< 1 Sama’ila 14 >
1 Wata rana Yonatan ɗan Shawulu ya ce wa saurayin da yake ɗaukar masa makamai, “Zo mu tafi wajen sansanin Filistiyawa a wancan hayi.” Amma bai gaya wa mahaifinsa ba.
Kwasekusithi ngolunye usuku, uJonathani indodana kaSawuli wathi emfaneni othwala izikhali zakhe: Woza sichaphele ebuthweni lenqaba yamaFilisti elingaphetsheya ngale. Kodwa kamtshelanga uyise.
2 Shawulu kuwa na zaune a gindin itacen rumman a bayan garin Gibeya a Migron. Tare da shi akwai mutum wajen ɗari shida.
USawuli wayehlala-ke ephethelweni leGibeya ngaphansi kwesihlahla sepomegranati esiseMigironi; labantu ababelaye babengaphose babe ngamadoda angamakhulu ayisithupha;
3 A cikinsu akwai Ahiya sanye da efod. Shi yaron Ikabod ɗan’uwan Ahitub ne, ɗan Finehas, ɗan Eli, firist na Ubangiji a Shilo. Ba wanda ya san cewa Yonatan ya tafi wani wuri.
loAhiya, indodana kaAhitubi, umfowabo kaIkabodi, indodana kaPhinehasi, indodana kaEli, umpristi weNkosi eShilo, wayembethe i-efodi. Kodwa abantu babengazi ukuthi uJonathani uhambile.
4 A kowane gefe na mashigin da Yonatan ya so yă bi zuwa wurin Filistiyawa, akwai hawa mai tsawo, ana kira ɗaya Bozez, ɗayan kuma ana kira Senet.
Laphakathi kwemikhandlo, lapho uJonathani ayezama ukuchapha khona ukuya ebuthweni lenqaba yamaFilisti, kwakuledwala elicijileyo nganeno, ledwala elicijileyo ngaphetsheya; njalo ibizo lelinye laliyiBozezi, lebizo lelinye laliyiSene.
5 Hawan da yake arewa yana fuskantar Mikmash, wanda yake kudu kuma yana fuskantar Geba.
Elinye iliwa laligxile enyakatho maqondana leMikimashi, lelinye ngeningizimu maqondana leGeba.
6 Yonatan ya ce wa saurayin mai ɗaukan makamai, “Zo mu haye zuwa mashigin mutane marasa kaciyan nan, wataƙila Ubangiji zai yi aiki a madadinmu. Ba abin da zai iya hana Ubangiji yin aikin ceto ta wurin mutane masu yawa, ko ta wurin mutane kaɗan.”
UJonathani wasesithi emfaneni othwala izikhali zakhe: Woza sichaphele ebuthweni lenqaba elalaba abangasokanga; mhlawumbe iNkosi izasisebenzela, ngoba kakulasenqabelo eNkosini ukusindisa ngabanengi loba ngabalutshwana.
7 Mai ɗaukan makaman ya ce, “Ka yi duk abin da yake zuciyarka. Ci gaba, ina tare da kai gaba da baya.”
Umthwali wezikhali zakhe wasesithi kuye: Yenza konke okusenhliziyweni yakho; phambuka, khangela ngilawe njengokwenhliziyo yakho.
8 Yonatan ya ce, “To, zo mu haye zuwa wajen mutanen, mu sa su gan mu.
UJonathani wasesithi: Khangela, sizachaphela kulabobantu sizibonakalise kibo.
9 In suka ce mana, ‘Ku tsaya nan har mu zo wurinku,’ za mu dakata inda muke, ba za mu haura wajensu ba.
Uba bekhuluma njalo kithi besithi: Manini mpo, size sifike kini; sizakuma-ke endaweni yethu, singenyukeli kibo.
10 Amma in suka ce mana, ‘Ku haura wurinmu,’ to, sai mu haura, wannan zai zama mana alama cewa Ubangiji ya bashe su a hannunmu.”
Kodwa uba bekhuluma njalo kithi besithi: Yenyukelani kithi; sizakwenyuka-ke, ngoba iNkosi ibanikele esandleni sethu; lalokhu kuzakuba yisibonakaliso kithi.
11 Sai suka nuna kansu a sansanin Filistiyawa. Sai Filistiyawa suka ce, “Ku duba ga Ibraniyawa suna fitowa daga cikin ramummuka inda suka ɓuya.”
Ngakho bobabili bazibonakalisa ebuthweni lenqaba yamaFilisti; amaFilisti asesithi: Khangelani, amaHebheru asephuma emilindini abecatshe kiyo.
12 Mutanen da suke sansanin suka kira Yonatan da mai ɗaukan makamansa da babbar murya suka ce, “Ku hauro wajenmu, mu kuwa za mu koya muku hankali.” Sai Yonatan ya ce wa mai ɗaukan makamansa, “Biyo ni, gama Ubangiji ya bashe su a hannun Isra’ila.”
Amadoda ebutho lenqaba asephendula oJonathani lomthwali wezikhali zakhe athi: Yenyukelani kithi, sizalitshengisa ulutho. UJonathani wasesithi kumthwali wezikhali zakhe: Yenyuka ungilandele, ngoba iNkosi iwanikele esandleni sikaIsrayeli.
13 Sai Yonatan ya hau dutsen da rarrafe, mai ɗaukan makamansa kuwa yana biye. Yonatan ya yi ta fyaɗa Filistiyawa da ƙasa, mai ɗaukan makamansa kuma ya yi ta karkashe su.
UJonathani wasekhwela ngezandla zakhe langenyawo zakhe, lomthwali wezikhali zakhe emva kwakhe. Asesiwa phambi kukaJonathani, lomthwali wezikhali zakhe wawabulala emva kwakhe.
14 A wannan karo na farko Yonatan da mai ɗaukan makamansa suka kashe mutum wajen ashirin a wani fili mai fāɗi rabin kadada.
Ukutshaya kokuqala atshaya ngakho uJonathani lomthwali wezikhali zakhe kwakungaba phose ngamadoda angamatshumi amabili, ensimini elingana lengxenye yendima yesipani.
15 Sai tsoro ya kama dukan sojojin Filistiyawa, waɗanda suke cikin sansanin da waɗanda suke fili, har da waɗanda suke waje, da kuma waɗanda suke kai hari, ƙasa ta girgiza. Allah ne ya kawo wannan rikicewa.
Kwasekusiba khona ukuthuthumela enkambeni, egangeni, laphakathi kwabantu bonke; ibutho lenqaba labachithi labo bathuthumela, lomhlaba wanyikinyeka, kwasekusiba yikuthuthumela okukhulu.
16 Masu gadin Shawulu a Gebiya da take a Benyamin suka duba sai ga rundunar Filistiyawa a warwatsewa ko’ina.
Abalindi bakaSawuli eGibeya yakoBhenjamini basebebona ukuthi, khangela, ixuku lancibilika lihamba litshayelana phansi.
17 Sai Shawulu ya ce wa mutanen da suke tare da shi, “Ku ƙidaya mayaƙa ku ga wane ne ba ya nan.” Da suka ƙirga sai suka tarar Yonatan da mai ɗaukan makamansa ba sa nan.
USawuli wasesithi ebantwini ababelaye: Ake libale, libone ukuthi ngubani osuke kithi. Kwathi sebebalile, khangela, uJonathani lomthwali wezikhali zakhe babengekho.
18 Shawulu ya ce wa Ahiya, “Kawo akwatin alkawarin Allah.” (A lokacin akwatin alkawarin yana tare da Isra’ilawa.)
USawuli wasesithi kuAhiya: Letha lapha umtshokotsho kaNkulunkulu. Ngoba umtshokotsho kaNkulunkulu ngalolosuku wawukubantwana bakoIsrayeli.
19 Yayinda Shawulu yake magana da firist kuwa, harguwa ya yi ta ƙaruwa a sansanin Filistiyawa. Sai Shawulu ya ce wa firist, “Janye hannunka.”
Kwasekusithi uSawuli esakhuluma lompristi, umsindo owawusenkambeni yamaFilisti waqhubeka wanda. USawuli wasesithi kumpristi: Buyisela isandla sakho.
20 Sa’an nan Shawulu da dukan mutanensa suka taru suka tafi yaƙi. Suka tarar Filistiyawa sun ruɗe suna yaƙi da juna da takubansu.
USawuli labo bonke abantu ababelaye basebebizelwa ndawonye bafika empini, khangela-ke, inkemba yalowo lalowo yayimelene lomakhelwane wakhe, isiyaluyalu esikhulu kakhulu.
21 Ibraniyawan da suke tare da Filistiyawa a dā, waɗanda suka bi Filistiyawan zuwa sansanin yaƙinsu, suka juya, suka goyi bayan Shawulu da Yonatan sa’ad da yaƙin ya taso.
LamaHebheru ayelamaFilisti njengakuqala, enyukela lawo enkambeni inhlangothi zonke, ngitsho lawo aphenduka ukuthi abe loIsrayeli owayeloSawuli loJonathani.
22 Sa’ad da dukan Isra’ilawan da suka ɓuya a duwatsu a ƙasar Efraim suka ji labari cewa Filistiyawa suna gudu, sai suka fito suka fafare su.
Kwathi amadoda wonke akoIsrayeli ayecatshe entabeni yakoEfrayimi esezwile ukuthi amaFilisti ayabaleka, ngitsho lawo awanamathela ewalandela empini.
23 Haka Ubangiji ya kuɓutar da Isra’ila a wannan rana. Yaƙin kuwa ya ci gaba har gaba da Bet-Awen.
Ngokunjalo iNkosi yamsindisa uIsrayeli ngalolosuku; lempi yedlulela eBeti-Aveni.
24 A wannan rana, Isra’ilawa suka sha wahala ƙwarai domin Shawulu ya sa mutane suka yi rantsuwa cewa, “La’ananne ne mutumin da ya ci abinci kafin fāɗuwar rana, kafin in ɗauki fansa a kan abokan gābana.” Don haka ba mutumin da ya ɗanɗana abinci.
Amadoda akoIsrayeli asekhathala ngalolosuku, ngoba uSawuli wafungisa abantu esithi: Kaqalekiswe umuntu odla ukudla kuze kube ntambama, ukuze ngiziphindiselele ezitheni zami. Ngakho kakho ebantwini owanambitha ukudla.
25 Dukan rundunar ta shiga kurmi, sai ga zuma a ƙasa.
Bonke abelizwe basebefika ehlathini; njalo kwakuloluju phezu kobuso bomhlabathi.
26 Da suka shiga ciki kurmin, suka ga zuma tana zubowa, duk da haka ba wanda ya sa yatsansa ya lasa saboda tsoron rantsuwar da suka yi.
Lapho abantu bengena ehlathini, khangela, uluju lwathonta; kodwa kakho loyedwa owasa isandla sakhe emlonyeni wakhe, ngoba abantu besaba isifungo.
27 Yonatan bai san cewa mahaifinsa ya sa mutane suka yi rantsuwa ba. Sai ya sa gindin sandan da yake hannunsa a saƙar zuma, ya kai bakinsa. Nan da nan sai ya ji ƙarfin jiki ya zo masa.
Kodwa uJonathani wayengezwanga lapho uyise efungisa abantu; ngakho welula isihloko somqwayi owawusesandleni sakhe, wasigxamuza ehlangeni lwenyosi, wasesisa isandla sakhe emlonyeni wakhe, lamehlo akhe aqaqabuka.
28 Sai wani soja ya gaya masa cewa, “Mahaifinka ya sa kowa ya yi rantsuwa cewa, ‘La’ananne ne mutumin da ya ci abinci kafin fāɗuwar rana!’ Shi ya sa duk sojojin ba su da ƙarfi.”
Omunye wabantu wasephendula wathi: Uyihlo ubafungisile lokubafungisa abantu esithi: Uqalekisiwe umuntu odla ukudla lamuhla. Abantu basebephele amandla.
29 Yonatan ya ce, “Mahaifina ya jefa ƙasar cikin matsala. Duba yadda na ji ƙarfin jiki sa’ad da na ɗanɗana wannan’yar zuma mana.
UJonathani wasesithi: Ubaba ulihluphile ilizwe; ake libone ukuthi amehlo ami aseqaqabuke njani, ngoba nginambithe ingcosana yaloluluju.
30 Da yaya zai kasance ke nan da a ce an bar sojoji suka ci abincin da suka ƙwace daga abokan gābansu? Ai, da gawawwakin Filistiyawan da aka kashe sun fi haka.”
Kudlula kangakanani aluba abantu bebedlile lokudla lamuhla okwempango yezitha zabo abayitholayo? Ngoba khathesi ukubulala kakubanga kukhulu phakathi kwamaFilisti.
31 A ranan nan Isra’ilawa suka yi ta kashe Filistiyawa daga Mikmash har zuwa Aiyalon. Bayan haka gajiya ta kama su sosai saboda yunwa.
Basebetshaya amaFilisti ngalolosuku kusukela eMikimashi kuze kube seAjaloni. Abantu basebephele amandla kakhulu.
32 Sai suka yi warwason ganima, suka kwashe tumaki, da shanu, da maruƙa, suka yayyanka su, suka ci naman ɗanye.
Abantu basebetheleka empangweni; bathatha izimvu, lezinkabi, lamathole enkomo, bakuhlabela emhlabathini; abantu bakudla kanye legazi.
33 Sai wani mutum ya ce wa Shawulu, “Duba, ga mutane suna zunubi ga Ubangiji, suna cin nama da jini.” Shawulu ya ce, “Kun ci amana. Ku mirgino babban dutse zuwa wurina nan da nan.”
Basebemtshela uSawuli besithi: Khangela, abantu bayona eNkosini ngokudla kanye legazi. Wasesithi: Lenze ngokungathembeki; giqelani kimi ilitshe elikhulu lamuhla.
34 Sa’an nan ya ce, “Ku tafi ku faɗa wa jama’a duka, su kawo shanu da tumaki a nan, su yayyanka, su ci a nan, don kada su yi wa Ubangiji zunubi da cin nama ɗanye.” Haka nan kowa ya kawo saniyarsa a daren, ya yanka a can.
USawuli wasesithi: Zihlakazeni phakathi kwabantu lithi kibo: Sondezani kimi, ngulowo lalowo inkabi yakhe, langulowo lalowo imvu yakhe, lizihlabele lapha, lidle; njalo lingoni eNkosini ngokudla kanye legazi. Ngakho bonke abantu basondeza, ngulowo lalowo inkabi yakhe ngesandla sakhe ngalobobusuku, bazihlaba khona.
35 Sa’an nan Shawulu ya gina wa Ubangiji bagade. Wannan ne bagade na farkon da ya gina.
USawuli waseyakhela iNkosi ilathi; kwakulilathi lokuqala alakhela iNkosi.
36 Shawulu ya ce, “Mu bi gangara mu fafare Filistiyawa da dare mu washe su har gari yă waye, mu kuma karkashe kowannensu, kada mu bar wani da rai.” Suka ce, “Ka yi duk abin da ka ga ya fi maka kyau.” Amma firist ya ce, “Bari mu nemi nufin Allah tukuna.”
USawuli wasesithi: Asehleni silandele amaFilisti ebusuku, siwaphange kuze kube yikukhanya kokusa, singatshiyi lamuntu kiwo. Basebesithi: Yenza konke okuhle emehlweni akho. Kodwa umpristi wathi: Asisondeleni lapha kuNkulunkulu.
37 Saboda haka Shawulu ya tambayi Allah ya ce, “Mu bi bayan Filistiyawa? Za ka bashe su a hannun Isra’ila?” Amma Allah bai ba shi amsa a ranar ba.
USawuli wasebuza kuNkulunkulu wathi: Ngehle ngilandele amaFilisti yini? Uzawanikela esandleni sikaIsrayeli yini? Kodwa kamphendulanga ngalolosuku.
38 Saboda haka Shawulu ya ce, “Ku zo nan dukanku shugabannin rundunoni, mu bincika mu san zunubin da ya kawo rashin amsan nan yau.
USawuli wasesithi: Sondelani lapha lonke bakhokheli babantu, lazi libone ukuthi lesisono sikukuphi lamuhla.
39 Muddin Ubangiji wanda ya ceci Isra’ila yana raye, ko da ɗana Yonatan ne ya yi zunubin, dole yă mutu.” Amma ba ko ɗaya daga cikinsu da ya ce uffam.
Ngoba kuphila kukaJehova owasindisa uIsrayeli, lanxa kungaba kuJonathani indodana yami, isibili uzakufa lokufa. Kodwa kakho loyedwa owamphendulayo ebantwini bonke.
40 Sai Shawulu ya ce wa dukan Isra’ilawa, “Ku tsaya a can, ni kuma da Yonatan ɗana mu tsaya a nan.” Mutanen suka ce, “Ka yi abin da ya fi maka kyau.”
Wasesithi kuIsrayeli wonke: Banini nganxanye lina, mina-ke loJonathani indodana yami sizakuba nganxanye. Abantu basebesithi kuSawuli: Yenza okuhle emehlweni akho.
41 Sa’an nan Shawulu ya yi addu’a ga Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, “Me ya sa ba ka amsa mini addu’ata a yau ba? Idan wannan laifina ne, ko kuwa na ɗana, Yonatan, ka nuna mana ta wurin Urim, amma idan laifin mutanen ne ka amsa ta wurin Tummim.” Ba a sami mutane da laifi ba, amma ƙuri’a ta fāɗa a kan Yonatan da Shawulu.
Ngakho uSawuli wathi eNkosini uNkulunkulu kaIsrayeli: Phana opheleleyo. UJonathani loSawuli basebebanjwa, kodwa abantu baphunyuka.
42 Shawulu ya ce, “Ku jefa ƙuri’a tsakanina da ɗana Yonatan.” Sai ƙuri’ar ta fāɗa a kan Yonatan.
USawuli wasesithi: Yenzani inkatho yokuphosa phakathi kwami loJonathani indodana yami. UJonathani wasebanjwa.
43 Sai Shawulu ya ce wa Yonatan, “Gaya mini mene ne ka yi.” Yonatan ya ce masa, “Na ɗanɗana zuma kaɗan daga gindin sandanta. Yanzu kuwa dole in mutu!”
USawuli wasesithi kuJonathani: Ngitshela okwenzileyo. UJonathani wasemtshela wathi: Oqotho nginambithe ngesihloko somqwayi obusesandleni sami imbijana yoluju; khangela ngilapha, sengizakufa!
44 Shawulu ya ce, “Bari hukunci mai tsanani na Allah yă kasance a kaina, in ba ka mutu ba, Yonatan.”
USawuli wasesithi: UNkulunkulu kenze njalo langokunjalo engezelele; ngoba uzakufa lokufa, Jonathani.
45 Amma mutane suka ce wa Shawulu, “A ce Yonatan yă mutu bayan shi ya kawo babban nasara a Isra’ila? Faufau, muddin Ubangiji yana raye, ko gashin kansa ɗaya ba zai fāɗi a ƙasa ba, gama abin da ya yi yau, Allah ne yana tare da shi.” Ta haka mutane suka ceci Yonatan daga mutuwa.
Kodwa abantu bathi kuSawuli: Uzakufa yini uJonathani, owenze lolusindiso olukhulu koIsrayeli? Kakube khatshana! Kuphila kukaJehova, kakuyikuwela emhlabathini lolulodwa unwele lwekhanda lakhe, ngoba usebenze loNkulunkulu lamuhla. Ngakho abantu bamhlenga uJonathani ukuthi angafi.
46 Sai Shawulu ya daina bin Filistiyawa, suka koma ƙasarsu.
USawuli wasesenyuka esuka ekulandeleni amaFilisti; amaFilisti asesiya endaweni yawo.
47 Bayan Shawulu ya hau karagar mulkin Isra’ila, ya yi yaƙi da abokan gābansu ta kowane gefe. Mowabawa, Ammonawa, mutanen Edom, sarakunan Zoba, da kuma Filistiyawa. Duk wurin da ya juya, ya hore su.
USawuli wasethatha ubukhosi phezu kukaIsrayeli, walwa emelene lezitha zakhe zonke inhlangothi zonke, emelene loMowabi, njalo emelene labantwana bakoAmoni, njalo emelene loEdoma, njalo emelene lamakhosi eZoba, njalo emelene lamaFilisti; laloba ngaphi lapho aphendukela khona wayejezisa.
48 Ya yi jaruntaka sosai, ya ci Amalekawa da yaƙi, ya kuma ceci Isra’ila daga hannuwan waɗanda suka ƙwace musu kaya.
Wenza ngobuqhawe wasetshaya amaAmaleki, wakhulula uIsrayeli esandleni somphangi wakhe.
49 ’Ya’yan Shawulu maza su ne, Yonatan, Ishbi, da Malki-Shuwa. Sunan babban’yarsa ita ce Merab, ƙaramar kuma Mikal.
Lamadodana kaSawuli ayengoJonathani loIshivi, loMaliki-Shuwa; lamabizo amadodakazi akhe amabili yila: Ibizo lezibulo lalinguMerabi, lebizo lencinyane linguMikhali.
50 Sunan matarsa kuwa Ahinowam,’yar Ahimawaz. Sunan shugaban ƙungiyar sojan Shawulu kuwa Abner ne ɗan Ner, shi Ner kuwa ɗan’uwan mahaifin Shawulu ne.
Lebizo lomkaSawuli lalinguAhinowama indodakazi kaAhimahazi; lebizo lenduna yebutho lakhe lalinguAbhineri indodana kaNeri, uyise omncinyane kaSawuli.
51 Mahaifin Shawulu, Kish da kuma Ner mahaifin Abner,’ya’yan Abiyel ne.
Njalo uKishi wayenguyise kaSawuli, loNeri uyise kaAbhineri wayeyindodana kaAbiyeli.
52 Dukan kwanakin Shawulu sun kasance na yaƙe-yaƙe da Filistiyawa ne. Duk lokacin da Shawulu ya ga ƙaƙƙarfan mutum ko jarumi, sai yă ɗauke shi aikin sojansa.
Njalo kwakukhona impi enzima lamaFilisti zonke izinsuku zikaSawuli; lapho uSawuli ebona indoda elamandla loba iqhawe, wayezibuthela yona.