kawacho wechege mag ajara mapile kendo Daudi nowinje.
24 Da Isra’ilawa suka ga mutumin, sai dukansu suka gudu saboda tsananin tsoro.
Kane jo-Israel oneno ngʼatno, to giduto ne giringe ka giluor ahinya.
25 Isra’ilawa suka yi ta cewa, “Kun ga yadda wannan mutum yana ta fitowa? Yana fitowa ne don yă kalubalanci Isra’ila. Sarki zai sāka wa mutumin da ya kashe wannan da dukiya mai yawa. Zai kuma ba shi’yarsa yă aura, yă cire suna mahaifinsa daga biyan kuɗin haraji cikin Isra’ila.”
Koro noyudo ka jo-Israel osebedo kawacho niya, “Donge uneno kaka ngʼatni osiko wuok? Owuok, mana mar jaro, Israel. Ruoth biro chiwo mwandu mathoth ne ngʼat monege. Bende obiro miye nyare mondo okendi, joodgi bende ok nogol osuru e Israel.”
26 Dawuda ya tambayi mutanen da suke tsaye kusa da shi ya ce, “Me za a yi wa wanda ya kashe Bafilistin nan, ya kuma cire wannan kunya daga Isra’ila? Wane ne wannan bafilistin marar kaciya da yake kalubalantar rundunar yaƙi na Allah mai rai?”
Daudi nopenjo joma nochungʼ machiegni kode niya, “Ibiro tim angʼo ne ngʼat monego ja-Filistiani magol wichkuodni e Israel? Ja-Filistia ma ok oter nyangu to en ngʼa manyalo jaro jolweny mag Nyasaye mangima?”
27 Sai suka sāke gaya masa abin da suka faɗa cewa, “Ga abin da zai faru da wanda ya kashe shi.”
Neginwoyone weche mane oyudo giwacho mi giwachone niya, “Ma e gima ibiro timo ne ngʼat manonege.”
28 Da wansa Eliyab, ya ji yana magana da mutanen, sai ransa ya ɓace ƙwarai saboda fushi, sai ya ce wa Dawuda, “Me ka zo yi a nan? Wa kuma ka bar wa’yan tumakin a jeji? Na san ka da taurinkai, da kuma mugun hali. Ka zo nan ne don ka yi kallon yaƙi kawai.”
Kane Eliab mowadgi Daudi maduongʼ, owinje ka owuoyo gi ji, mirima nomake kode mopenje niya, “Ibiro ka nangʼo? To rombe manok ka to iweyo gi ngʼa e thim? Angʼeyo ni in jangʼayi bende pachi richo, isebiro mana ni mondo ine kaka lweny dhi.”
29 Dawuda ya ce, “To, yanzu me na yi? Ba zan ma yi magana ba?”
Daudi nowacho niya, “Koro sani to atimo angʼo? Ok anyal kata wuoyoe?”
30 Sai ya juya wajen wani kuma ya sāke kawo zancen, mutanen kuwa suka amsa masa kamar dā.
Eka nolokore mochako wuoyo gi ngʼama chielo konono mana wachno kendo ji nodwoke mana wach machalre gi manosewinjo.
31 Aka ji abin da Dawuda ya ce, aka kuwa gaya wa Shawulu, Shawulu kuma ya aika a kawo shi.
Gima Daudi nowacho nolandore mochopo ne Saulo eka Saulo noluonge.
32 Da Shawulu ya tambayi Dawuda, sai Dawuda ya ce masa, “Kada kowa yă damu saboda wannan Bafilistin. Bawanka zai je yă yi faɗa da shi.”
Daudi nowachone Saulo niya, “Kik chuny ji nyosre nikech ja-Filistiani; jatichni biro dhi mondo oked kode.”
33 Shawulu ya ce, “Ba za ka iya yin faɗa da wannan Bafilistin ba, ya daɗe yana yaƙi, ya yi yaƙi tun yana saurayi. Ga shi kuwa kai ɗan yaro ne kawai.”
Saulo nodwoko niya, “In ok inyal dhi kedo gi ja-Filistia nikech in mana rawera, to en to osebedo kokedo chakre tin-ne.”
34 Amma Dawuda ya ce wa Shawulu, “Bawanka yana kiwon tumakin mahaifinsa. Sa’ad da zaki ko beyar ta zo ta kama tunkiya, ta tafi da ita.
To Daudi nowacho ni Saulo niya, “Jatichni osebedo kakwayo romb wuon-gi. Ka sibuor kata ondiek omako achiel kuom rombwa,
35 Nakan bi ta a baya in buga ta in kuma ƙwato tunkiyar daga bakinta. In kuma ta taso mini, nakan cafke ta a gashinta in buga ta in kashe.
to ne alawe kendo agoye mi amaye rombo kagolo e dhoge. Kane ochikore ira, ne amake gi yie dende mi agoye kendo anege.
36 Bawanka ya kashe zaki da beyar, wannan Bafilistin marar kaciya zai zama kamar ɗaya daga cikinsu, domin ya rena rundunar Allah mai rai.
Jatichni osenego sibuor gi ondiek; ja-Filistia ma ok oter nyanguni, biro bedo achiel kuomgi nikech osejaro jolwenj Nyasaye mangima.
37 Ubangiji wanda ya cece ni daga kumbar zaki da kuma kumbar beyar, zai cece ni daga hannun wannan Bafilistin.” Shawulu ya ce wa Dawuda, “Je ka, Ubangiji yă kasance tare da kai.”
Jehova Nyasaye mane oresa e kok sibuor gi kok ondiek biro resa e lwet ja-Filistiani.” Saulo nowachone Daudi niya, “Dhi kendo Jehova Nyasaye obed kodi.”
38 Sai Shawulu ya kawo kayan yaƙinsa ya sa wa Dawuda. Ya sa masa hular kwanon da aka yi da tagulla a kansa, ya kuma sa masa rigar ƙarfensa.
Eka Saulo norwako Daudi gi lawe owuon. Norwakone koti mar lweny kendo nosidhone ogudu mar mula e wiye.
39 Dawuda ya ɗaura māshin Shawulu a sulken, ya yi ƙoƙari yă zaga, sai ya ji ba zai iya ba saboda bai saba ba. Ya cewa Shawulu, “Ba zan iya tafiya da waɗannan ba, domin ban saba ba.” Don haka ya tuɓe su.
Daudi notweyo liganglane ewi law mi notemo wuothogo nikech ne ok ongʼiyo gi gigo. Nowachone Saulo niya, “Ok anyal dhi gi gigi nikech ok angʼiyo kodgi.” Omiyo nogonyogi oko.
40 Sai ya ɗauki sandansa, ya zaɓi duwatsu guda biyar masu sulɓi daga cikin rafi, ya sa su a’yar jakarsa ta makiyaya; ya kuma ɗauki majajjawarsa, ya tafi, yă fuskanci Bafilistin.
Eka nokawo ludhe mi oyiero kite mapoth abich ei aora kendo noketogi e ofukune mar kwath mi otingʼo orujre e lwete kendo osudo machiegni gi ja-Filistiano.
41 Ana ciki haka, sai Bafilistin nan shi ma ya fita yana gusowa zuwa wurin Dawuda. Mai riƙe masa garkuwar yaƙi kuwa yana tafe a gabansa.
E kindeno, ja-Filistiano gi jatingʼ kuode, ne sudo machiegni gi Daudi.
42 Bafilistin ya dubi Dawuda daga sama har ƙasa, ya gan dai ɗan yaro ne kawai, kyakkyawa kuma mai ƙoshin lafiya, sai ya rena shi.
Eka norango Daudi konone moneno ni en mana rawera ma silwal, ma jaber, mine obuone.
43 Ya ce masa, “Kana tsammani ni kare ne da za ka zo mini da sanda?” Sai ya la’anci Dawuda da sunayen allolin Filistiyawa.
Nowachone Daudi niya, “An guok mibirona kitongʼona kete?” Ja-Filistia nokwongʼo Daudi gi nying nyisechene.
44 Ya ce, “Zo nan, ni kuwa zan ba da naman jikinka ga tsuntsayen sama da namun jeji su ci.”
Nowachone niya, “Bi ka abiro miyo winy ma e kor yamo ringi gi le man e thim.”
45 Dawuda ya ce wa Bafilistin, “Kana zuwa ka yaƙe ni da māshi da takobi da kere, amma ni ina zuwa in yaƙe ka a cikin sunan Ubangiji Maɗaukaki, Allah na rundunar Isra’ila, wanda ka rena.
Daudi nowachone ja-Filistiano niya, “Ibirona gi ligangla kod tongʼ gi bidhi, anto abironi e nying Jehova Nyasaye Maratego, ma Nyasach jolweny Israel ma iseyanyo.
46 Yau nan, Ubangiji zai bashe ka a hannuna, zan kuwa kashe ka, in datse kanka. Yau, zan ba da gawawwakin rundunar Filistiyawa ga tsuntsayen sama da namun jeji, da haka duniya za tă sani lalle akwai Allah a cikin Isra’ila.
Kawuononi Jehova Nyasaye biro keti e lweta, abiro goyi piny mi angʼad ngʼuti. Kawuono abiro miyo winy mae kor polo gi le man e thim ringre jolweny mag jo-Filistia, kendo piny mangima biro ngʼeyo ni nitie Nyasaye ei Israel.
47 Duk waɗanda suka taru a nan za su san cewa ba da māshi ko takobi ne Ubangiji yake ceto ba, gama yaƙin nan na Ubangiji ne, shi kuwa zai bashe ku duka a hannuwanmu.”
Ji duto mochokore ka biro ngʼeyo ni Jehova Nyasaye ok res joge gi ligangla gi tongʼ nimar lweny en mar Jehova Nyasaye, kendo obiro chiwou uduto e lwetwa.”
48 Yayinda Bafilistin yana matsowa kusa domin yă fāɗa wa Dawuda, sai Dawuda ya ruga a guje zuwa bakin dāgā don yă same shi.
Kane ja-Filistiano osudo machiegni mondo oked kode, Daudi ne oringo mapiyo piyo kochiko kar kedo mondo orom kode.
49 Ya sa hannu a jakarsa ya ɗauki dutse, ya sa cikin majajjawa ya wurga, dutsen kuwa ya bugi Bafilistin a goshi, dutsen ya shiga cikin goshinsa, sai Bafilistin ya fāɗi rubda ciki.
Nosoyo lwete ei mifukune mogolo kidi; eka noketo kidino e orujre mine odiro mogoyogo lend wangʼ ja-Filistiano. Kidi nodonjo e lend wangʼe mine opodho piny auma.
50 Da majajjawa da dutse kawai Dawuda ya ci nasara a kan Bafilistin. Ya buge shi, ya kashe shi ba tare da takobi a hannunsa ba.
Omiyo Daudi noloyo ja-Filistiano gi orujre kod kidi; ka oonge gi ligangla e lwete nogoyo ja-Filistiano piny monege.
51 Dawuda ya ruga ya tsaya a bisan Bafilistin, ya zare takobin Bafilistin daga kubensa, ya datse masa kai da shi. Da Filistiyawa suka ga jaruminsu ya mutu, sai suka juya suka gudu.
Daudi noringo mochungʼ kuome. Nokawo ligangla ja-Filistia mowuodho e olalone kane osenege, nongʼado wiye gi ligangla. Kane jo-Filistia oneno ni thuon-gi osetho negilokore mi gichako ngʼwech.
52 Mutanen Isra’ila da na Yahuda suka rugo gaba da babbar murya, suka fafari Filistiyawa har zuwa mashigin Gat da kuma ƙofofin Ekron. Gawawwakin Filistiyawa suka bazu a hanyar Sha’arayim zuwa Gat da kuma Ekron.
Eka jo-Israel gi jo-Juda nosudo machiegni negigiyo sigich lweny mi gilawo jo-Filistia nyaka gichopi kama idonjogo Gath nyaka rangeye mag Ekron. Ringre jogi motho nokeyore e yo madhi Sharaim nyaka Gath gi Ekron.
53 Da Isra’ilawa suka komo daga bin Filistiyawa sai suka washe sansanin Filistiyawa.
Kane jo-Israel odwogo koa lawo jo-Filistia, ne giyako kargi mar bworo.
54 Dawuda ya ɗauki kan Bafilistin zuwa Urushalima. Sai Dawuda ya ajiye kayan yaƙin Bafilistin a tentinsa.
Daudi nokawo wi ja-Filistia mokelo Jerusalem, to gige lweny mag ja-Filistia notero e hembe owuon.
55 Yayinda Shawulu yake kallon Dawuda sa’ad da za shi yă yaƙi Bafilistin, sai ya tambayi Abner, komandan rundunarsa ya ce, “Abner, ɗan wane ne wannan saurayi?” Abner ya ce ran sarki yă daɗe, “Ban sani ba.”
Kane Saulo orango Daudi e sa mane odhi rado gi ja-Filistia, nopenjo Abner mane jatend jolweny niya, “Abner wuowini en wuod ngʼa?” Abner nodwoko niya “Yaye ruoth, akwongʼora e nyimi ni ok angʼeye.”
56 Sarki ya ce, “Ka tambaya mini ko yaron wane ne wannan saurayi.”
Ruoth nowachone niya, “Non ane ni wuowini en wuod ngʼa?”
57 Dawuda yana dawowa daga karkashe Filistiyawa ke nan, sai Abner ya kai shi gaban Shawulu, riƙe da kan Bafilistin.
Mapiyo piyo kane Daudi odwogo koa nego ja-Filistia, Abner nokawe motere e nyim Saulo, kapod Daudi otingʼo wi ja-Filistia.
58 Sai Shawulu ya ce, “Kai ɗan wane ne, saurayi?” Dawuda ya ce, “Ni ɗan bawanka Yesse ne, na Betlehem.”
Saulo nopenje niya, “Wuowi matin in wuod ngʼa?” Daudi nodwoko niya, “An wuod Jesse ma ja-Bethlehem ma jatichni.”

< 1 Sama’ila 17 >