< 1 Sama’ila 15 >

1 Sama’ila ya ce wa Shawulu, “Ni ne wanda Ubangiji ya aika in shafe ka ka zama sarki bisa mutanensa Isra’ila. Saurara yanzu ka ji saƙo daga wurin Ubangiji.
Or Samuel dit à Saül: L'Eternel m'a envoyé pour t'oindre afin que tu sois Roi sur mon peuple, sur Israël; maintenant donc écoute les paroles de l'Eternel.
2 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Zan hori Amalekawa saboda abin da suka yi wa Isra’ila sa’ad da suka ba su wahala yayinda suka fito daga Masar.
Ainsi a dit l'Eternel des armées: J'ai rappelé en ma mémoire ce qu'Hamalec a fait à Israël, [et] comment il s'opposa à lui sur le chemin, quand il montait d'Egypte.
3 Yanzu ka tafi ka yaƙi Amalekawa, ka hallaka kome da yake nasu, kada ka bar su da rai, ka kashe maza, da mata, da yara, da jarirai, da dabbobi, da tumaki, da raƙuma, da kuma jakuna.’”
Va maintenant, et frappe Hamalec, et détruisez à la façon de l'interdit tout ce qu'il a, et ne l'épargne point; mais fais mourir tant les hommes que les femmes; tant les grands que ceux qui tètent, tant les bœufs que le menu bétail, tant les chameaux que les ânes.
4 Sai Shawulu ya tattara sojoji, ya ƙidaya su a Telayim, ya sami su dubu ɗari biyu da dubu goma daga Yahuda.
Saül donc assembla le peuple à cri public, et en fit le dénombrement à Télaïm, qui fut de deux cent mille hommes de pied, et de dix mille hommes de Juda.
5 Shawulu ya tafi birnin Amalek ya yi kwanto a kwari.
Et Saül vint jusqu'à la ville de Hamalec, et mit des embuscades en la vallée.
6 Sai Shawulu ya ce wa Keniyawa, “Ku tashi ku bar Amalekawa don kada in hallaka ku tare da su, saboda kun yi wa dukan Isra’ilawa kirki, lokacin da suka fito daga Masar.” Saboda haka Keniyawa suka tashi suka bar Amalekawa.
Et Saül dit aux Kéniens: Allez retirez-vous, descendez du milieu des Hamalécites, de peur que je ne vous enveloppe avec eux; car vous usâtes de gratuité envers tous les enfants d'Israël, quand ils montèrent d'Egypte. Et les Kéniens se retirèrent d'entre les Hamalécites.
7 Sa’an nan Shawulu ya ci Amalekawa da yaƙi tun daga Hawila har zuwa Shur, a gabashin iyakar Masar.
Et Saül frappa les Hamalécites depuis Havila jusqu'en Sur, qui est vis-à-vis d'Egypte.
8 Ya kama Agag sarkin Amalekawa da rai. Ya kuma hallaka dukan mutanensa da takobi.
Et il prit vif Agag, Roi d'Hamalec; mais il fît passer tout le peuple au fil de l'épée à la façon de l'interdit.
9 Amma Shawulu da sojojinsa suka bar Agag, da tumaki, da shanu, da’yan maruƙa masu ƙiba da kuma duk abin da yake mai kyau da rai. Waɗannan ba su so su hallaka su gaba ɗaya ba, amma duk abin da ba a so da kuma marar amfani suka hallaka.
Saül donc et le peuple épargnèrent Agag, et les meilleures brebis, les [meilleurs] bœufs, les bêtes grasses, les agneaux, et tout ce qui était bon; et ils ne voulurent point les détruire à la façon de l'interdit; ils détruisirent seulement à la façon de l'interdit tout ce qui n'était d'aucun prix, et méprisable.
10 Sai Ubangiji ya yi magana da Sama’ila ya ce,
Alors la parole de l'Eternel fut adressée à Samuel en disant:
11 “Na damu da na naɗa Shawulu sarki, domin ya juya mini baya, bai kuma bi umarnina ba.” Sama’ila ya damu ƙwarai, ya yi kuka ga Ubangiji dukan dare.
Je me repens d'avoir établi Saül pour Roi, car il s'est détourné de moi, et n'a point exécuté mes paroles. Et Samuel en fut fort attristé, et cria à l'Eternel toute cette nuit-là.
12 Kashegari da sassafe sai Sama’ila ya tashi ya tafi domin yă sadu da Shawulu, amma aka gaya masa cewa Shawulu ya tafi Karmel. A can ya yi wa kansa abin tunawa don yă girmama kansa, daga can kuma ya juya ya gangara zuwa Gilgal.
Puis Samuel se leva de bon matin pour aller au-devant de Saül. Et on fit rapport à Samuel, en disant: Saül est venu à Carmel, et voici il s'est fait [là] dresser une place, mais il s'en est retourné, et passant au delà il est descendu à Guilgal.
13 Da Sama’ila ya kai wurinsa, sai Shawulu ya ce, “Ubangiji yă albarkace ka, na aikata umarnin Ubangiji.”
Quand Samuel fut venu à Saül, Saül lui dit: Tu sois béni de l'Eternel; j'ai exécuté la parole de l'Eternel.
14 Amma Sama’ila ya ce, “Ashe, waɗannan ba kukan tumaki ke nan nake ji a kunnena ba? Wane kuka shanu ke nan nake ji?”
Et Samuel dit: Quel est donc ce bêlement de brebis à mes oreilles, et ce meuglement de bœufs que j'entends?
15 Shawulu ya amsa ya ce, “Sojoji ne suka kawo su daga Amalekawa. Sun bar tumaki da shanu masu kyau da rai don su yi wa Ubangiji Allahnka hadaya, amma sauran mun hallaka duka.”
Et Saül répondit: Ils les ont amenés des Hamalécites; car le peuple a épargné les meilleures brebis et les [meilleurs] bœufs, pour les sacrifier à l'Eternel ton Dieu; et nous avons détruit le reste à la façon de l'interdit.
16 Sama’ila ya ce, “Dakata, bari in faɗa maka abin da Ubangiji ya ce mini jiya da dare.” Shawulu ya ce, “Gaya mini.”
Et Samuel dit à Saül: Arrête, et je te déclarerai ce que l'Eternel m'a dit cette nuit; et il lui répondit: Parle?
17 Sama’ila ya ce, “Ko da yake kana ganin kanka kai ba wani abu ne ba, ashe, ba kai ne yanzu shugaban kabilan Isra’ila ba? Ubangiji ya shafe ka ka zama sarkin Isra’ila.
Samuel donc dit: N'est-il pas vrai que, quand tu étais petit à tes yeux, tu as été fait Chef des Tribus d'Israël, et l'Eternel t'a oint pour Roi sur Israël?
18 Shi kuma ya aika, ya umarce ka cewa, ‘Tafi ka hallaka Amalekawa mugayen mutanen nan duka, ka yaƙe su sai ka share su ƙaf.’
Or l'Eternel t'avait envoyé en cette expédition, et t'avait dit: Va, et détruis à la façon de l'interdit ces pécheurs, les Hamalécites, et fais-leur la guerre, jusqu'à ce qu'ils soient consumés.
19 Me ya sa ba ka bi umarnin Ubangiji ba? Me ya sa ka sa hannu a ganima, ka kuma yi mugun abu a gaban Ubangiji?”
Et pourquoi n'as-tu pas obéi à la voix de l'Eternel, mais tu t'es jeté sur le butin, et as fait ce qui déplaît à l'Eternel.
20 Shawulu ya ce, “Amma na bi umarnin Ubangiji. Na bi saƙon da Ubangiji ya ba ni. Na hallaka Amalekawa, na kuma kamo Agag sarkinsu.
Et Saül répondit à Samuel: J'ai pourtant obéi à la voix de l'Eternel, et je suis allé par le chemin par lequel l'Eternel m'a envoyé, et j'ai amené Agag Roi des Hamalécites, et j'ai détruit à la façon de l'interdit les Hamalécites.
21 Sojoji suka kawo tumaki da shanu mafi kyau daga cikin ganimar domin a miƙa hadaya ga Ubangiji Allahnka a Gilgal.”
Mais le peuple a pris des brebis et des bœufs du butin, [comme] des prémices de l'interdit, pour sacrifier à l'Eternel ton Dieu à Guilgal.
22 Amma Sama’ila ya ce, “Ubangiji yana murna da sadaka da hadaya fiye da biyayya ga maganar Ubangiji? Yin biyayya ta fi hadaya a kula kuma ta fi ƙibabbun raguna.
Alors Samuel dit: L'Eternel prend-il plaisir aux holocaustes et aux sacrifices, comme qu'on obéisse à sa voix? Voici, l'obéissance vaut mieux que le sacrifice, [et] se rendre attentif vaut mieux que la graisse des moutons;
23 Gama tawaye yana kama da zunubi na duba, girman kai kuma yana kama da bautar gumaka. Saboda ka ƙi maganar Ubangiji, shi ma ya ƙi ka da zaman sarki.”
Car la rébellion est [autant que] le péché de divination, et c'est une idole et un Théraphim que la transgression. Parce [donc] que tu as rejeté la parole de l'Eternel, il t'a aussi rejeté, afin que tu ne sois plus Roi.
24 Sai Shawulu ya ce wa Sama’ila, “Na yi zunubi, na ƙi bin umarnin Ubangiji, na kuma ƙi bin maganarka. Na ji tsoron mutane ne shi ya sa na bi maganarsu.
Et Saül répondit à Samuel: J'ai péché parce que j'ai transgressé le commandement de l'Eternel, et tes paroles; car je craignais le peuple, et j'ai acquiescé à sa voix.
25 Yanzu fa, ina roƙonka ka yafe mini zunubina, ka koma tare da ni, domin in yi wa Ubangiji sujada.”
Mais maintenant, je te prie, pardonne-moi mon péché, et retourne-t'en avec moi, et je me prosternerai devant l'Eternel.
26 Amma Sama’ila ya ce, “Ba zan koma tare da kai ba. Ka ƙi maganar Ubangiji, Ubangiji kuma ya ƙi ka da zama sarki a bisa Isra’ila.”
Et Samuel dit à Saül: Je ne retournerai point avec toi; parce que tu as rejeté la parole de l'Eternel, et que l'Eternel t'a rejeté, afin que tu ne sois plus Roi sur Israël.
27 Da Sama’ila ya juya zai tafi, sai Shawulu ya kama bakin rigarsa, sai rigar ta yage.
Et comme Samuel se tournait pour s'en aller, [Saül] lui prit le pan de son manteau, qui se déchira.
28 Sama’ila ya ce masa, “Ubangiji ya yage masarautar Isra’ila daga gare ka yau, ya ba wa wani daga cikin maƙwabtanka wanda ya fi ka.
Alors Samuel lui dit: L'Eternel a aujourd'hui déchiré le Royaume d'Israël de dessus toi, et l'a donné à ton prochain, qui est meilleur que toi.
29 Shi wanda yake Ɗaukakar Isra’ila ba ya ƙarya ko yă canja zuciyarsa, gama shi ba mutum ba ne da zai canja zuciyarsa.”
Et en effet; la force d'Israël ne mentira point, elle ne se repentira point; car il n'est pas un homme, pour se repentir.
30 Shawulu ya ce, “Na yi zunubi. Amma ina roƙonka ka ba ni girma a gaban dattawan mutanena da kuma a gaban Isra’ila, ka koma tare da ni domin in yi wa Ubangiji Allahnka sujada.”
Et Saül répondit: J'ai péché; [mais] honore moi maintenant, je te prie, en la présence des Anciens de mon peuple, et en la présence d'Israël, et retourne-t'en avec moi, et je me prosternerai devant l'Eternel ton Dieu.
31 Saboda haka sai Sama’ila ya koma tare da Shawulu, Shawulu kuwa ya yi wa Ubangiji sujada.
Samuel donc s'en retourna et suivit Saül; et Saül se prosterna devant l'Eternel.
32 Sa’an nan Sama’ila ya ce, “Kawo mini Agag sarkin Amalekawa.” Agag kuwa ya zo wurinsa daure da sarƙa, yana tunani cewa, “Tabbatacce zancen mutuwa dai ya wuce.”
Puis Samuel dit: Amenez-moi Agag Roi d'Hamalec. Et Agag vint à lui, faisant le gracieux; car Agag disait: Certainement l'amertume de la mort est passée.
33 Amma Sama’ila ya ce, “Yadda takobinka ya sa mata suka rasa’ya’ya, haka mahaifiyarka za tă zama marar’ya’ya a cikin mata.” Sama’ila kuwa ya kashe Agag a Gilgal a gaban Ubangiji.
Mais Samuel dit: Comme ton épée a privé les femmes [de leurs enfants], ainsi ta mère sera privée d'enfants entre les femmes. Et Samuel mit Agag en pièces devant l'Eternel à Guilgal.
34 Sai Sama’ila ya tafi Rama, amma Shawulu ya haura zuwa gidansa a Gibeya na Shawulu.
Puis il s'en alla à Rama; et Saül monta en sa maison à Guibbath-Saül.
35 Daga wannan rana Sama’ila bai ƙara saduwa da sarki Shawulu ba, har rasuwar Sama’ila, amma ya yi baƙin ciki sosai a kan Shawulu. Ubangiji kuwa ya damu da ya sa Shawulu ya zama Sarkin Isra’ila ba.
Et Samuel n'alla plus voir Saül jusqu'au jour de sa mort; quoique Samuel eût mené deuil sur Saül, de ce que l'Eternel s'était repenti d'avoir établi Saül pour Roi sur Israël.

< 1 Sama’ila 15 >