< 1 Sama’ila 15 >

1 Sama’ila ya ce wa Shawulu, “Ni ne wanda Ubangiji ya aika in shafe ka ka zama sarki bisa mutanensa Isra’ila. Saurara yanzu ka ji saƙo daga wurin Ubangiji.
Et Samuel dit à Saül: Le Seigneur m’a envoyé pour vous oindre comme roi sur son peuple, Israël: maintenant donc écoutez la voix du Seigneur.
2 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Zan hori Amalekawa saboda abin da suka yi wa Isra’ila sa’ad da suka ba su wahala yayinda suka fito daga Masar.
Voici ce que dit le Seigneur des armées: J’ai passé en revue tout ce qu’a fait Amalec à Israël, comment il lui résista dans le chemin, lorsqu’il montait de l’Égypte.
3 Yanzu ka tafi ka yaƙi Amalekawa, ka hallaka kome da yake nasu, kada ka bar su da rai, ka kashe maza, da mata, da yara, da jarirai, da dabbobi, da tumaki, da raƙuma, da kuma jakuna.’”
Maintenant donc va et bats Amalec et détruis tout ce qui est à lui: ne l’épargne point, et ne désire rien de ce qui lui appartient; mais tue depuis l’homme jusqu’à la femme, jusqu’au petit enfant, et celui qui est à la mamelle, jusqu’au bœuf, à la brebis, au chameau et à l’âne.
4 Sai Shawulu ya tattara sojoji, ya ƙidaya su a Telayim, ya sami su dubu ɗari biyu da dubu goma daga Yahuda.
C’est pourquoi Saül ordonna au peuple, et il les recensa comme des agneaux; et il y eut deux cent mille hommes de pied et dix mille de la tribu de Juda.
5 Shawulu ya tafi birnin Amalek ya yi kwanto a kwari.
Et quand Saül fut venu jusqu’à la ville d’Amalec, il dressa des embuscades sur le bord du torrent.
6 Sai Shawulu ya ce wa Keniyawa, “Ku tashi ku bar Amalekawa don kada in hallaka ku tare da su, saboda kun yi wa dukan Isra’ilawa kirki, lokacin da suka fito daga Masar.” Saboda haka Keniyawa suka tashi suka bar Amalekawa.
Et Saül dit au Cinéen: Allez, retirez-vous, et descendez loin d’Amalec, de peur que je ne t’enveloppe avec lui; car tu as fait miséricorde à tous les enfants d’Israël, lorsqu’ils montaient de l’Égypte. Et le Cinéen se retira du milieu d’Amalec.
7 Sa’an nan Shawulu ya ci Amalekawa da yaƙi tun daga Hawila har zuwa Shur, a gabashin iyakar Masar.
Et Saül battit Amalec depuis Hévila jusqu’à ce qu’on vienne à Sur, qui est vis-à-vis de l’Égypte.
8 Ya kama Agag sarkin Amalekawa da rai. Ya kuma hallaka dukan mutanensa da takobi.
Et il prit Agag, roi d’Amalec, vivant; mais tout le peuple, il le tua par le tranchant du glaive.
9 Amma Shawulu da sojojinsa suka bar Agag, da tumaki, da shanu, da’yan maruƙa masu ƙiba da kuma duk abin da yake mai kyau da rai. Waɗannan ba su so su hallaka su gaba ɗaya ba, amma duk abin da ba a so da kuma marar amfani suka hallaka.
Et Saül et le peuple épargnèrent Agag, les meilleurs troupeaux de brebis et de bœufs, les vêtements, les béliers et tout ce qui était beau, et ils ne voulurent pas les détruire; mais tout ce qui était vil et méprisable, voilà ce qu’ils détruisirent.
10 Sai Ubangiji ya yi magana da Sama’ila ya ce,
Or, la parole du Seigneur se fit entendre à Samuel, disant:
11 “Na damu da na naɗa Shawulu sarki, domin ya juya mini baya, bai kuma bi umarnina ba.” Sama’ila ya damu ƙwarai, ya yi kuka ga Ubangiji dukan dare.
Je me repens d’avoir établi Saül roi, parce qu’il m’a abandonné, et qu’il n’a pas accompli mes paroles par ses œuvres. Et Samuel fut contristé, et il cria vers le Seigneur pendant toute la nuit.
12 Kashegari da sassafe sai Sama’ila ya tashi ya tafi domin yă sadu da Shawulu, amma aka gaya masa cewa Shawulu ya tafi Karmel. A can ya yi wa kansa abin tunawa don yă girmama kansa, daga can kuma ya juya ya gangara zuwa Gilgal.
Et lorsque Samuel se fut levé de nuit pour aller vers Saül au matin, on annonça à Samuel que Saül était venu sur le Carmel, qu’il s’était érigé un arc de triomphe, et que, retournant, il était passé et descendu à Galgala. Samuel vint donc vers Saül, et Saül offrait un holocauste au Seigneur des prémices des dépouilles qu’il avait emportées d’Amalec.
13 Da Sama’ila ya kai wurinsa, sai Shawulu ya ce, “Ubangiji yă albarkace ka, na aikata umarnin Ubangiji.”
Et quand Samuel fut venu vers Saül, Saül lui dit: Béni soyez-vous du Seigneur! J’ai accompli la parole du Seigneur,
14 Amma Sama’ila ya ce, “Ashe, waɗannan ba kukan tumaki ke nan nake ji a kunnena ba? Wane kuka shanu ke nan nake ji?”
Et Samuel demanda: Quelle est cette voix de brebis, qui retentit à mes oreilles, et de bœufs, que j’entends?
15 Shawulu ya amsa ya ce, “Sojoji ne suka kawo su daga Amalekawa. Sun bar tumaki da shanu masu kyau da rai don su yi wa Ubangiji Allahnka hadaya, amma sauran mun hallaka duka.”
Et Saül répondit: On les a amenés d’Amalec; car le peuple a épargné les meilleures brebis et les meilleurs bœufs, pour qu’ils fussent immolés au Seigneur votre Dieu; mais le reste nous l’avons tué.
16 Sama’ila ya ce, “Dakata, bari in faɗa maka abin da Ubangiji ya ce mini jiya da dare.” Shawulu ya ce, “Gaya mini.”
Mais Samuel dit à Saül: Laissez-moi, et je vous déclarerai ce que le Seigneur m’a dit pendant cette nuit. Et il lui répondit: Parlez.
17 Sama’ila ya ce, “Ko da yake kana ganin kanka kai ba wani abu ne ba, ashe, ba kai ne yanzu shugaban kabilan Isra’ila ba? Ubangiji ya shafe ka ka zama sarkin Isra’ila.
Et Samuel dit: Est-ce que, quand vous étiez petit à vos yeux, vous n’êtes pas devenu chef parmi les tribus d’Israël? Le Seigneur vous a même oint comme roi sur Israël;
18 Shi kuma ya aika, ya umarce ka cewa, ‘Tafi ka hallaka Amalekawa mugayen mutanen nan duka, ka yaƙe su sai ka share su ƙaf.’
De plus, il vous a lancé dans la voie, et il a dit: Va, et tue les pécheurs d’Amalec, et tu combattras contre eux jusqu’à leur entière extermination.
19 Me ya sa ba ka bi umarnin Ubangiji ba? Me ya sa ka sa hannu a ganima, ka kuma yi mugun abu a gaban Ubangiji?”
Pourquoi donc n’avez-vous pas écouté la voix du Seigneur; mais, que vous étant tourné du côté du butin, vous avez fait le mal sous les yeux du Seigneur?
20 Shawulu ya ce, “Amma na bi umarnin Ubangiji. Na bi saƙon da Ubangiji ya ba ni. Na hallaka Amalekawa, na kuma kamo Agag sarkinsu.
Et Saül répondit à Samuel: Au contraire, j’ai écouté la voix du Seigneur, et j’ai marché dans la voie dans laquelle m’a lancé le Seigneur, et j’ai amené Agag, roi d’Amalec, et j’ai tué Amalec.
21 Sojoji suka kawo tumaki da shanu mafi kyau daga cikin ganimar domin a miƙa hadaya ga Ubangiji Allahnka a Gilgal.”
Mais le peuple a pris dans le butin des brebis et des bœufs, prémices de ceux qui ont été taillés en pièces, pour les immoler au Seigneur son Dieu à Galgala.
22 Amma Sama’ila ya ce, “Ubangiji yana murna da sadaka da hadaya fiye da biyayya ga maganar Ubangiji? Yin biyayya ta fi hadaya a kula kuma ta fi ƙibabbun raguna.
Et Samuel repartit: Est-ce que le Seigneur veut des holocaustes et des victimes, et non pas plutôt qu’on obéisse à la voix du Seigneur? Car l’obéissance est (meilleure) que des victimes, et écouter vaut mieux qu’offrir de la graisse de béliers.
23 Gama tawaye yana kama da zunubi na duba, girman kai kuma yana kama da bautar gumaka. Saboda ka ƙi maganar Ubangiji, shi ma ya ƙi ka da zaman sarki.”
Car c’est comme un péché de magie que de résister, et comme un crime d’idolâtrie, que de ne vouloir pas se rendre. Parce donc que vous avez rejeté la parole du Seigneur, le Seigneur vous a rejeté, afin que vous ne soyez plus roi.
24 Sai Shawulu ya ce wa Sama’ila, “Na yi zunubi, na ƙi bin umarnin Ubangiji, na kuma ƙi bin maganarka. Na ji tsoron mutane ne shi ya sa na bi maganarsu.
Et Saül répondit à Samuel: J’ai péché, parce que j’ai prévariqué contre la parole du Seigneur et vos paroles, craignant le peuple et obéissant à sa voix.
25 Yanzu fa, ina roƙonka ka yafe mini zunubina, ka koma tare da ni, domin in yi wa Ubangiji sujada.”
Mais maintenant portez, je vous prie, mon péché, et retournez avec moi, afin que j’adore le Seigneur.
26 Amma Sama’ila ya ce, “Ba zan koma tare da kai ba. Ka ƙi maganar Ubangiji, Ubangiji kuma ya ƙi ka da zama sarki a bisa Isra’ila.”
Et Samuel répliqua à Saül: Je ne retournerai pas avec vous, parce que vous avez rejeté la parole du Seigneur, et que le Seigneur vous a rejeté, afin que vous ne soyez plus roi sur Israël.
27 Da Sama’ila ya juya zai tafi, sai Shawulu ya kama bakin rigarsa, sai rigar ta yage.
Et Samuel se tourna pour s’en aller, mais Saül saisit le coin de son manteau, qui se déchira,
28 Sama’ila ya ce masa, “Ubangiji ya yage masarautar Isra’ila daga gare ka yau, ya ba wa wani daga cikin maƙwabtanka wanda ya fi ka.
Et Samuel lui dit: Le Seigneur a déchiré le royaume d’Israël, en vous l’ôtant aujourd’hui, et il l’a livré à votre prochain, meilleur que vous.
29 Shi wanda yake Ɗaukakar Isra’ila ba ya ƙarya ko yă canja zuciyarsa, gama shi ba mutum ba ne da zai canja zuciyarsa.”
Or, le Triomphateur en Israël n’épargnera point, et il ne sera pas touché de repentir; car ce n’est pas un homme pour qu’il se repente.
30 Shawulu ya ce, “Na yi zunubi. Amma ina roƙonka ka ba ni girma a gaban dattawan mutanena da kuma a gaban Isra’ila, ka koma tare da ni domin in yi wa Ubangiji Allahnka sujada.”
Mais Saül reprit: J’ai péché; mais honorez-moi maintenant devant les anciens de mon peuple et devant Israël et retournez avec moi, afin que j’adore le Seigneur votre Dieu.
31 Saboda haka sai Sama’ila ya koma tare da Shawulu, Shawulu kuwa ya yi wa Ubangiji sujada.
Samuel donc, retournant, suivit Saül; et Saül adora le Seigneur.
32 Sa’an nan Sama’ila ya ce, “Kawo mini Agag sarkin Amalekawa.” Agag kuwa ya zo wurinsa daure da sarƙa, yana tunani cewa, “Tabbatacce zancen mutuwa dai ya wuce.”
Alors Samuel dit: Amenez-moi Agag, roi d’Amalec. Et on lui présenta Agag, fort gras et tremblant. Et Agag dit: Est-ce ainsi que la mort amère sépare?
33 Amma Sama’ila ya ce, “Yadda takobinka ya sa mata suka rasa’ya’ya, haka mahaifiyarka za tă zama marar’ya’ya a cikin mata.” Sama’ila kuwa ya kashe Agag a Gilgal a gaban Ubangiji.
Et Samuel répondit: Comme ton glaive a privé des femmes de leurs enfants, ainsi ta mère sera sans enfants parmi les femmes. Et Samuel le coupa en morceaux devant le Seigneur à Galgala.
34 Sai Sama’ila ya tafi Rama, amma Shawulu ya haura zuwa gidansa a Gibeya na Shawulu.
Or, Samuel s’en alla à Ramatha; mais Saül monta en sa maison à Gabaa.
35 Daga wannan rana Sama’ila bai ƙara saduwa da sarki Shawulu ba, har rasuwar Sama’ila, amma ya yi baƙin ciki sosai a kan Shawulu. Ubangiji kuwa ya damu da ya sa Shawulu ya zama Sarkin Isra’ila ba.
Et Samuel ne vit plus Saül jusqu’au jour de sa mort; cependant Samuel pleurait Saül, parce que le Seigneur se repentait de l’avoir établi roi sur Israël

< 1 Sama’ila 15 >