< 1 Sama’ila 16 >

1 Ubangiji ya ce wa Sama’ila, “Har yaushe za ka yi ta makoki saboda Shawulu? Na riga na ƙi shi da zaman sarkin Isra’ila. Ka cika ƙahonka da mai, zan aike ka zuwa wurin Yesse na Betlehem. Na zaɓi ɗaya daga cikin’ya’yansa maza yă zama sarki.”
Herren sa til Samuel: Hvor lenge vil du sørge over Saul, enda jeg har forkastet ham, så han ikke skal være konge over Israel? Fyll ditt horn med olje og gå avsted! Jeg sender dig til betlehemitten Isai, for blandt hans sønner har jeg utsett mig en til konge.
2 Amma Sama’ila ya ce, “Yaya zan yi haka? Ai, in Shawulu ya ji labari, zai kashe ni.” Ubangiji ya ce, “To, sai ka tafi tare da’yar karsana ka ce, ‘Na zo don in yi wa Ubangiji hadaya.’
Men Samuel sa: Hvorledes kan jeg gjøre slik en ferd? Får Saul høre det, slår han mig ihjel. Da sa Herren: Ta med dig en kalv av buskapen og si: Jeg er kommet for å ofre til Herren.
3 Ka gayyato Yesse a wurin hadayar, ni kuma zan gaya maka abin da za ka yi. Za ka shafe mini wanda na nuna maka.”
Og innbyd Isai til ofringen, så vil jeg la dig få vite hvad du skal gjøre, og du skal salve for mig den jeg sier dig.
4 Sama’ila kuwa ya yi abin da Ubangiji ya umarce shi. Da ya isa Betlehem, sai dattawan garin suka tarye shi da rawar jiki, suka ce masa, “Mai duba, wannan ziyara lafiya dai ko?”
Samuel gjorde som Herren sa. Da han kom til Betlehem, gikk byens eldste ham skjelvende i møte og sa: Kommer du med fred?
5 Sama’ila ya ce, “I, lafiya ƙalau. Na zo ne domin in yi wa Ubangiji hadaya. Ku tsarkake kanku sa’an nan ku zo mu tafi wurin yin hadaya tare.” Ya kuma sa Yesse da’ya’yansa maza su tsarkake kansu, su je wurin hadayar.
Han svarte: Ja, jeg kommer med fred; jeg er kommet for å ofre til Herren; hellige eder og kom med mig til ofringen! Og han lot Isai og hans sønner hellige sig og innbød dem til ofringen.
6 Da isarsu, Sama’ila ya ga Eliyab sai ya yi tsammani shi ne, sai ya ce, “Lalle ga shafaffe na Ubangiji tsaye a gaban Ubangiji.”
Da de kom, og han fikk se Eliab, tenkte han: Visselig står her for Herren hans salvede.
7 Amma Ubangiji ya ce wa Sama’ila, “Kada ka dubi kyan tsarinsa ko tsayinsa, domin ba shi nake so ba, gama yadda Ubangiji yake gani, ba haka mutum yake gani ba. Mutum yakan dubi kyan tsari ne kawai daga waje, amma Ubangiji yakan dubi zuciya.”
Men Herren sa til Samuel: Se ikke på hans utseende og på hans høie vekst! For jeg har forkastet ham; jeg ser ikke på hvad mennesket ser på, for mennesket ser på det utvortes, men Herren ser på hjertet.
8 Sai Yesse ya kira Abinadab yă zo gaban Sama’ila. Amma Sama’ila ya ce, “Ko wannan ma Ubangiji bai zaɓe shi ba.”
Så kalte Isai på Abinadab og lot ham gå frem for Samuel; men han sa: Heller ikke ham har Herren utvalgt.
9 Sai Yesse ya sa Shamma yă zo gaban Sama’ila, amma Sama’ila ya ce, “Ubangiji bai zaɓi wannan ma ba.”
Så lot Isai Samma gå frem; men han sa: Heller ikke ham har Herren utvalgt.
10 Yesse ya sa’ya’yansa maza bakwai suka wuce gaban Sama’ila, amma Sama’ila ya ce masa, “Ubangiji bai zaɓi waɗannan ba.”
Således lot Isai syv sønner gå frem for Samuel; men Samuel sa til Isai: Herren har ikke utvalgt nogen av disse.
11 Don haka ya tambayi Yesse ya ce, “Su ke nan’ya’yan maza da kake da su?” Yesse ya ce, “Har yanzu akwai ɗan autan, amma yana kiwon tumaki.” Sama’ila ya ce, “Ka aika yă zo, ba za mu zauna ba sai ya iso.”
Og Samuel sa til Isai: Var dette alle de gutter du har? Han svarte: Ennu er den yngste tilbake; han vokter småfeet. Da sa Samuel til Isai: Send bud efter ham! Vi setter oss ikke til bords før han kommer.
12 Sai ya aika aka kawo shi. Ga shi kuwa kyakkyawan saurayi ne mai kyan gani. Ubangiji ya ce, “Tashi ka shafe shi, shi ne wannan.”
Så sendte han bud efter ham. Han var rødkinnet og hadde vakre øine og var fager av utseende. Da sa Herren: Stå op og salv ham! For han er det.
13 Saboda haka Sama’ila ya ɗauko ƙahon nan da yake da mai ya shafe Dawuda a gaban’yan’uwansa. Daga wannan rana kuwa ruhun Ubangiji ya sauko wa Dawuda da iko. Sai Sama’ila ya koma Rama.
Da tok Samuel oljehornet og salvet ham midt iblandt hans brødre, og Herrens Ånd kom over David fra den dag og fremdeles. Så brøt Samuel op og gikk til Rama.
14 To, fa, Ruhun Ubangiji ya riga ya rabu da Shawulu, sai mugun ruhu daga Ubangiji ya soma ba shi wahala.
Men Herrens Ånd vek fra Saul, og en ond ånd fra Herren forferdet ham.
15 Ma’aikatan Shawulu suka ce masa, “Duba, ga mugun ruhu daga Allah yana ba ka wahala.
Da sa Sauls tjenere til ham: Vi ser at en ond ånd fra Gud forferder dig.
16 Ranka yă daɗe, muna so ka ba mu izini mu tafi, mu nemo wanda ya iya kiɗan molo, domin duk sa’ad da mugun ruhun nan daga Allah ya tashi, sai yă kaɗa molon don hankalinka yă kwanta.”
Herre, byd bare dine tjenere som står for ditt ansikt, å opsøke en mann som er kyndig i å spille på harpe. Når da en ond ånd fra Gud kommer over dig, skal han spille på sin harpe; da vil det bli bedre med dig.
17 Saboda haka Shawulu ya ce wa ma’aikatansa, “Ku nemo wanda ya iya kiɗan molo sosai ku kawo mini.”
Da sa Saul til sine tjenere: Ja, finn mig en mann som spiller godt, og før ham hit til mig!
18 Ɗaya daga cikin bayin ya ce, “Na san wani yaro, ɗan Yesse na Betlehem, ya iya kiɗan molo, yana da hikima, shi kuma ya iya yaƙi. Ya iya magana, ga shi kuma kyakkyawa, Ubangiji kuwa yana tare da shi.”
En av de unge menn svarte og sa: Jeg har sett en sønn av betlehemitten Isai som er kyndig i å spille, en djerv mann og en stridsmann, god til å tale for sig og en vakker mann, og Herren er med ham.
19 Sai Shawulu ya aiki manzanni zuwa wurin Yesse ya ce, “Ka aiko mini da ɗanka Dawuda wanda yake kiwon tumaki.”
Da sendte Saul bud til Isai og lot si: Send hit til mig din sønn David, han som er med småfeet!
20 Saboda haka Yesse ya ɗauki jaki tare da burodi da ruwan inabi da ɗan ƙarami bunsuru ya ba wa ɗansa Dawuda yă kai wa Shawulu.
Så tok Isai et asen, som han lesste brød på, og en skinnsekk med vin og et kje og sendte det med sin sønn David til Saul.
21 Dawuda ya isa wurin Shawulu ya shiga hidimarsa. Shawulu kuwa ya so shi ƙwarai da gaske. Dawuda ya zama ɗaya daga cikin masu sanya sulke.
Således kom David til Saul, og han blev i hans tjeneste; og Saul fikk ham meget kjær, og han blev hans våbensvenn.
22 Sa’an nan Shawulu ya aika saƙo wurin Yesse cewa, “Ka bar Dawuda yă yi mini hidima domin ina jin daɗinsa ƙwarai.”
Og Saul sendte bud til Isai og lot si: Kjære, la David bli i min tjeneste! For han har funnet nåde for mine øine.
23 Duk lokacin da ruhun nan daga Allah ya sauko a kan Shawulu, sai Dawuda yă ɗauki molonsa yă kaɗa. Sa’an nan sauƙi yă zo wa Shawulu, mugun ruhu kuma yă rabu da shi.
Når da den onde ånd fra Gud kom over Saul, tok David harpen og spilte på den, og Saul fikk lindring, og det blev bedre med ham, og den onde ånd vek fra ham.

< 1 Sama’ila 16 >