< 1 Sama’ila 15 >
1 Sama’ila ya ce wa Shawulu, “Ni ne wanda Ubangiji ya aika in shafe ka ka zama sarki bisa mutanensa Isra’ila. Saurara yanzu ka ji saƙo daga wurin Ubangiji.
Or, Samuel dit à Saül: C'est moi que l'Éternel a envoyé pour t'oindre roi sur son peuple, sur Israël; maintenant donc, écoute les paroles de l'Éternel.
2 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Zan hori Amalekawa saboda abin da suka yi wa Isra’ila sa’ad da suka ba su wahala yayinda suka fito daga Masar.
Ainsi a dit l'Éternel des armées: J'ai rappelé à ma mémoire ce qu'a fait Amalek à Israël, comment il s'opposa à lui sur le chemin, quand il montait d'Égypte.
3 Yanzu ka tafi ka yaƙi Amalekawa, ka hallaka kome da yake nasu, kada ka bar su da rai, ka kashe maza, da mata, da yara, da jarirai, da dabbobi, da tumaki, da raƙuma, da kuma jakuna.’”
Maintenant va, et frappe Amalek, et vouez à l'interdit tout ce qu'il a; et ne l'épargne point, mais fais mourir et les hommes et les femmes, et les jeunes enfants et ceux qui tètent, et les bœufs et les brebis, et les chameaux et les ânes.
4 Sai Shawulu ya tattara sojoji, ya ƙidaya su a Telayim, ya sami su dubu ɗari biyu da dubu goma daga Yahuda.
Saül convoqua donc le peuple, et en fit la revue à Télaïm, au nombre de deux cent mille hommes de pied, et dix mille hommes de Juda.
5 Shawulu ya tafi birnin Amalek ya yi kwanto a kwari.
Et Saül vint jusqu'à la ville d'Amalek, et mit une embuscade dans la vallée.
6 Sai Shawulu ya ce wa Keniyawa, “Ku tashi ku bar Amalekawa don kada in hallaka ku tare da su, saboda kun yi wa dukan Isra’ilawa kirki, lokacin da suka fito daga Masar.” Saboda haka Keniyawa suka tashi suka bar Amalekawa.
Et Saül dit aux Kéniens: Allez, retirez-vous, descendez du milieu des Amalécites, de peur que je ne vous enveloppe avec eux; car vous usâtes d'humanité envers tous les enfants d'Israël, quand ils montèrent hors d'Égypte. Et les Kéniens se retirèrent du milieu des Amalécites.
7 Sa’an nan Shawulu ya ci Amalekawa da yaƙi tun daga Hawila har zuwa Shur, a gabashin iyakar Masar.
Or, Saül battit Amalek depuis Havila jusqu'à Shur, qui est vis-à-vis de l'Égypte;
8 Ya kama Agag sarkin Amalekawa da rai. Ya kuma hallaka dukan mutanensa da takobi.
Et il prit vivant Agag, roi d'Amalek; et il fit passer tout le peuple au fil de l'épée, le vouant à l'interdit.
9 Amma Shawulu da sojojinsa suka bar Agag, da tumaki, da shanu, da’yan maruƙa masu ƙiba da kuma duk abin da yake mai kyau da rai. Waɗannan ba su so su hallaka su gaba ɗaya ba, amma duk abin da ba a so da kuma marar amfani suka hallaka.
Mais Saül et le peuple épargnèrent Agag et les meilleures brebis, les meilleurs bœufs, les bêtes de seconde qualité, les agneaux, et tout ce qu'il y avait de bon, et ne voulurent point les vouer à l'interdit; ils vouèrent seulement à l'interdit tout ce qui était méprisable et chétif.
10 Sai Ubangiji ya yi magana da Sama’ila ya ce,
Alors la parole de l'Éternel fut adressée à Samuel, en disant:
11 “Na damu da na naɗa Shawulu sarki, domin ya juya mini baya, bai kuma bi umarnina ba.” Sama’ila ya damu ƙwarai, ya yi kuka ga Ubangiji dukan dare.
Je me repens d'avoir établi Saül pour roi; car il s'est détourné de moi, et n'a point exécuté mes paroles. Et Samuel en fut fort affligé, et cria à l'Éternel toute la nuit.
12 Kashegari da sassafe sai Sama’ila ya tashi ya tafi domin yă sadu da Shawulu, amma aka gaya masa cewa Shawulu ya tafi Karmel. A can ya yi wa kansa abin tunawa don yă girmama kansa, daga can kuma ya juya ya gangara zuwa Gilgal.
Puis Samuel se leva de bon matin pour aller au-devant de Saül; et l'on fit ce rapport à Samuel, et on lui dit: Saül est venu à Carmel, et voici, il s'est fait élever un monument; puis il s'en est retourné, et, passant outre, il est descendu à Guilgal.
13 Da Sama’ila ya kai wurinsa, sai Shawulu ya ce, “Ubangiji yă albarkace ka, na aikata umarnin Ubangiji.”
Quand Samuel fut venu vers Saül, Saül lui dit: Sois béni de l'Éternel! j'ai exécuté la parole de l'Éternel.
14 Amma Sama’ila ya ce, “Ashe, waɗannan ba kukan tumaki ke nan nake ji a kunnena ba? Wane kuka shanu ke nan nake ji?”
Et Samuel dit: Quel est donc ce bêlement de brebis qui retentit à mes oreilles, et ce meuglement de bœufs que j'entends?
15 Shawulu ya amsa ya ce, “Sojoji ne suka kawo su daga Amalekawa. Sun bar tumaki da shanu masu kyau da rai don su yi wa Ubangiji Allahnka hadaya, amma sauran mun hallaka duka.”
Et Saül répondit: Ils les ont amenés des Amalécites; car le peuple a épargné les meilleures brebis, et les meilleurs bœufs, pour les sacrifier à l'Éternel, ton Dieu, et nous avons voué le reste à l'interdit.
16 Sama’ila ya ce, “Dakata, bari in faɗa maka abin da Ubangiji ya ce mini jiya da dare.” Shawulu ya ce, “Gaya mini.”
Et Samuel dit à Saül: Laisse-moi te déclarer ce que l'Éternel m'a dit cette nuit. Et il lui répondit: Parle.
17 Sama’ila ya ce, “Ko da yake kana ganin kanka kai ba wani abu ne ba, ashe, ba kai ne yanzu shugaban kabilan Isra’ila ba? Ubangiji ya shafe ka ka zama sarkin Isra’ila.
Et Samuel dit: N'est-il pas vrai que lorsque tu étais petit à tes yeux, tu devins chef des tribus d'Israël, et que l'Éternel t'a oint pour être roi sur Israël?
18 Shi kuma ya aika, ya umarce ka cewa, ‘Tafi ka hallaka Amalekawa mugayen mutanen nan duka, ka yaƙe su sai ka share su ƙaf.’
Or, l'Éternel t'avait envoyé en expédition, et t'avait dit: Va, et voue à l'interdit ces pécheurs, les Amalécites, et fais-leur la guerre jusqu'à ce que tu les aies consumés.
19 Me ya sa ba ka bi umarnin Ubangiji ba? Me ya sa ka sa hannu a ganima, ka kuma yi mugun abu a gaban Ubangiji?”
Pourquoi n'as-tu pas obéi à la voix de l'Éternel, et pourquoi t'es-tu jeté sur le butin, et as-tu fait ce qui déplaît à l'Éternel?
20 Shawulu ya ce, “Amma na bi umarnin Ubangiji. Na bi saƙon da Ubangiji ya ba ni. Na hallaka Amalekawa, na kuma kamo Agag sarkinsu.
Et Saül répondit à Samuel: J'ai pourtant obéi à la voix de l'Éternel, et je suis allé par le chemin par lequel l'Éternel m'a envoyé; j'ai amené Agag, roi d'Amalek, et j'ai voué à l'interdit les Amalécites.
21 Sojoji suka kawo tumaki da shanu mafi kyau daga cikin ganimar domin a miƙa hadaya ga Ubangiji Allahnka a Gilgal.”
Mais le peuple a pris sur le butin des brebis et des bœufs, comme prémices de l'interdit, pour sacrifier à l'Éternel, ton Dieu, à Guilgal.
22 Amma Sama’ila ya ce, “Ubangiji yana murna da sadaka da hadaya fiye da biyayya ga maganar Ubangiji? Yin biyayya ta fi hadaya a kula kuma ta fi ƙibabbun raguna.
Alors Samuel dit: L'Éternel prend-il plaisir aux holocaustes et aux sacrifices, comme à ce qu'on obéisse à la voix de l'Éternel? Voici, obéir vaut mieux que sacrifice; être attentif vaut mieux que la graisse des moutons;
23 Gama tawaye yana kama da zunubi na duba, girman kai kuma yana kama da bautar gumaka. Saboda ka ƙi maganar Ubangiji, shi ma ya ƙi ka da zaman sarki.”
Car la rébellion est autant que le péché de divination, et la résistance autant que les idoles et les théraphim. Parce que tu as rejeté la parole de l'Éternel, il t'a aussi rejeté, pour n'être plus roi.
24 Sai Shawulu ya ce wa Sama’ila, “Na yi zunubi, na ƙi bin umarnin Ubangiji, na kuma ƙi bin maganarka. Na ji tsoron mutane ne shi ya sa na bi maganarsu.
Alors Saül répondit à Samuel: J'ai péché; car j'ai transgressé le commandement de l'Éternel et tes paroles, parce que je craignais le peuple, et j'ai obéi à sa voix.
25 Yanzu fa, ina roƙonka ka yafe mini zunubina, ka koma tare da ni, domin in yi wa Ubangiji sujada.”
Mais maintenant, je te prie, pardonne mon péché, et reviens avec moi, et je me prosternerai devant l'Éternel.
26 Amma Sama’ila ya ce, “Ba zan koma tare da kai ba. Ka ƙi maganar Ubangiji, Ubangiji kuma ya ƙi ka da zama sarki a bisa Isra’ila.”
Et Samuel dit à Saül: Je ne retournerai point avec toi; car tu as rejeté la parole de l'Éternel, et l'Éternel t'a rejeté, pour n'être plus roi d'Israël.
27 Da Sama’ila ya juya zai tafi, sai Shawulu ya kama bakin rigarsa, sai rigar ta yage.
Et comme Samuel se tournait pour s'en aller, Saül saisit le pan de son manteau, qui se déchira.
28 Sama’ila ya ce masa, “Ubangiji ya yage masarautar Isra’ila daga gare ka yau, ya ba wa wani daga cikin maƙwabtanka wanda ya fi ka.
Alors Samuel lui dit: L'Éternel a aujourd'hui déchiré le royaume d'Israël de dessus toi, et il l'a donné à ton prochain, qui est meilleur que toi.
29 Shi wanda yake Ɗaukakar Isra’ila ba ya ƙarya ko yă canja zuciyarsa, gama shi ba mutum ba ne da zai canja zuciyarsa.”
Et même, celui qui est la force d'Israël ne mentira point, et ne se repentira point; car il n'est pas un homme pour se repentir.
30 Shawulu ya ce, “Na yi zunubi. Amma ina roƙonka ka ba ni girma a gaban dattawan mutanena da kuma a gaban Isra’ila, ka koma tare da ni domin in yi wa Ubangiji Allahnka sujada.”
Et Saül répondit: J'ai péché; maintenant honore-moi, je te prie, en présence des anciens de mon peuple, et en présence d'Israël; et reviens avec moi, et je me prosternerai devant l'Éternel ton Dieu.
31 Saboda haka sai Sama’ila ya koma tare da Shawulu, Shawulu kuwa ya yi wa Ubangiji sujada.
Samuel retourna donc, et suivit Saül; et Saül se prosterna devant l'Éternel.
32 Sa’an nan Sama’ila ya ce, “Kawo mini Agag sarkin Amalekawa.” Agag kuwa ya zo wurinsa daure da sarƙa, yana tunani cewa, “Tabbatacce zancen mutuwa dai ya wuce.”
Puis Samuel dit: Amenez-moi Agag, roi d'Amalek. Et Agag vint à lui gaiement. Et Agag disait: Certainement l'amertume de la mort est passée.
33 Amma Sama’ila ya ce, “Yadda takobinka ya sa mata suka rasa’ya’ya, haka mahaifiyarka za tă zama marar’ya’ya a cikin mata.” Sama’ila kuwa ya kashe Agag a Gilgal a gaban Ubangiji.
Mais Samuel dit: Comme ton épée a privé des femmes de leurs enfants, ainsi ta mère, entre les femmes, sera privée d'un fils. Et Samuel mit Agag en pièces, devant l'Éternel, à Guilgal.
34 Sai Sama’ila ya tafi Rama, amma Shawulu ya haura zuwa gidansa a Gibeya na Shawulu.
Puis Samuel s'en alla à Rama; et Saül monta en sa maison, à Guibea de Saül.
35 Daga wannan rana Sama’ila bai ƙara saduwa da sarki Shawulu ba, har rasuwar Sama’ila, amma ya yi baƙin ciki sosai a kan Shawulu. Ubangiji kuwa ya damu da ya sa Shawulu ya zama Sarkin Isra’ila ba.
Et Samuel n'alla plus voir Saül, jusqu'au jour de sa mort; car Samuel pleurait sur Saül, parce que l'Éternel se repentait d'avoir établi Saül roi sur Israël.