< 1 Sama’ila 15 >

1 Sama’ila ya ce wa Shawulu, “Ni ne wanda Ubangiji ya aika in shafe ka ka zama sarki bisa mutanensa Isra’ila. Saurara yanzu ka ji saƙo daga wurin Ubangiji.
[One day] Samuel said to Saul, “Yahweh sent me to appoint you to be the king of the Israeli people. So now listen to this message from Yahweh:
2 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Zan hori Amalekawa saboda abin da suka yi wa Isra’ila sa’ad da suka ba su wahala yayinda suka fito daga Masar.
Yahweh, [the commander] of the armies [of angels] has declared this: ‘I am going to punish [the descendants of] Amalek for [attacking] the Israeli people after the Israelis left Egypt.
3 Yanzu ka tafi ka yaƙi Amalekawa, ka hallaka kome da yake nasu, kada ka bar su da rai, ka kashe maza, da mata, da yara, da jarirai, da dabbobi, da tumaki, da raƙuma, da kuma jakuna.’”
So now go [with your army] and attack the Amalek people-group. Destroy them completely—destroy them and everything that belongs to them—the men and women, their children and infants, their cattle and sheep and camels and donkeys. Do not (spare any of them/allow any of them to remain alive)!’”
4 Sai Shawulu ya tattara sojoji, ya ƙidaya su a Telayim, ya sami su dubu ɗari biyu da dubu goma daga Yahuda.
So Saul summoned the army, and they gathered at Telaim [town]. There were 200,000 soldiers. 10,000 of them were from Judah, [and the others were from the other Israeli tribes].
5 Shawulu ya tafi birnin Amalek ya yi kwanto a kwari.
Then Saul went [with his army] to a town where some of the Amalek people-group lived. [His army prepared to attack them suddenly by] hiding in the valley.
6 Sai Shawulu ya ce wa Keniyawa, “Ku tashi ku bar Amalekawa don kada in hallaka ku tare da su, saboda kun yi wa dukan Isra’ilawa kirki, lokacin da suka fito daga Masar.” Saboda haka Keniyawa suka tashi suka bar Amalekawa.
Then Saul sent this message to the Ken people-group [who lived in that area]: “You acted kindly toward all our Israeli [ancestors] when they left Egypt. But we are going to kill all of the Amalek people-group, [because they opposed/attacked our ancestors]. So move away from where the Amalek people-group live. [If you do not move away], you will be killed when they are killed.” So [when] the Ken people-group [heard that, they immediately] left that area.
7 Sa’an nan Shawulu ya ci Amalekawa da yaƙi tun daga Hawila har zuwa Shur, a gabashin iyakar Masar.
Then Saul’s [army] slaughtered the Amalek people-group, from Havilah [town in the east] to Shur [town in the west]. Shur was at the border [between Israel and] Egypt.
8 Ya kama Agag sarkin Amalekawa da rai. Ya kuma hallaka dukan mutanensa da takobi.
Saul’s army captured Agag, the king of the Amalek people-group, but they killed everyone else.
9 Amma Shawulu da sojojinsa suka bar Agag, da tumaki, da shanu, da’yan maruƙa masu ƙiba da kuma duk abin da yake mai kyau da rai. Waɗannan ba su so su hallaka su gaba ɗaya ba, amma duk abin da ba a so da kuma marar amfani suka hallaka.
They not only (spared/did not kill) Agag, but they also took the best sheep and goats and cattle. They took everything that was good. They destroyed only the animals that they considered to be worthless.
10 Sai Ubangiji ya yi magana da Sama’ila ya ce,
Then Yahweh said to Samuel,
11 “Na damu da na naɗa Shawulu sarki, domin ya juya mini baya, bai kuma bi umarnina ba.” Sama’ila ya damu ƙwarai, ya yi kuka ga Ubangiji dukan dare.
“I am sorry that I appointed Saul to be your king, because he has turned away from me and has not obeyed what I commanded him to do.” Samuel was very disturbed/upset [when he heard that], and he cried out to Yahweh all that night.
12 Kashegari da sassafe sai Sama’ila ya tashi ya tafi domin yă sadu da Shawulu, amma aka gaya masa cewa Shawulu ya tafi Karmel. A can ya yi wa kansa abin tunawa don yă girmama kansa, daga can kuma ya juya ya gangara zuwa Gilgal.
Early the next morning, Samuel got up and went to talk with Saul. But someone told Samuel, “Saul went to Camel [city], where he has set up a monument to honor himself. Now he has left there and gone down to Gilgal.”
13 Da Sama’ila ya kai wurinsa, sai Shawulu ya ce, “Ubangiji yă albarkace ka, na aikata umarnin Ubangiji.”
When Samuel arrived [at Gilgal] he approached Saul, and Saul said to him, “I wish/desire that Yahweh will bless you! I have obeyed what Yahweh told me to do.”
14 Amma Sama’ila ya ce, “Ashe, waɗannan ba kukan tumaki ke nan nake ji a kunnena ba? Wane kuka shanu ke nan nake ji?”
But Samuel replied, “If that is true, why is it that I hear cattle mooing and I hear sheep bleating?”
15 Shawulu ya amsa ya ce, “Sojoji ne suka kawo su daga Amalekawa. Sun bar tumaki da shanu masu kyau da rai don su yi wa Ubangiji Allahnka hadaya, amma sauran mun hallaka duka.”
Saul replied, “The soldiers took them from the Amalek people-group. They saved the best sheep and cattle, in order to offer them as sacrifices to Yahweh, your God. But we have completely destroyed all the others.”
16 Sama’ila ya ce, “Dakata, bari in faɗa maka abin da Ubangiji ya ce mini jiya da dare.” Shawulu ya ce, “Gaya mini.”
Samuel said to Saul, “Stop [talking]! Allow me to tell you what Yahweh said to me last night.” Saul replied, “Tell me [what he said].”
17 Sama’ila ya ce, “Ko da yake kana ganin kanka kai ba wani abu ne ba, ashe, ba kai ne yanzu shugaban kabilan Isra’ila ba? Ubangiji ya shafe ka ka zama sarkin Isra’ila.
Samuel said, “Previously you did not think that you were important. But now you have become [RHQ] the leader of the tribes of Israel. Yahweh appointed you to be their king.
18 Shi kuma ya aika, ya umarce ka cewa, ‘Tafi ka hallaka Amalekawa mugayen mutanen nan duka, ka yaƙe su sai ka share su ƙaf.’
And Yahweh sent you to do something [for him]. He said to you, ‘Go and get rid of all those sinful people, the Amalek people-group. Attack them and kill all of them.’
19 Me ya sa ba ka bi umarnin Ubangiji ba? Me ya sa ka sa hannu a ganima, ka kuma yi mugun abu a gaban Ubangiji?”
So why did you not obey Yahweh [RHQ]? Why did your men take the best animals [RHQ]? Why did you do what Yahweh said was evil?” [RHQ]
20 Shawulu ya ce, “Amma na bi umarnin Ubangiji. Na bi saƙon da Ubangiji ya ba ni. Na hallaka Amalekawa, na kuma kamo Agag sarkinsu.
Saul replied to Samuel, “Hey, I did what Yahweh sent me to do! I brought back King Agag, but we killed everyone else!
21 Sojoji suka kawo tumaki da shanu mafi kyau daga cikin ganimar domin a miƙa hadaya ga Ubangiji Allahnka a Gilgal.”
My men brought back only the best sheep and cattle and other things, in order to sacrifice them to Yahweh your God here at Gilgal.”
22 Amma Sama’ila ya ce, “Ubangiji yana murna da sadaka da hadaya fiye da biyayya ga maganar Ubangiji? Yin biyayya ta fi hadaya a kula kuma ta fi ƙibabbun raguna.
But Samuel replied, “Which [do you think] pleases Yahweh more, animals that are completely burned [on the altar] and other sacrifices, or people obeying him [SYN]? It is better to obey [Yahweh] than [to offer] sacrifices [to him]. It is better to pay attention to what he says than [to burn] the fat of rams, [even though God said they should be sacrificed to him].
23 Gama tawaye yana kama da zunubi na duba, girman kai kuma yana kama da bautar gumaka. Saboda ka ƙi maganar Ubangiji, shi ma ya ƙi ka da zaman sarki.”
To rebel [against God] is as sinful as doing sorcery/black magic, and being stubborn is as sinful as worshiping idols. So, because you disobeyed what Yahweh told you to do, he has declared that you will no longer be king.”
24 Sai Shawulu ya ce wa Sama’ila, “Na yi zunubi, na ƙi bin umarnin Ubangiji, na kuma ƙi bin maganarka. Na ji tsoron mutane ne shi ya sa na bi maganarsu.
Then Saul said to Samuel, “[Yes], I have sinned. I disobeyed what you told me to do, which is what Yahweh commanded. I did that because I was (afraid of/worried about) what my men would say [if I did not do what they wanted]. So I did what they demanded.
25 Yanzu fa, ina roƙonka ka yafe mini zunubina, ka koma tare da ni, domin in yi wa Ubangiji sujada.”
But now, please forgive me for having sinned. And come back with me [to where the people are] in order that I may worship Yahweh.”
26 Amma Sama’ila ya ce, “Ba zan koma tare da kai ba. Ka ƙi maganar Ubangiji, Ubangiji kuma ya ƙi ka da zama sarki a bisa Isra’ila.”
But Samuel replied, “No, I will not go back with you. You have rejected/disobeyed what Yahweh commanded you to do. So he has rejected you, [and declared that you will no longer] be the king of Israel. [So I do not want to talk any more with you].”
27 Da Sama’ila ya juya zai tafi, sai Shawulu ya kama bakin rigarsa, sai rigar ta yage.
As Samuel turned to leave, Saul tried to stop him by grabbing the edge of Samuel’s robe, and it tore.
28 Sama’ila ya ce masa, “Ubangiji ya yage masarautar Isra’ila daga gare ka yau, ya ba wa wani daga cikin maƙwabtanka wanda ya fi ka.
Samuel said to him, “[You tore my robe! And] today Yahweh has torn away from you the kingdom of Israel! He will appoint someone else to be king, someone who is a better man than you are.
29 Shi wanda yake Ɗaukakar Isra’ila ba ya ƙarya ko yă canja zuciyarsa, gama shi ba mutum ba ne da zai canja zuciyarsa.”
And since the one who is the glorious [God] of the Israeli people does not lie, he will not change (his mind/what he has said). Humans sometimes change their minds, but God does not do that, because he is not a human.”
30 Shawulu ya ce, “Na yi zunubi. Amma ina roƙonka ka ba ni girma a gaban dattawan mutanena da kuma a gaban Isra’ila, ka koma tare da ni domin in yi wa Ubangiji Allahnka sujada.”
Then Saul [pleaded again. He] said, “I know that I have sinned. But please honor me in front of the leaders of the Israeli people and in front of all the other Israeli people by coming back [to them] with me in order that I may worship Yahweh your God.”
31 Saboda haka sai Sama’ila ya koma tare da Shawulu, Shawulu kuwa ya yi wa Ubangiji sujada.
So Samuel finally agreed to do that, and they went together back [to where the people were], and Saul worshiped Yahweh there.
32 Sa’an nan Sama’ila ya ce, “Kawo mini Agag sarkin Amalekawa.” Agag kuwa ya zo wurinsa daure da sarƙa, yana tunani cewa, “Tabbatacce zancen mutuwa dai ya wuce.”
Then Samuel said, “Bring King Agag to me.” So they brought Agag to him. Agag was confidently expecting that they would spare him/not kill him. He was thinking, “Surely I will not have to endure an agonizing death!”
33 Amma Sama’ila ya ce, “Yadda takobinka ya sa mata suka rasa’ya’ya, haka mahaifiyarka za tă zama marar’ya’ya a cikin mata.” Sama’ila kuwa ya kashe Agag a Gilgal a gaban Ubangiji.
But Samuel said to him, “You have killed the sons of many women with your sword, so now your mother will no longer have a son.” And Samuel cut Agag into pieces [with his sword], there at Gilgal, in the presence of Yahweh.
34 Sai Sama’ila ya tafi Rama, amma Shawulu ya haura zuwa gidansa a Gibeya na Shawulu.
Then Samuel left there and returned to his home in Ramah, and Saul went to his home in Gibeah.
35 Daga wannan rana Sama’ila bai ƙara saduwa da sarki Shawulu ba, har rasuwar Sama’ila, amma ya yi baƙin ciki sosai a kan Shawulu. Ubangiji kuwa ya damu da ya sa Shawulu ya zama Sarkin Isra’ila ba.
Samuel never saw Saul again, but he was very sad about [what] Saul [had done]. And Yahweh was very sorry that he had appointed Saul to be the king of Israel.

< 1 Sama’ila 15 >