< 1 Sama’ila 14 >

1 Wata rana Yonatan ɗan Shawulu ya ce wa saurayin da yake ɗaukar masa makamai, “Zo mu tafi wajen sansanin Filistiyawa a wancan hayi.” Amma bai gaya wa mahaifinsa ba.
A I kekahi la, olelo aku la o Ionatana ke keiki a Saula ike kanaka ui, nana i hali kana mea kaua, Ea, e hele kaua i ka pakaua o ko Pilisetia ma kela aoao. Aka, aole ia i hai aku i kona makuakane.
2 Shawulu kuwa na zaune a gindin itacen rumman a bayan garin Gibeya a Migron. Tare da shi akwai mutum wajen ɗari shida.
Noho iho la o Saula ma ka aoao mamao loa o Gibea, malalo o ka laau pomegerane ma Migerona: a o na Kanaka me ia, aono paha haneri lakou;
3 A cikinsu akwai Ahiya sanye da efod. Shi yaron Ikabod ɗan’uwan Ahitub ne, ɗan Finehas, ɗan Eli, firist na Ubangiji a Shilo. Ba wanda ya san cewa Yonatan ya tafi wani wuri.
A o Ahia, ke keiki a Ahituba, a ke kaikuaana o Ikaboda, ke keiki a Pinehasa, ke keiki a Eli, ke kahuna a Iehova ma Silo, ua hookomoia ka epoda. Aole i ike na kanaka, ua hala o Ionatana.
4 A kowane gefe na mashigin da Yonatan ya so yă bi zuwa wurin Filistiyawa, akwai hawa mai tsawo, ana kira ɗaya Bozez, ɗayan kuma ana kira Senet.
A ma ke ala a Ionatana i imi ai e hele i ka poe koa o ko Pilisetia, he pohaku oi ma keia aoao, a he pohaku oi ma kela aoao: o Bozeza ka inoa o kekahi, a o Sene ka inoa o kekahi.
5 Hawan da yake arewa yana fuskantar Mikmash, wanda yake kudu kuma yana fuskantar Geba.
A o ka mea oi o kekahi, ua kiekie ia ma ke kukuluakau e ku pono ana i Mikemasa, a o kekahi ma ke kukuluhema e ku pono ana i Gibea.
6 Yonatan ya ce wa saurayin mai ɗaukan makamai, “Zo mu haye zuwa mashigin mutane marasa kaciyan nan, wataƙila Ubangiji zai yi aiki a madadinmu. Ba abin da zai iya hana Ubangiji yin aikin ceto ta wurin mutane masu yawa, ko ta wurin mutane kaɗan.”
Olelo aku la o Ionatana i ke kanaka ui, nana i hali kana mea kaua, Ea, e hele kaua i kahi paa o ua poe la i okipoepoe ole ia: e hana mai paha o Iehova no kaua; no ka mea, aohe mea keakea ia Iehova, ke hoola ma ka poe nui, a ma ka poe uuku.
7 Mai ɗaukan makaman ya ce, “Ka yi duk abin da yake zuciyarka. Ci gaba, ina tare da kai gaba da baya.”
I mai la ka mea nana i hali kana mea kaua ia ia, E hana oe i ka mea a pau maloko o kou naau: o hele; aia hoi, owau pu kekahi me oe e like me kou manao.
8 Yonatan ya ce, “To, zo mu haye zuwa wajen mutanen, mu sa su gan mu.
Olelo aku la o Ionatana, Aia hoi, e hele kaua i ua poe kanaka la, a e hoike ia kaua iho ia lakou.
9 In suka ce mana, ‘Ku tsaya nan har mu zo wurinku,’ za mu dakata inda muke, ba za mu haura wajensu ba.
Ina e olelo mai lakou ia kaua peneia, E noho malie olua a hiki aku makou io olua la; alaila ku malie kaua ma ko kaua wahi, aole e pii aku io lakou la.
10 Amma in suka ce mana, ‘Ku haura wurinmu,’ to, sai mu haura, wannan zai zama mana alama cewa Ubangiji ya bashe su a hannunmu.”
Aka, i olelo mai lakou ia kaua peneia, E pii mai olua io makou nei; alaila e pii aku kaua: no ka mea, ua hoolilo mai o Iehova ia lakou i ko kaua lima; a oia ka hoailona no kaua.
11 Sai suka nuna kansu a sansanin Filistiyawa. Sai Filistiyawa suka ce, “Ku duba ga Ibraniyawa suna fitowa daga cikin ramummuka inda suka ɓuya.”
Hoike aku la laua ia laua iho i ka poe koa o ko Pilisetia: i ae la ko Pilisetia, E nana i ka poe Hebera e hele mai ana mailoko mai o na lua a lakou i pee ai.
12 Mutanen da suke sansanin suka kira Yonatan da mai ɗaukan makamansa da babbar murya suka ce, “Ku hauro wajenmu, mu kuwa za mu koya muku hankali.” Sai Yonatan ya ce wa mai ɗaukan makamansa, “Biyo ni, gama Ubangiji ya bashe su a hannun Isra’ila.”
Olelo mai la na kanaka o ka poe koa ia Ionatana, a me ka mea nana i hali kana mea kaua, i mai la, E pii mai olua io makou nei, a e hoike aku makou ia olua i kekahi mea. I aku la Ionatana i ka mea nana i hali kana mea kaua, E pii mai oe mahope o'u; no ka mea, ua hoolilo mai o Iehova ia lakou iloko o ka lima o ka Iseraela.
13 Sai Yonatan ya hau dutsen da rarrafe, mai ɗaukan makamansa kuwa yana biye. Yonatan ya yi ta fyaɗa Filistiyawa da ƙasa, mai ɗaukan makamansa kuma ya yi ta karkashe su.
Pii ae la o Ionatana ma kona lima, a ma kona wawae, a o ka mea nana i hali kana mea kaua mahope ona: a haule lakou imua o Ionatana; a o ka mea nana i hali kana mea kaua pepehi aku la ia mahope ona.
14 A wannan karo na farko Yonatan da mai ɗaukan makamansa suka kashe mutum wajen ashirin a wani fili mai fāɗi rabin kadada.
A o ka pepehi mua ana a Ionatana a me ka mea nana i hali kana mea kaua, he iwakalua paha kanaka ia, ma kahi kokoke, e like paha me ka hapalua o ka eka aina hookahi.
15 Sai tsoro ya kama dukan sojojin Filistiyawa, waɗanda suke cikin sansanin da waɗanda suke fili, har da waɗanda suke waje, da kuma waɗanda suke kai hari, ƙasa ta girgiza. Allah ne ya kawo wannan rikicewa.
He haalulu iwaena o ka poe koa ma ke kula, a iwaena o na kanaka a pau; a o ka poe kaua, a o ka poe luku, haalulu iho la lakou, nauwe ka aina; a he haalulu nui.
16 Masu gadin Shawulu a Gebiya da take a Benyamin suka duba sai ga rundunar Filistiyawa a warwatsewa ko’ina.
Nana aku la ka poe kiai o Saula ma Gibea o Beniamina; aia hoi, ua hee aku la ka poe nui, a holo lakou, a hele liilii aku.
17 Sai Shawulu ya ce wa mutanen da suke tare da shi, “Ku ƙidaya mayaƙa ku ga wane ne ba ya nan.” Da suka ƙirga sai suka tarar Yonatan da mai ɗaukan makamansa ba sa nan.
Olelo aku la o Saula i na kanaka me ia, E helu ano, i ike kakou i ka mea i hele ae mai o kakou aku. Helu aku la lakou, aia hoi, aole o Ionatana, a me ka mea nana i hali kana mea kaua.
18 Shawulu ya ce wa Ahiya, “Kawo akwatin alkawarin Allah.” (A lokacin akwatin alkawarin yana tare da Isra’ilawa.)
I aku la o Saula ia Ahia, E lawe mai maanei i ka pahu o ke Akua: no ka mea, i kela manawa, aia no ka pahu o ke Akua me na mamo a Iseraela.
19 Yayinda Shawulu yake magana da firist kuwa, harguwa ya yi ta ƙaruwa a sansanin Filistiyawa. Sai Shawulu ya ce wa firist, “Janye hannunka.”
A ia Saula i kamailio ai me ke kahuna, ua nui loa ka haunaele iwaena o ka poe koa o ko Pilisetia; i aku la o Saula i ke kahuna, E hoi hou mai i kou lima.
20 Sa’an nan Shawulu da dukan mutanensa suka taru suka tafi yaƙi. Suka tarar Filistiyawa sun ruɗe suna yaƙi da juna da takubansu.
Houluuluia'e la o Saula me na kanaka a pau me ia, a hele aku i ke kaua: aia hoi, ua ku e ka pahikaua a kela kanaka keia kanaka i kona hoa, a ua nui loa ka pioloke.
21 Ibraniyawan da suke tare da Filistiyawa a dā, waɗanda suka bi Filistiyawan zuwa sansanin yaƙinsu, suka juya, suka goyi bayan Shawulu da Yonatan sa’ad da yaƙin ya taso.
A o ka poe Hebera i noho ai me ko Pilisetia mamua, a i hele pu ai me lakou i kahi hoomoana'i, mai kela wahi keia wahi, o lakou kekahi i hui pu ai me ka Iseraela me Saula a me Ionatana.
22 Sa’ad da dukan Isra’ilawan da suka ɓuya a duwatsu a ƙasar Efraim suka ji labari cewa Filistiyawa suna gudu, sai suka fito suka fafare su.
A o na kanaka a pau o ka Iseraela i pee ai ma ka mauna o Eperaima, ia lakou i lohe ai, ua holo ko Pilisetia, o lakou no hoi kekahi i hahai mahope o lakou i ke kaua.
23 Haka Ubangiji ya kuɓutar da Isra’ila a wannan rana. Yaƙin kuwa ya ci gaba har gaba da Bet-Awen.
A hoopakele mai o Iehova i ka Iseraela ia la: a hele aku la ke kaua ma Betavena.
24 A wannan rana, Isra’ilawa suka sha wahala ƙwarai domin Shawulu ya sa mutane suka yi rantsuwa cewa, “La’ananne ne mutumin da ya ci abinci kafin fāɗuwar rana, kafin in ɗauki fansa a kan abokan gābana.” Don haka ba mutumin da ya ɗanɗana abinci.
A ua pilikia na kanaka o ka Iseraela ia la: no ka mea, ua hoohiki aku o Saula i na kauaka, i aku la, Poino ke kanaka, ke ai ia i ka ai a hiki i ke ahiahi, i hoopai aku ai au i ko'u poe enemi. Nolaila, aole i ai na kanaka i ka ai.
25 Dukan rundunar ta shiga kurmi, sai ga zuma a ƙasa.
A hele na kanaka a pau ma ka ululaau; a he meli maluna o ka aina.
26 Da suka shiga ciki kurmin, suka ga zuma tana zubowa, duk da haka ba wanda ya sa yatsansa ya lasa saboda tsoron rantsuwar da suka yi.
A hiki na kanaka ma ka ululaau, aia hoi, e kahe ana o ka meli, aole ka lima o kekahi kanaka i hoopa aku i kona waha: no ka mea, makau na kanaka i ka hoohiki ana.
27 Yonatan bai san cewa mahaifinsa ya sa mutane suka yi rantsuwa ba. Sai ya sa gindin sandan da yake hannunsa a saƙar zuma, ya kai bakinsa. Nan da nan sai ya ji ƙarfin jiki ya zo masa.
Aka, aole i lohe o Ionatana i ke kauoha a kona makuakane i na kanaka i ka hoohiki ana; nolaila, o aku la ia i ke kookoo ma kona lima, a hou iho la iloko o ka waihona meli, a hoopa kona lima i kona waha, a hoomalamalamaia kona mau maka.
28 Sai wani soja ya gaya masa cewa, “Mahaifinka ya sa kowa ya yi rantsuwa cewa, ‘La’ananne ne mutumin da ya ci abinci kafin fāɗuwar rana!’ Shi ya sa duk sojojin ba su da ƙarfi.”
Alaila, olelo mai la kekahi o na kanaka, i mai la, Ua kauoha ikaika mai kou makuakane i na kanaka me ka hoohiki, i mai la, Poino ke kanaka, ke ai i ka ai i keia la. A ua nawaliwali na kanaka.
29 Yonatan ya ce, “Mahaifina ya jefa ƙasar cikin matsala. Duba yadda na ji ƙarfin jiki sa’ad da na ɗanɗana wannan’yar zuma mana.
Olelo aku la o Ionatana, i aku la, Ua hoopilikia ko'u makuakane i ka aina: ke noi aku nei au ia oukou, e nana, ua hoomalamalamaia ko'u mau maka, no kuu hoao ana i kauwahi uuku o keia meli.
30 Da yaya zai kasance ke nan da a ce an bar sojoji suka ci abincin da suka ƙwace daga abokan gābansu? Ai, da gawawwakin Filistiyawan da aka kashe sun fi haka.”
Aole anei he nui aku, ina paha ua ai nui na kanaka i keia la i ka mea o ko lakou poe enemi i loaa ai ia lakou? Aole anei he nui aku ka luku iwaena o ko Pilisetia?
31 A ranan nan Isra’ilawa suka yi ta kashe Filistiyawa daga Mikmash har zuwa Aiyalon. Bayan haka gajiya ta kama su sosai saboda yunwa.
A luku aku la lakou i ko Pilisetia ia la, mai Mikemasa a hiki i Aialona: a ua nawaliwali loa na kanaka.
32 Sai suka yi warwason ganima, suka kwashe tumaki, da shanu, da maruƙa, suka yayyanka su, suka ci naman ɗanye.
Lalau aku la na kanaka i ka waiwai pio, a lawe i na hipa, a me na bipi, a me na bipikeiki, a pepehi iho la ma ka aina; a ai iho la na kanaka me ke koko.
33 Sai wani mutum ya ce wa Shawulu, “Duba, ga mutane suna zunubi ga Ubangiji, suna cin nama da jini.” Shawulu ya ce, “Kun ci amana. Ku mirgino babban dutse zuwa wurina nan da nan.”
Hai aku la lakou ia Saula, i aku la, Aia hoi, ke hana hewa nei na kanaka ia Iehova, i ka lakou ai ana me ke koko. I mai la kela, Ua hana pono ole oukou: e olokaa mai i pohaku nui io'u nei i keia la.
34 Sa’an nan ya ce, “Ku tafi ku faɗa wa jama’a duka, su kawo shanu da tumaki a nan, su yayyanka, su ci a nan, don kada su yi wa Ubangiji zunubi da cin nama ɗanye.” Haka nan kowa ya kawo saniyarsa a daren, ya yanka a can.
Olelo aku la o Saula, E hele oukou iwaena o na kanaka, e i aku ia lakou, E lawe mai io'u nei kela kanaka keia kanaka i kana bipi a me kana hipa, a e pepehi maanei, a ai iho; a mai hana hewa ia Iehova i ka ai ana me ke koko. A lawe mai la na kanaka a pau, o kela kanaka keia kanaka i kana bipi, me ia ia po, a pepehi iho la malaila.
35 Sa’an nan Shawulu ya gina wa Ubangiji bagade. Wannan ne bagade na farkon da ya gina.
Hana aku la o Saula i kuahu no Iehova, oia ke kuahu ana i hoomaka ai e hana no Iehova.
36 Shawulu ya ce, “Mu bi gangara mu fafare Filistiyawa da dare mu washe su har gari yă waye, mu kuma karkashe kowannensu, kada mu bar wani da rai.” Suka ce, “Ka yi duk abin da ka ga ya fi maka kyau.” Amma firist ya ce, “Bari mu nemi nufin Allah tukuna.”
I aku la o Saula, E hahai aku kakou i ko Pilisetia i ka po, a e luku aku ia lakou a hiki i ka malamalama o ke ao, a mai waiho kakou i kekahi kauaka o lakou. I mai la lakou, E hana oe i ka mea pono i kou maka. I mai la ke kahuna, E hookoke mai nei kakou i ke Akua.
37 Saboda haka Shawulu ya tambayi Allah ya ce, “Mu bi bayan Filistiyawa? Za ka bashe su a hannun Isra’ila?” Amma Allah bai ba shi amsa a ranar ba.
Ninau aku la o Saula i ke Akua, E hahai aku anei au i ko Pilisetia? e hoolilo mai anei oe ia lakou i ka lima o ka Iseraela? Aka, aole ia i olelo mai ia ia ia la.
38 Saboda haka Shawulu ya ce, “Ku zo nan dukanku shugabannin rundunoni, mu bincika mu san zunubin da ya kawo rashin amsan nan yau.
Olelo aku la o Saula, E hookokoke mai oukou ia nei, e na alakai o na kanaka; i ike pono kakou i ka mea o keia hewa i keia la.
39 Muddin Ubangiji wanda ya ceci Isra’ila yana raye, ko da ɗana Yonatan ne ya yi zunubin, dole yă mutu.” Amma ba ko ɗaya daga cikinsu da ya ce uffam.
No ka mea, ma ke ola o Iehova nana i hoola i ka Iseraela, ina paha iloko o Ionatana ka'u keiki keia mea, e make io no ia. Aole kekahi kanaka iwaena o ka Iseraela i olelo mai ia ia.
40 Sai Shawulu ya ce wa dukan Isra’ilawa, “Ku tsaya a can, ni kuma da Yonatan ɗana mu tsaya a nan.” Mutanen suka ce, “Ka yi abin da ya fi maka kyau.”
Olelo aku la ia i ka Iseraela a pau, O oukou ma kekahi aoao, a owau a me Ionatana kuu keiki, ma kekahi aoao. I mai la na kanaka ia Saula, E hana oe i ka mea pono i kou maka.
41 Sa’an nan Shawulu ya yi addu’a ga Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, “Me ya sa ba ka amsa mini addu’ata a yau ba? Idan wannan laifina ne, ko kuwa na ɗana, Yonatan, ka nuna mana ta wurin Urim, amma idan laifin mutanen ne ka amsa ta wurin Tummim.” Ba a sami mutane da laifi ba, amma ƙuri’a ta fāɗa a kan Yonatan da Shawulu.
Olelo aku la o Saula ia Iehova ke Akua o ka Iseraela, E hoike mai i ka oiaio. A ua laweia o Saula a me Ionatana: a pakele na kanaka.
42 Shawulu ya ce, “Ku jefa ƙuri’a tsakanina da ɗana Yonatan.” Sai ƙuri’ar ta fāɗa a kan Yonatan.
I aku la o Saula, E hailona iwaena o maua a me Ionatana kuu keiki. A ua laweia o Ionatana.
43 Sai Shawulu ya ce wa Yonatan, “Gaya mini mene ne ka yi.” Yonatan ya ce masa, “Na ɗanɗana zuma kaɗan daga gindin sandanta. Yanzu kuwa dole in mutu!”
Alaila i aku la o Saula ia Ionatana, E hai mai oe ia'u i kau mea i hana'i. Hai aku la o Ionatana, i aku la, Ua hoao iho au i kahi meli uuku wale no me ke kookoo ma kuu lima, aia hoi, e make ana au.
44 Shawulu ya ce, “Bari hukunci mai tsanani na Allah yă kasance a kaina, in ba ka mutu ba, Yonatan.”
I aku la o Saula, Pela ke Akua e hana mai ai, pela io hoi, no ka mea, e make io no oe, e Ionatana.
45 Amma mutane suka ce wa Shawulu, “A ce Yonatan yă mutu bayan shi ya kawo babban nasara a Isra’ila? Faufau, muddin Ubangiji yana raye, ko gashin kansa ɗaya ba zai fāɗi a ƙasa ba, gama abin da ya yi yau, Allah ne yana tare da shi.” Ta haka mutane suka ceci Yonatan daga mutuwa.
Olelo mai la na kanaka ia Saula, E make anei o Ionatana, nana i hana keia ola nui iwaena o ka Iseraela? Aole loa, ma ke ola o Iehova, aole e haule iho ma ka honua kekahi lauoho o kona poo; no ka mea, ua hana pu aku ia me ke Akua i keia la. A hoopakele aku la na kanaka ia Ionatana, aole ia i make.
46 Sai Shawulu ya daina bin Filistiyawa, suka koma ƙasarsu.
Haalele aku la o Saula i ka hahai ana i ko Pilisetia: a hoi aku la ko Pilisetia i ko lakou wahi.
47 Bayan Shawulu ya hau karagar mulkin Isra’ila, ya yi yaƙi da abokan gābansu ta kowane gefe. Mowabawa, Ammonawa, mutanen Edom, sarakunan Zoba, da kuma Filistiyawa. Duk wurin da ya juya, ya hore su.
A lawe ae la o Saula i ke aupuni o ka Iseraela, a kana aku la i kona poe enemi a pau, ma na aoao a pau i ko Moaba, a me na mamo a Amona, a me ka Edoma, a me na'lii o Zoba, a me ko Pilisetia, a ma na wahi a pau ana i huli ae, ua lanakila ia.
48 Ya yi jaruntaka sosai, ya ci Amalekawa da yaƙi, ya kuma ceci Isra’ila daga hannuwan waɗanda suka ƙwace musu kaya.
Hana ikaika aku la ia, a luku aku la i ka Ameleka, a hoopakele i ka Iseraela i ka lima o ka poe i luku mai ia lakou.
49 ’Ya’yan Shawulu maza su ne, Yonatan, Ishbi, da Malki-Shuwa. Sunan babban’yarsa ita ce Merab, ƙaramar kuma Mikal.
Eia na keiki a Saula, o Ionatana, o Isui a me Melekisua: a o ka inoa o kana mau kaikamahine elua, o Meraba ka inoa o ke kaikuaana, a o Mikala ka inoa o ke kaikaina.
50 Sunan matarsa kuwa Ahinowam,’yar Ahimawaz. Sunan shugaban ƙungiyar sojan Shawulu kuwa Abner ne ɗan Ner, shi Ner kuwa ɗan’uwan mahaifin Shawulu ne.
A o Ahinoama ka inoa o ka wahine a Saula, ke kaikamahine a Ahimaaza; a o ka inoa o kona alihikaua, o Abenera, ke keiki a Nera, kahi makua o Saula.
51 Mahaifin Shawulu, Kish da kuma Ner mahaifin Abner,’ya’yan Abiyel ne.
A o Kisa ka makuakane o Saula: a o Nera ka makuakane o Abenera, ke keiki a Abiela.
52 Dukan kwanakin Shawulu sun kasance na yaƙe-yaƙe da Filistiyawa ne. Duk lokacin da Shawulu ya ga ƙaƙƙarfan mutum ko jarumi, sai yă ɗauke shi aikin sojansa.
A ua nui ke kaua ana i ko Pilisetia i na la a pau o Saula: a ike aku la o Saula i ke kanaka ikaika, a i ke kanaka koaka, lawe aku la kela ia ia nona.

< 1 Sama’ila 14 >