< 1 Sama’ila 16 >

1 Ubangiji ya ce wa Sama’ila, “Har yaushe za ka yi ta makoki saboda Shawulu? Na riga na ƙi shi da zaman sarkin Isra’ila. Ka cika ƙahonka da mai, zan aike ka zuwa wurin Yesse na Betlehem. Na zaɓi ɗaya daga cikin’ya’yansa maza yă zama sarki.”
Rəbbee Şamuelik'le eyhen: – Ğu geebne Şaulna haa'as, geedne uts'ur ts'ıts'a'as? Zı mang'usse İzrailyna paççahiyvalla g'avşuna. Gaç q'ışika gyavts'av'u, yəqqı'lqa gixhe. Zı ğu Bet-Lexemğançene Yesseyne k'anyaqa g'ıxele. Zı mang'une dixbışike Yizdemee paççah g'əyxı'.
2 Amma Sama’ila ya ce, “Yaya zan yi haka? Ai, in Shawulu ya ji labari, zai kashe ni.” Ubangiji ya ce, “To, sai ka tafi tare da’yar karsana ka ce, ‘Na zo don in yi wa Ubangiji hadaya.’
Şamuelee eyhen: – Zı nəxürna ı'qqəs? Şauluk'le g'ayxhee, zı gik'asda. Rəbbee eyhen: – Vaka sa vuç'e vukkee, «Rəbbis q'urban ablyaa'as arıva» eyhe.
3 Ka gayyato Yesse a wurin hadayar, ni kuma zan gaya maka abin da za ka yi. Za ka shafe mini wanda na nuna maka.”
Yesseyir q'urban ablyaa'asde cigeeqa qot'le, qiyğa hucooyiy ha'as ıkkanva Zı vak'le eyhesın. Zı eyhene insanne vuk'lelqa ğu q'ış qadğvas, mang'uke Yizdemee paççah ha'as.
4 Sama’ila kuwa ya yi abin da Ubangiji ya umarce shi. Da ya isa Betlehem, sai dattawan garin suka tarye shi da rawar jiki, suka ce masa, “Mai duba, wannan ziyara lafiya dai ko?”
Şamuelee Rəbbee eyhəxüd ha'a. Mana Bet-Lexemqa qarımee, şaharın ağsaqqalar mang'une ögilqa qəvəyq'ən-qəvəyq'ən qığeepç'ı, eyhen: – Ğu yugvalisne arı?
5 Sama’ila ya ce, “I, lafiya ƙalau. Na zo ne domin in yi wa Ubangiji hadaya. Ku tsarkake kanku sa’an nan ku zo mu tafi wurin yin hadaya tare.” Ya kuma sa Yesse da’ya’yansa maza su tsarkake kansu, su je wurin hadayar.
Mang'vee eyhen: – Ho'o, yugvalis arı. Zı Rəbbis q'urban ablyaa'as arı. Mətteepxha, zakasana q'urban ablyaa'ane cigeeqa able. Şamuelee Yesseyik'leyiy mang'une dixbışik'led mətteepxha q'urban ablyaa'asde cigeeqa ableva eyhe.
6 Da isarsu, Sama’ila ya ga Eliyab sai ya yi tsammani shi ne, sai ya ce, “Lalle ga shafaffe na Ubangiji tsaye a gaban Ubangiji.”
Manbı vüqqəmee, Şamuel Eliavıqa ilyakkı culed-alqa eyhen: «İna Rəbbee paççah ixhes g'əyxı'na vor!»
7 Amma Ubangiji ya ce wa Sama’ila, “Kada ka dubi kyan tsarinsa ko tsayinsa, domin ba shi nake so ba, gama yadda Ubangiji yake gani, ba haka mutum yake gani ba. Mutum yakan dubi kyan tsari ne kawai daga waje, amma Ubangiji yakan dubi zuciya.”
Rəbbeemee Şamuelik'le inəxüd eyhe: – Mang'une micagiyvaliqayiy axtıvaliqa ilymakka, Zı mana əq'əna qı'ı. Rəbb, insan ilyakkan xhinne deş ilyakka. İnsan insanne aq'vayqa, tanaqa ilyakka, Rəbbmee insanne yik'eeqa ilyakka.
8 Sai Yesse ya kira Abinadab yă zo gaban Sama’ila. Amma Sama’ila ya ce, “Ko wannan ma Ubangiji bai zaɓe shi ba.”
Mane gahıl Yesseyee Avinadav qort'ul, mana Şamuelyne ögiyle alğayhe. Şamuelee eyhen: – Rəbbee inar g'əyxı' deş.
9 Sai Yesse ya sa Shamma yă zo gaban Sama’ila, amma Sama’ila ya ce, “Ubangiji bai zaɓi wannan ma ba.”
Manke Yesseyee Şamma qort'ul, mana alğayhe Şamuelyne ögeençe. Şamuelee eyhen: – Rəbbee inar g'əyxı' deş.
10 Yesse ya sa’ya’yansa maza bakwai suka wuce gaban Sama’ila, amma Sama’ila ya ce masa, “Ubangiji bai zaɓi waɗannan ba.”
Yesseyee dixbışda yighırsana qort'ul, manbı Şamuelyne ögiyle alğaa'a. Şamuelee Yesseyk'le eyhen: – Rəbbee inbı g'əvxü deş.
11 Don haka ya tambayi Yesse ya ce, “Su ke nan’ya’yan maza da kake da su?” Yesse ya ce, “Har yanzu akwai ɗan autan, amma yana kiwon tumaki.” Sama’ila ya ce, “Ka aika yă zo, ba za mu zauna ba sai ya iso.”
Şamuelee Yesseyke qiyghanan: – İnbı yiğne dixbışin gırgınbıne? Yesseyee eyhen: – Nekke k'ınnar vorna, mang'vee vəq'əbı uxhiyxhan. Şamuelee Yesseyk'le eyhen: – Mang'uqar qihna insan g'axıle, hasre manar inyaqa qoracen. Mana inyaqa qalesmee, şi sufranılqa savaales deş.
12 Sai ya aika aka kawo shi. Ga shi kuwa kyakkyawan saurayi ne mai kyan gani. Ubangiji ya ce, “Tashi ka shafe shi, shi ne wannan.”
Yesseyee mang'uqar qihna insan g'axuvu mana qalya'ana. Mang'uqa ç'ərəxən xhinnen danbı, micagın uleppı, uftanınıd aq'va eyxhe. Rəbbee Şamuelik'le eyhen: – Oza qixhe, mang'ulqa q'ış qadğve, Zı eyhena mana vor.
13 Saboda haka Sama’ila ya ɗauko ƙahon nan da yake da mai ya shafe Dawuda a gaban’yan’uwansa. Daga wannan rana kuwa ruhun Ubangiji ya sauko wa Dawuda da iko. Sai Sama’ila ya koma Rama.
Şamuelee q'ışnana gaç alyapt'ı, çocaaşine k'ane Davudulqa q'ış qadağva. Manke Rəbbin Rı'h Davudulqa g'eç'e, mane yiğıled mang'ul oğa axva. Şamuel mançe Ramayeeqa siyk'al.
14 To, fa, Ruhun Ubangiji ya riga ya rabu da Shawulu, sai mugun ruhu daga Ubangiji ya soma ba shi wahala.
Rəbbin Rı'h Şaulule atk'ınmee, Rəbbee mang'ulqa sa medın pisın rı'h g'ıxele ıxha. Mançinıb Şaulus əq'üba hoole vuxha.
15 Ma’aikatan Shawulu suka ce masa, “Duba, ga mugun ruhu daga Allah yana ba ka wahala.
Şaulne insanaaşe mang'uk'le eyhen: – Allahee g'axuvuyne pisde rı'hı'n həşde vas əq'üba hoole.
16 Ranka yă daɗe, muna so ka ba mu izini mu tafi, mu nemo wanda ya iya kiɗan molo, domin duk sa’ad da mugun ruhun nan daga Allah ya tashi, sai yă kaɗa molon don hankalinka yă kwanta.”
Yişda xərna, yiğne insanaaşilqa əmr hee'e, vas yugba lira əlivxəs vəəxəna insan t'abal he'ecen. Allahee g'axuvuyn pisın rı'h valqa qadımee, mang'vee lira əlivxee, vasıd yugda ixhes.
17 Saboda haka Shawulu ya ce wa ma’aikatansa, “Ku nemo wanda ya iya kiɗan molo sosai ku kawo mini.”
Şaulee cune insanaaşik'le eyhen: – Manke yizdemee sa yugba lira ilyviyxəna insan t'abal hı'ı zasqa ayre.
18 Ɗaya daga cikin bayin ya ce, “Na san wani yaro, ɗan Yesse na Betlehem, ya iya kiɗan molo, yana da hikima, shi kuma ya iya yaƙi. Ya iya magana, ga shi kuma kyakkyawa, Ubangiji kuwa yana tare da shi.”
Mang'une insanaaşine sang'vee alidghıniy qele: – Zak'le Bet-Lexemğançene Yesseyne dixbışde sang'vee yugba lira ilyviyxə g'avcuna. Mana cehil, yik'ekana, yugra siç'ekkvana, k'orara yuşan ha'ana, micagna gadeyiy. Rəbbir mang'ukayiy.
19 Sai Shawulu ya aiki manzanni zuwa wurin Yesse ya ce, “Ka aiko mini da ɗanka Dawuda wanda yake kiwon tumaki.”
Şaulee, Yesseysqa xabar ana insanar g'axuvu, eyhen: – Vəq'əbı uxhiyxhan ha'ana yiğna dix, Davud, zasqa g'axıle.
20 Saboda haka Yesse ya ɗauki jaki tare da burodi da ruwan inabi da ɗan ƙarami bunsuru ya ba wa ɗansa Dawuda yă kai wa Shawulu.
Yesseyee əməlelqa gıney, çaxıren tuluğ, mısva alivxhu, cune duxayka Davuduka Şaulus g'uxoole.
21 Dawuda ya isa wurin Shawulu ya shiga hidimarsa. Shawulu kuwa ya so shi ƙwarai da gaske. Dawuda ya zama ɗaya daga cikin masu sanya sulke.
Davud Şaulusqa qarı, mang'une ögil ulyoyzar. Şaulus Davud geer ikkiykan, mang'uke cuna silahdar ha'a.
22 Sa’an nan Shawulu ya aika saƙo wurin Yesse cewa, “Ka bar Dawuda yă yi mini hidima domin ina jin daɗinsa ƙwarai.”
Qiyğa Şaulee, Yesseysqa cuna insan g'axuvu, eyhen: – Hucoona ixhes, hasre Davud yizde k'ane axvecen, mana zasqa yugra qarı.
23 Duk lokacin da ruhun nan daga Allah ya sauko a kan Shawulu, sai Dawuda yă ɗauki molonsa yă kaɗa. Sa’an nan sauƙi yă zo wa Shawulu, mugun ruhu kuma yă rabu da shi.
Allahee g'axuvuyn pisın rı'h Şaululqa qadıyne gahbışil, Davudee cuna lira alyapt'ı əlivxümee, mana yug qexhe ıxha. Pisın rı'hı'd mang'uke əq'əna qexhe ıxha.

< 1 Sama’ila 16 >