< 1 Sama’ila 16 >

1 Ubangiji ya ce wa Sama’ila, “Har yaushe za ka yi ta makoki saboda Shawulu? Na riga na ƙi shi da zaman sarkin Isra’ila. Ka cika ƙahonka da mai, zan aike ka zuwa wurin Yesse na Betlehem. Na zaɓi ɗaya daga cikin’ya’yansa maza yă zama sarki.”
سرانجام خداوند به سموئیل فرمود: «بیش از این برای شائول عزا نگیر، چون من او را از سلطنت اسرائیل برکنار کرده‌ام. حال، یک ظرف روغن زیتون بردار و به خانهٔ یَسای بیت‌لحمی برو، زیرا یکی از پسران او را برگزیده‌ام تا پادشاه اسرائیل باشد.»
2 Amma Sama’ila ya ce, “Yaya zan yi haka? Ai, in Shawulu ya ji labari, zai kashe ni.” Ubangiji ya ce, “To, sai ka tafi tare da’yar karsana ka ce, ‘Na zo don in yi wa Ubangiji hadaya.’
ولی سموئیل پرسید: «چطور می‌توانم این کار را بکنم؟ اگر شائول بشنود مرا می‌کشد!» خداوند پاسخ داد: «گوساله‌ای ماده با خود ببر و بگو آمده‌ای تا برای خداوند قربانی کنی.
3 Ka gayyato Yesse a wurin hadayar, ni kuma zan gaya maka abin da za ka yi. Za ka shafe mini wanda na nuna maka.”
بعد یَسا را به مذبح دعوت کن، آنگاه به تو نشان خواهم داد که کدام یک از پسرانش را باید برای پادشاهی تدهین کنی.»
4 Sama’ila kuwa ya yi abin da Ubangiji ya umarce shi. Da ya isa Betlehem, sai dattawan garin suka tarye shi da rawar jiki, suka ce masa, “Mai duba, wannan ziyara lafiya dai ko?”
سموئیل طبق دستور خداوند عمل کرد. وقتی به بیت‌لحم رسید، بزرگان شهر با ترس و لرز به استقبالش آمدند و پرسیدند: «چه اتفاقی افتاده است؟»
5 Sama’ila ya ce, “I, lafiya ƙalau. Na zo ne domin in yi wa Ubangiji hadaya. Ku tsarkake kanku sa’an nan ku zo mu tafi wurin yin hadaya tare.” Ya kuma sa Yesse da’ya’yansa maza su tsarkake kansu, su je wurin hadayar.
سموئیل جواب داد: «نترسید، هیچ اتفاق بدی نیفتاده است. آمده‌ام تا برای خداوند قربانی کنم. خود را تقدیس کنید و همراه من برای قربانی کردن بیایید.» او یَسا و پسرانش را تقدیس کرد و آنها را به قربانی دعوت نمود.
6 Da isarsu, Sama’ila ya ga Eliyab sai ya yi tsammani shi ne, sai ya ce, “Lalle ga shafaffe na Ubangiji tsaye a gaban Ubangiji.”
وقتی پسران یَسا آمدند، سموئیل چشمش به الیاب افتاد و فکر کرد او همان کسی است که خداوند برگزیده است.
7 Amma Ubangiji ya ce wa Sama’ila, “Kada ka dubi kyan tsarinsa ko tsayinsa, domin ba shi nake so ba, gama yadda Ubangiji yake gani, ba haka mutum yake gani ba. Mutum yakan dubi kyan tsari ne kawai daga waje, amma Ubangiji yakan dubi zuciya.”
اما خداوند به سموئیل فرمود: «به چهرهٔ او و بلندی قدش نگاه نکن، زیرا او آن کسی نیست که من در نظر گرفته‌ام. من مثل انسان قضاوت نمی‌کنم. انسان به ظاهر نگاه می‌کند، اما من به دل.»
8 Sai Yesse ya kira Abinadab yă zo gaban Sama’ila. Amma Sama’ila ya ce, “Ko wannan ma Ubangiji bai zaɓe shi ba.”
پس یَسا ابیناداب را نزد سموئیل خواند. خداوند فرمود: «او نیز شخص مورد نظر نیست.»
9 Sai Yesse ya sa Shamma yă zo gaban Sama’ila, amma Sama’ila ya ce, “Ubangiji bai zaɓi wannan ma ba.”
بعد یَسا شمعا را احضار نمود، اما خداوند فرمود: «این هم آنکه من می‌خواهم نیست.»
10 Yesse ya sa’ya’yansa maza bakwai suka wuce gaban Sama’ila, amma Sama’ila ya ce masa, “Ubangiji bai zaɓi waɗannan ba.”
به همین ترتیب یَسا هفت پسرش را احضار نمود و همه رد شدند. سموئیل به یَسا گفت: «خداوند هیچ‌یک از اینها را برنگزیده است. آیا تمام پسرانت اینها هستند؟» یَسا پاسخ داد: «یکی دیگر هم دارم که از همه کوچکتر است. اما او در صحرا مشغول چرانیدن گوسفندان است.» سموئیل گفت: «فوری کسی را بفرست تا او را بیاورد چون تا او نیاید ما سر سفره نخواهیم نشست.»
11 Don haka ya tambayi Yesse ya ce, “Su ke nan’ya’yan maza da kake da su?” Yesse ya ce, “Har yanzu akwai ɗan autan, amma yana kiwon tumaki.” Sama’ila ya ce, “Ka aika yă zo, ba za mu zauna ba sai ya iso.”
12 Sai ya aika aka kawo shi. Ga shi kuwa kyakkyawan saurayi ne mai kyan gani. Ubangiji ya ce, “Tashi ka shafe shi, shi ne wannan.”
پس یَسا فرستاد و او را آوردند. او پسری شاداب و خوش‌قیافه بود و چشمانی زیبا داشت. خداوند فرمود: «این همان کسی است که من برگزیده‌ام. او را تدهین کن.»
13 Saboda haka Sama’ila ya ɗauko ƙahon nan da yake da mai ya shafe Dawuda a gaban’yan’uwansa. Daga wannan rana kuwa ruhun Ubangiji ya sauko wa Dawuda da iko. Sai Sama’ila ya koma Rama.
سموئیل ظرف روغن زیتون را که با خود آورده بود برداشت و بر سر داوود که در میان برادرانش ایستاده بود، ریخت. روح خداوند بر او نازل شد و از آن روز به بعد بر او قرار داشت. سپس سموئیل به خانهٔ خود در رامه بازگشت.
14 To, fa, Ruhun Ubangiji ya riga ya rabu da Shawulu, sai mugun ruhu daga Ubangiji ya soma ba shi wahala.
روح خداوند از شائول دور شد و به جای آن روح پلید از جانب خداوند او را سخت عذاب می‌داد.
15 Ma’aikatan Shawulu suka ce masa, “Duba, ga mugun ruhu daga Allah yana ba ka wahala.
بعضی از افراد شائول به او گفتند: «اگر اجازه دهی، نوازنده‌ای که در نواختن چنگ ماهر باشد پیدا کنیم تا هر وقت روح پلید تو را آزار می‌دهد، برایت چنگ بنوازد و تو را آرامش دهد.»
16 Ranka yă daɗe, muna so ka ba mu izini mu tafi, mu nemo wanda ya iya kiɗan molo, domin duk sa’ad da mugun ruhun nan daga Allah ya tashi, sai yă kaɗa molon don hankalinka yă kwanta.”
17 Saboda haka Shawulu ya ce wa ma’aikatansa, “Ku nemo wanda ya iya kiɗan molo sosai ku kawo mini.”
شائول گفت: «بسیار خوب، نوازندهٔ ماهری پیدا کنید و نزد من بیاورید.»
18 Ɗaya daga cikin bayin ya ce, “Na san wani yaro, ɗan Yesse na Betlehem, ya iya kiɗan molo, yana da hikima, shi kuma ya iya yaƙi. Ya iya magana, ga shi kuma kyakkyawa, Ubangiji kuwa yana tare da shi.”
یکی از افرادش گفت: «پسر یَسای بیت‌لحمی خیلی خوب می‌نوازد. در ضمن جوانی است شجاع و جنگاور. او خوش‌بیان و خوش‌قیافه است، و خداوند با او می‌باشد.»
19 Sai Shawulu ya aiki manzanni zuwa wurin Yesse ya ce, “Ka aiko mini da ɗanka Dawuda wanda yake kiwon tumaki.”
شائول قاصدانی به خانهٔ یَسا فرستاد تا داوود چوپان را نزد وی ببرند.
20 Saboda haka Yesse ya ɗauki jaki tare da burodi da ruwan inabi da ɗan ƙarami bunsuru ya ba wa ɗansa Dawuda yă kai wa Shawulu.
یَسا الاغی را با نان و مشکی شراب و یک بزغاله بار کرد و همه را همراه داوود نزد شائول فرستاد.
21 Dawuda ya isa wurin Shawulu ya shiga hidimarsa. Shawulu kuwa ya so shi ƙwarai da gaske. Dawuda ya zama ɗaya daga cikin masu sanya sulke.
شائول وقتی چشمش به داوود افتاد از او خوشش آمد و داوود سلاحدار شائول شد.
22 Sa’an nan Shawulu ya aika saƙo wurin Yesse cewa, “Ka bar Dawuda yă yi mini hidima domin ina jin daɗinsa ƙwarai.”
پس شائول برای یَسا پیغام فرستاده، گفت: «بگذار داوود پیش من بماند، چون از او خوشم آمده است.»
23 Duk lokacin da ruhun nan daga Allah ya sauko a kan Shawulu, sai Dawuda yă ɗauki molonsa yă kaɗa. Sa’an nan sauƙi yă zo wa Shawulu, mugun ruhu kuma yă rabu da shi.
هر وقت آن روح پلید از جانب خدا شائول را آزار می‌داد، داوود برایش چنگ می‌نواخت و روح بد از او دور می‌شد و او احساس آرامش می‌کرد.

< 1 Sama’ila 16 >