< 1 Sama’ila 14 >

1 Wata rana Yonatan ɗan Shawulu ya ce wa saurayin da yake ɗaukar masa makamai, “Zo mu tafi wajen sansanin Filistiyawa a wancan hayi.” Amma bai gaya wa mahaifinsa ba.
Sa yiğıl Şaulne duxee Yonatanee cun silah haqqane nukarık'le eyhen: – Qora derayne şene suralyne Filiştinaaşine desteysqa ılğeepç'es. Mançine hək'ee, mang'vee dekkık'le eyhe deş.
2 Shawulu kuwa na zaune a gindin itacen rumman a bayan garin Gibeya a Migron. Tare da shi akwai mutum wajen ɗari shida.
Şaulna çadırmee Givea ç'əvooxhene cigee Migroneene sa narıne yivek avub güvxü vuxha. Mang'une k'ane yixhıd vəşşilqa ələəna insan eyxhe.
3 A cikinsu akwai Ahiya sanye da efod. Shi yaron Ikabod ɗan’uwan Ahitub ne, ɗan Finehas, ɗan Eli, firist na Ubangiji a Shilo. Ba wanda ya san cewa Yonatan ya tafi wani wuri.
Manbışika sacigee kaahinaaşin ileylığ givatxınna kaahin Axiyar eyxhena. Mana İkavodne çocuna, Axituvna dix eyxhe. Axituvur, Şilo eyhene cigee eyxhene Rəbbine kaahinna Eliyna neva, Pinxasna dix eyxhe. Yonatanın ark'ıniy şavuk'lecad ats'a ıxha deş.
4 A kowane gefe na mashigin da Yonatan ya so yă bi zuwa wurin Filistiyawa, akwai hawa mai tsawo, ana kira ɗaya Bozez, ɗayan kuma ana kira Senet.
Filiştinaaşina deste ulyobzurne cigeeqa ı'qqəsdemee Yonatan q'öne ganznane cigeençe ılğeç'e. Mane ganzbışin sançin do Botsets, mansançinıd Sene ıxha.
5 Hawan da yake arewa yana fuskantar Mikmash, wanda yake kudu kuma yana fuskantar Geba.
Ganzbışin sa şimalne surayle Mikmasıqa, mansa ganzmee canubne surayle Giveayqa ilyakka ıxha.
6 Yonatan ya ce wa saurayin mai ɗaukan makamai, “Zo mu haye zuwa mashigin mutane marasa kaciyan nan, wataƙila Ubangiji zai yi aiki a madadinmu. Ba abin da zai iya hana Ubangiji yin aikin ceto ta wurin mutane masu yawa, ko ta wurin mutane kaɗan.”
Yonatanee cune silah haqqane nukarık'le eyhen: – Qora ine sunnat hıdyav'uynbışde desteysqa ılğeepç'es. Sayid Rəbbee yişin sura aqqaqqa. Rəbbis ıkkanang'a, geebnanbı ğamaa'a, ıkkanang'ab, k'ılybananbı ğamaa'a.
7 Mai ɗaukan makaman ya ce, “Ka yi duk abin da yake zuciyarka. Ci gaba, ina tare da kai gaba da baya.”
Mang'une nukaree eyhen: – Yiğne yik'es nəxüdiy ıkkan həməxüdud he'e. Hoora he'e, ğu nyaqa ark'ınee, zı vaka vor.
8 Yonatan ya ce, “To, zo mu haye zuwa wajen mutanen, mu sa su gan mu.
Yonatanee eyhen: – Qora şene insanaaşisqa ılğeepç'es, manbışik'le şicab şi haagvas.
9 In suka ce mana, ‘Ku tsaya nan har mu zo wurinku,’ za mu dakata inda muke, ba za mu haura wajensu ba.
Manbışe şak'le «Şi şosqa qavaalesmee ulyoozreva» uvheene, şi ulyobzurne cigeençe ı'ğdiviykar, cosqab ılqıdebaç'e.
10 Amma in suka ce mana, ‘Ku haura wurinmu,’ to, sai mu haura, wannan zai zama mana alama cewa Ubangiji ya bashe su a hannunmu.”
De'eş, cone k'anyaqa ılqeepç'eva uvhee, şinab ılqeebaç'e. Man yişdemee, Rəbbee man insanar yişde xılyaqa quvuva işaara eyxhe.
11 Sai suka nuna kansu a sansanin Filistiyawa. Sai Filistiyawa suka ce, “Ku duba ga Ibraniyawa suna fitowa daga cikin ramummuka inda suka ɓuya.”
Manbışda q'öyursana şenbışde zastaveençe g'avcesde cigee ulyoozar. Filiştinaaşe eyhen: – İlyaakende, cühüt'yar dyuguleepxhayne q'əç'ürbışeençe qığəə vob.
12 Mutanen da suke sansanin suka kira Yonatan da mai ɗaukan makamansa da babbar murya suka ce, “Ku hauro wajenmu, mu kuwa za mu koya muku hankali.” Sai Yonatan ya ce wa mai ɗaukan makamansa, “Biyo ni, gama Ubangiji ya bashe su a hannun Isra’ila.”
Eskeraaşe Yonatanık'leyiy mang'un nukarık'le eyhen: – Şasqa ılqeepç'e, vuşun darsbı qeles. Yonatanee cune nukarık'le eyhen: – Zaqar qihna qora, Rəbbee manbı İzrailyne xılyaqa quvu.
13 Sai Yonatan ya hau dutsen da rarrafe, mai ɗaukan makamansa kuwa yana biye. Yonatan ya yi ta fyaɗa Filistiyawa da ƙasa, mai ɗaukan makamansa kuma ya yi ta karkashe su.
Yonatan g'elybışikayiy xıleppışika ilyt'iyq'an-ilyt'iyq'an ooqa ılqeç'e. Cuqar qihnar cuna nukar ılqeç'e. Yonatan ooqa ılqeç'u, Filiştinar uvxü hı'ğəəkar haa'anbı, cuqar qihna qööne nukareeyib manbı gyabat'anbı.
14 A wannan karo na farko Yonatan da mai ɗaukan makamansa suka kashe mutum wajen ashirin a wani fili mai fāɗi rabin kadada.
Ts'eppa aldaaxhvan gibğılmee, Yonataneeyiy cune silah haqqane nukaree g'ane insanılqa ələəna insan gek'a. Manbı q'öne yatsısse sa yiğee ezas əxəsde çolun surameene cigee aldaaxhvan vuxha.
15 Sai tsoro ya kama dukan sojojin Filistiyawa, waɗanda suke cikin sansanin da waɗanda suke fili, har da waɗanda suke waje, da kuma waɗanda suke kai hari, ƙasa ta girgiza. Allah ne ya kawo wannan rikicewa.
Zastaveeneyiy çolbışeene milletne yik'eeqa qəpq'ı'niy eç'e. Zastaveene eskeraaşineyiy ts'eppa ögeeqa aldaaxhvanas avayk'ananbışde yı'q'nee məxdın alikkiy-gikkiy gexha, mançike ç'iyecad ı'ğiykar. Man qəpq'ı'niy Allahee g'axuvu eyxhe.
16 Masu gadin Shawulu a Gebiya da take a Benyamin suka duba sai ga rundunar Filistiyawa a warwatsewa ko’ina.
Benyaminaaşine Giveayee vooxhene Şaulne mane cigayqa ilyaakane eskeraaşik'le, Filiştinaaşin eskerar opt'ul-opxul heepxı əlyhəə g'ooce.
17 Sai Shawulu ya ce wa mutanen da suke tare da shi, “Ku ƙidaya mayaƙa ku ga wane ne ba ya nan.” Da suka ƙirga sai suka tarar Yonatan da mai ɗaukan makamansa ba sa nan.
Şaulee cune hıqiy-alla sadıyne milletık'le, eyhen: – Qəpqe, ilyaake vuşuyiy yişinbışda deş. Qəpqı'mee, manbışik'le Yonatanıy mang'una silah haqqana cokasana maa devxhay ats'axhxhen.
18 Shawulu ya ce wa Ahiya, “Kawo akwatin alkawarin Allah.” (A lokacin akwatin alkawarin yana tare da Isra’ilawa.)
Şaulee Axiyayk'le eyhen: – Allahna q'utye inyaqa qavaale. (Şene gahbışil Allahna q'utye İzrailybışiqa vuxha.)
19 Yayinda Shawulu yake magana da firist kuwa, harguwa ya yi ta ƙaruwa a sansanin Filistiyawa. Sai Shawulu ya ce wa firist, “Janye hannunka.”
Şaulee kaahinık'le manva eyhemee, Filiştinaaşine g'oşunnane cigee alikkı-gikkiy sık'ıldad geed qexhe. Şaulee kaahinık'le «Qımaaleva!» eyhe.
20 Sa’an nan Shawulu da dukan mutanensa suka taru suka tafi yaƙi. Suka tarar Filistiyawa sun ruɗe suna yaƙi da juna da takubansu.
Şaulıy mang'une hiqiy-alla sadıyn gırgın millet, dəv'ə əlyhəəne cigeeqa ayk'an. Manbışik'le Filiştinar alivku-givku, sana-sanbı g'ılıncbışika gyabat'a g'ooce.
21 Ibraniyawan da suke tare da Filistiyawa a dā, waɗanda suka bi Filistiyawan zuwa sansanin yaƙinsu, suka juya, suka goyi bayan Shawulu da Yonatan sa’ad da yaƙin ya taso.
Ts'eppiykecab Filiştinaaşine suralqa, manbışde zastaveeqa ılğeepç'ıyn cühüt'yar, Şaulneyiy Yonatanne k'anene İzrailyne milletne suralqa ılğeebaç'e.
22 Sa’ad da dukan Isra’ilawan da suka ɓuya a duwatsu a ƙasar Efraim suka ji labari cewa Filistiyawa suna gudu, sai suka fito suka fafare su.
Efrayimaaşine suvabınane cigabışee dyugul vuxhayne gırgıne İzrailybışik'led, Filiştinaaşin heepxıy g'ayxhımee, manbıb conbışika sacigee Filiştinaaşiqa qihna gyabak'a.
23 Haka Ubangiji ya kuɓutar da Isra’ila a wannan rana. Yaƙin kuwa ya ci gaba har gaba da Bet-Awen.
Məxüb mane yiğıl Rəbbee İzrail g'attivxhanaa'ana. Dəv'əb Bet-Avenısqa hiviyxhar.
24 A wannan rana, Isra’ilawa suka sha wahala ƙwarai domin Shawulu ya sa mutane suka yi rantsuwa cewa, “La’ananne ne mutumin da ya ci abinci kafin fāɗuwar rana, kafin in ɗauki fansa a kan abokan gābana.” Don haka ba mutumin da ya ɗanɗana abinci.
İzrailybı mane yiğıl geeb obzur vooxhe. Şaulee «Exhalilqamee, zı duşmanaaşikın ha'asmee, şavaayiy gıney otxhun bed-düə vuxhenava!» uvhu, g'oşunusqa k'ın g'assaras ilekka. G'oşuneenbışike şavaacad ghalik vuççud set'a deş.
25 Dukan rundunar ta shiga kurmi, sai ga zuma a ƙasa.
G'oşun ç'alagaqa ikkeç'umee, manbışik'le ç'iyel itv g'ece.
26 Da suka shiga ciki kurmin, suka ga zuma tana zubowa, duk da haka ba wanda ya sa yatsansa ya lasa saboda tsoron rantsuwar da suka yi.
G'oşunuk'le ç'alagee g'acuyne p'et'aybışike itv gyodatsts'e ıxheeyid, şavaacad xıl ghalyaqa ıkkekka deş. Manbı co g'assırne k'ınile qəvəyq'ən vuxha.
27 Yonatan bai san cewa mahaifinsa ya sa mutane suka yi rantsuwa ba. Sai ya sa gindin sandan da yake hannunsa a saƙar zuma, ya kai bakinsa. Nan da nan sai ya ji ƙarfin jiki ya zo masa.
Yonatanık'le, dekkee g'oşunusqa k'ın g'assaras alikkiy ats'a deşdiy. Mang'vee xıledın t'at'aa hotku ç'iyelyne ittveeqa k'yoq'u, qiyğad t'at'alyne ittulqa xıl qadğu, ghalyaqa ıkkekka. Manke mang'une uleppışeeqa işix qayle.
28 Sai wani soja ya gaya masa cewa, “Mahaifinka ya sa kowa ya yi rantsuwa cewa, ‘La’ananne ne mutumin da ya ci abinci kafin fāɗuwar rana!’ Shi ya sa duk sojojin ba su da ƙarfi.”
G'oşuneene sang'vee eyhen: – «G'iyna şavaayiy kar otxhun mang'us bed-düə vuxhenava!» uvhu, yiğne dekke g'oşunusqa it'umun k'ın g'assarasniy alikkı. Mançil-allab eskerar g'elike-xıleke g'a'apk'ı.
29 Yonatan ya ce, “Mahaifina ya jefa ƙasar cikin matsala. Duba yadda na ji ƙarfin jiki sa’ad da na ɗanɗana wannan’yar zuma mana.
Yonatanee eyhen: – Dekkee, g'oşunus əq'üba vob hoole. İlyaakende, zı mane ittvuke sık'ınincad otxhun, uleppışeeqa işix qadı!
30 Da yaya zai kasance ke nan da a ce an bar sojoji suka ci abincin da suka ƙwace daga abokan gābansu? Ai, da gawawwakin Filistiyawan da aka kashe sun fi haka.”
G'iyna eskeraaşe duşmanaaşike g'ayşuyne otxhuniybışike avts'esınmeen otxhun ıxhaynxhiy, hucoo dexheyiy? Nya'a, Filiştinaaşile sık'ılbab yugba ğamdeebaxheyiy?
31 A ranan nan Isra’ilawa suka yi ta kashe Filistiyawa daga Mikmash har zuwa Aiyalon. Bayan haka gajiya ta kama su sosai saboda yunwa.
Mane yiğıl Şaulna g'oşun, Mikmasıle Ayaloneeqamee Filiştinaaşile ğameebaxhenbı. Mane yiğıl eskerar geeb obzur vooxhe.
32 Sai suka yi warwason ganima, suka kwashe tumaki, da shanu, da maruƙa, suka yayyanka su, suka ci naman ɗanye.
Eskeraaşe cone xılyaqa aytk'uyn Filiştinaaşin vəq'əbı, yatsbı, vuç'ebı zarada maacad gyat'u, ebakacad çuru oyxhan.
33 Sai wani mutum ya ce wa Shawulu, “Duba, ga mutane suna zunubi ga Ubangiji, suna cin nama da jini.” Shawulu ya ce, “Kun ci amana. Ku mirgino babban dutse zuwa wurina nan da nan.”
Man Şaululqa hixhar ha'a: – İlyaakende, eskeraaşe çuru ebakacad otxhun, Rəbbine ögil bınah haa'a. Şaulee eyhen: – Şu Rəbb yik'el hixanı'ı, həşdeme zasqa sa xəbna g'aye qa'aak'an hee'e.
34 Sa’an nan ya ce, “Ku tafi ku faɗa wa jama’a duka, su kawo shanu da tumaki a nan, su yayyanka, su ci a nan, don kada su yi wa Ubangiji zunubi da cin nama ɗanye.” Haka nan kowa ya kawo saniyarsa a daren, ya yanka a can.
Meed Şauleecad eyhen: – G'oşunne yı'q'neençe ılğeepç'ı, manbışik'le eyhe: «Gırgıng'vee cuna yats, vəq'ə zasqa abı, kara'əəba yizde k'ane, mane g'ayel givk'u ooxhnecen. Çuru ebaka otxhun, Rəbbine ögil bınah hımaa'a». Mane xəmde gırgıng'vee, con yatsbıyiy vəq'əbı maqa adı, cone xıleka gyaat'a.
35 Sa’an nan Shawulu ya gina wa Ubangiji bagade. Wannan ne bagade na farkon da ya gina.
Məxüd Şaulee ts'etta Rəbbis q'urbanbı allya'an ciga ali'ı.
36 Shawulu ya ce, “Mu bi gangara mu fafare Filistiyawa da dare mu washe su har gari yă waye, mu kuma karkashe kowannensu, kada mu bar wani da rai.” Suka ce, “Ka yi duk abin da ka ga ya fi maka kyau.” Amma firist ya ce, “Bari mu nemi nufin Allah tukuna.”
Şaulee eyhen: – Qudoora, Filiştinaaşiqab qihna xəmdecab gyapk'as, miç'eediy qıxhesse, manbışin vodun-deşin g'ayşu, con gırgınbıb gyapt'as. Mang'uk'le «Vas nəxüdiy ıkkan həməxüdud he'eva» eyhe. Kaahineeme «Qudoora, Rəbbike qiyghanasva» eyhe.
37 Saboda haka Shawulu ya tambayi Allah ya ce, “Mu bi bayan Filistiyawa? Za ka bashe su a hannun Isra’ila?” Amma Allah bai ba shi amsa a ranar ba.
Şaulee Allahıke qiyghanan: – Zı Filiştinaaşiqa qihna gixhene? Ğu manbı İzrailybışde xılyaqa qevlesınbıne? Mane yiğıl Allahee mang'us alidghıniy qele deş.
38 Saboda haka Shawulu ya ce, “Ku zo nan dukanku shugabannin rundunoni, mu bincika mu san zunubin da ya kawo rashin amsan nan yau.
Şaulee eyhen: – G'oşunun ç'ak'ınbı, vuşun gırgınbı inyaqa savaale. Şu g'iyna nena bınahiy hav'uva, ats'axhxhes.
39 Muddin Ubangiji wanda ya ceci Isra’ila yana raye, ko da ɗana Yonatan ne ya yi zunubin, dole yă mutu.” Amma ba ko ɗaya daga cikinsu da ya ce uffam.
İzrail g'attivxhan hav'uyne, Vorne Rəbbilqan k'ın ixhen, ine işee yizde duxayn, Yonatanınıd, xıl ixheene, mana gik'as ıkkan. Milletıke şavaacad nıq' qığavhu deş.
40 Sai Shawulu ya ce wa dukan Isra’ilawa, “Ku tsaya a can, ni kuma da Yonatan ɗana mu tsaya a nan.” Mutanen suka ce, “Ka yi abin da ya fi maka kyau.”
Şaulee İzrailyne gırgınbışik'le eyhen: – Şu sa sural, zınar yizde duxayka manesa sural ulyoozaras. Eskeraaşe Şauluk'le: «Yiğne yik'es ıkkanəxüd he'eva» eyhe.
41 Sa’an nan Shawulu ya yi addu’a ga Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, “Me ya sa ba ka amsa mini addu’ata a yau ba? Idan wannan laifina ne, ko kuwa na ɗana, Yonatan, ka nuna mana ta wurin Urim, amma idan laifin mutanen ne ka amsa ta wurin Tummim.” Ba a sami mutane da laifi ba, amma ƙuri’a ta fāɗa a kan Yonatan da Shawulu.
Şaulee İzrailyne Allahık'le, Rəbbik'le, eyhen: – Zas qotkuyn alidghıniy qele! K'eççuyne çöpün Şaulıy Yonatan haagva. Bınah milletıl aaxva deş.
42 Shawulu ya ce, “Ku jefa ƙuri’a tsakanina da ɗana Yonatan.” Sai ƙuri’ar ta fāɗa a kan Yonatan.
Şaulee eyhen: – Yizdeyiy duxayne Yonatanne yı'q'neeyid çöp k'eççe. Çöpün Yonatan hagva.
43 Sai Shawulu ya ce wa Yonatan, “Gaya mini mene ne ka yi.” Yonatan ya ce masa, “Na ɗanɗana zuma kaɗan daga gindin sandanta. Yanzu kuwa dole in mutu!”
Şaulee Yonatanık'le eyhen: – Ğu hucoone hı'ı, zak'le eyhe! Yonatanee mang'uk'le eyhen: – Xılene t'at'aane sivelin sık'ınin itv otxhun. Zı mançil-alla qik'asda.
44 Shawulu ya ce, “Bari hukunci mai tsanani na Allah yă kasance a kaina, in ba ka mutu ba, Yonatan.”
Şaulee eyhen: – Yonatan, ğu g'iyna q'idek'vee, hasre Allahee zas mançiled pisın he'ecen!
45 Amma mutane suka ce wa Shawulu, “A ce Yonatan yă mutu bayan shi ya kawo babban nasara a Isra’ila? Faufau, muddin Ubangiji yana raye, ko gashin kansa ɗaya ba zai fāɗi a ƙasa ba, gama abin da ya yi yau, Allah ne yana tare da shi.” Ta haka mutane suka ceci Yonatan daga mutuwa.
Milletınmee Şauluk'le eyhen: – İzrail məxüb uftanba ğamav'una, Yonatanne qik'as? De'eş! Vorne Rəbbilqan k'ın ixhen, mang'une vuk'lelyna sa ç'ərıb ç'iyelqa g'a'avxhas deş. Nya'a, mang'vee g'iyna Allahne kumaagıka iş g'avcu. Məxür Yonatan milletın qik'uyke g'attixhan ha'a, gik'as haysar deş.
46 Sai Shawulu ya daina bin Filistiyawa, suka koma ƙasarsu.
Şaulur Filiştinaaşiqar qihna gexha deş. Filiştinarıb cone cigabışeeqa siviyk'al.
47 Bayan Shawulu ya hau karagar mulkin Isra’ila, ya yi yaƙi da abokan gābansu ta kowane gefe. Mowabawa, Ammonawa, mutanen Edom, sarakunan Zoba, da kuma Filistiyawa. Duk wurin da ya juya, ya hore su.
Şaul İzrailyna paççah ıxhayle qiyğa, mang'vee hiqiy-allane cone duşmanaaşika: Moavaaşika, Ammonaaşika, Edomaaşika, Tsovayne paççahaaşika, Filiştinaaşika dəv'ə haa'a. Mana nene suralqa ark'ınee duşmanaaşine vuk'lelqa ver ooxa vuxha.
48 Ya yi jaruntaka sosai, ya ci Amalekawa da yaƙi, ya kuma ceci Isra’ila daga hannuwan waɗanda suka ƙwace musu kaya.
Mana yik'eka sacikku Amalekaaşile ğamxha, İzrail q'əra qaa'anbışike g'attivxhanaa'ana.
49 ’Ya’yan Shawulu maza su ne, Yonatan, Ishbi, da Malki-Shuwa. Sunan babban’yarsa ita ce Merab, ƙaramar kuma Mikal.
Yonatan, İşvi, Malki-Şua Şaulun dixbı vuxha. Mang'une xənne yişşen do Merav, k'ıning'ı'nıd Mikal ıxha.
50 Sunan matarsa kuwa Ahinowam,’yar Ahimawaz. Sunan shugaban ƙungiyar sojan Shawulu kuwa Abner ne ɗan Ner, shi Ner kuwa ɗan’uwan mahaifin Shawulu ne.
Şaulne xhunaşşeyn do Axinoam eyxhe. Mana Axima'atsna yiş yixha. Şaulne g'oşunna xərna Avner ıxha. Avner Şaulne emisiyna, Nerna dix ıxha.
51 Mahaifin Shawulu, Kish da kuma Ner mahaifin Abner,’ya’yan Abiyel ne.
Şaulna dek Gişiy Avnerna dek Ner Avielin dixbı vuxha.
52 Dukan kwanakin Shawulu sun kasance na yaƙe-yaƙe da Filistiyawa ne. Duk lokacin da Shawulu ya ga ƙaƙƙarfan mutum ko jarumi, sai yă ɗauke shi aikin sojansa.
Şaulna ı'mı'rcab Filiştinaaşikane yı'q'ne dəv'ee ılğevç'u. Gucukana, yik'ekana insan nyaariy mang'usqa qızaxxı, mang'vee cusqa alyarat'a ıxha.

< 1 Sama’ila 14 >