< 1 Sama’ila 14 >

1 Wata rana Yonatan ɗan Shawulu ya ce wa saurayin da yake ɗaukar masa makamai, “Zo mu tafi wajen sansanin Filistiyawa a wancan hayi.” Amma bai gaya wa mahaifinsa ba.
Un jour, Jonathas, fils de Saül, dit au jeune homme qui portait ses armes: « Viens, et passons jusqu’au poste des Philistins, qui est là, de l’autre côté. » Et il n’en dit rien à son père.
2 Shawulu kuwa na zaune a gindin itacen rumman a bayan garin Gibeya a Migron. Tare da shi akwai mutum wajen ɗari shida.
— Saül se tenait à l’extrémité de Gabaa, sous le grenadier de Magron, et le peuple qui était avec lui était d’environ six cents hommes.
3 A cikinsu akwai Ahiya sanye da efod. Shi yaron Ikabod ɗan’uwan Ahitub ne, ɗan Finehas, ɗan Eli, firist na Ubangiji a Shilo. Ba wanda ya san cewa Yonatan ya tafi wani wuri.
Achias, fils d’Achitob, frère d’Ichabod, fils de Phinées, fils d’Héli, prêtre de Yahweh à Silo, portait l’éphod. Le peuple ne savait pas non plus que Jonathas s’en fût allé.
4 A kowane gefe na mashigin da Yonatan ya so yă bi zuwa wurin Filistiyawa, akwai hawa mai tsawo, ana kira ɗaya Bozez, ɗayan kuma ana kira Senet.
Entre les passages par lesquels Jonathas cherchait à arriver au poste des Philistins, il y avait une dent de rocher d’un côté et une dent de rocher de l’autre côté, l’une nommée Bosès, et l’autre nommée Séné.
5 Hawan da yake arewa yana fuskantar Mikmash, wanda yake kudu kuma yana fuskantar Geba.
L’une de ces dents se dresse au nord, vis-à-vis de Machmas, et l’autre au midi, vis-à-vis de Gabée. —
6 Yonatan ya ce wa saurayin mai ɗaukan makamai, “Zo mu haye zuwa mashigin mutane marasa kaciyan nan, wataƙila Ubangiji zai yi aiki a madadinmu. Ba abin da zai iya hana Ubangiji yin aikin ceto ta wurin mutane masu yawa, ko ta wurin mutane kaɗan.”
Jonathas dit donc au jeune homme qui portait ses armes: « Viens, et passons jusqu’au poste de ces incirconcis. Peut-être Yahweh agira-t-il pour nous; car rien n’empêche Yahweh de sauver, soit par un nombre grand, soit par un petit nombre. »
7 Mai ɗaukan makaman ya ce, “Ka yi duk abin da yake zuciyarka. Ci gaba, ina tare da kai gaba da baya.”
Son écuyer lui répondit: « Fais tout ce que tu as dans le cœur; va où tu voudras, me voici avec toi prêt à te suivre. »
8 Yonatan ya ce, “To, zo mu haye zuwa wajen mutanen, mu sa su gan mu.
Jonathas dit: « Voici, nous passerons vers ces hommes et nous nous montrerons vers eux.
9 In suka ce mana, ‘Ku tsaya nan har mu zo wurinku,’ za mu dakata inda muke, ba za mu haura wajensu ba.
S’ils nous disent: Arrêtez, jusqu’à ce que nous venions à vous! nous resterons en place et nous ne monterons pas vers eux.
10 Amma in suka ce mana, ‘Ku haura wurinmu,’ to, sai mu haura, wannan zai zama mana alama cewa Ubangiji ya bashe su a hannunmu.”
Mais s’ils disent: Montez vers nous! nous monterons, car Yahweh les a livrés entre nos mains. Cela sera pour nous le signe. »
11 Sai suka nuna kansu a sansanin Filistiyawa. Sai Filistiyawa suka ce, “Ku duba ga Ibraniyawa suna fitowa daga cikin ramummuka inda suka ɓuya.”
Ils se montrèrent tous deux au poste des Philistins, et les Philistins dirent: « Voici les Hébreux qui sortent des trous où ils s’étaient cachés. »
12 Mutanen da suke sansanin suka kira Yonatan da mai ɗaukan makamansa da babbar murya suka ce, “Ku hauro wajenmu, mu kuwa za mu koya muku hankali.” Sai Yonatan ya ce wa mai ɗaukan makamansa, “Biyo ni, gama Ubangiji ya bashe su a hannun Isra’ila.”
Et les hommes du poste, s’adressant à Jonathas et à son écuyer, dirent: « Montez vers nous, et nous vous ferons savoir quelque chose. » Et Jonathas dit à son écuyer: « Monte après moi, car Yahweh les a livrés entre nos mains. »
13 Sai Yonatan ya hau dutsen da rarrafe, mai ɗaukan makamansa kuwa yana biye. Yonatan ya yi ta fyaɗa Filistiyawa da ƙasa, mai ɗaukan makamansa kuma ya yi ta karkashe su.
Et Jonathas monta, sur les mains et sur les pieds, suivi de son écuyer. Les Philistins tombaient devant Jonathas, et son écuyer tuait derrière lui.
14 A wannan karo na farko Yonatan da mai ɗaukan makamansa suka kashe mutum wajen ashirin a wani fili mai fāɗi rabin kadada.
Ce premier massacre que firent Jonathas et son écuyer fut d’environ vingt hommes, sur la longueur d’un demi-sillon d’un arpent de terre.
15 Sai tsoro ya kama dukan sojojin Filistiyawa, waɗanda suke cikin sansanin da waɗanda suke fili, har da waɗanda suke waje, da kuma waɗanda suke kai hari, ƙasa ta girgiza. Allah ne ya kawo wannan rikicewa.
L’épouvante se répandit dans le camp des Philistins, dans la campagne et dans tout le peuple; le poste aussi et l’armée de destruction furent saisis de peur; la terre trembla: c’était une terreur de Dieu.
16 Masu gadin Shawulu a Gebiya da take a Benyamin suka duba sai ga rundunar Filistiyawa a warwatsewa ko’ina.
Les sentinelles de Saül qui étaient à Gabaa de Benjamin virent comment la multitude des Philistins se dispersait et allait de côté et d’autre.
17 Sai Shawulu ya ce wa mutanen da suke tare da shi, “Ku ƙidaya mayaƙa ku ga wane ne ba ya nan.” Da suka ƙirga sai suka tarar Yonatan da mai ɗaukan makamansa ba sa nan.
Saül dit au peuple qui était avec lui: « Faites la revue et voyez qui s’en est allé d’avec nous. » Ils firent la revue, et voici qu’il n’y avait ni Jonathas ni son écuyer.
18 Shawulu ya ce wa Ahiya, “Kawo akwatin alkawarin Allah.” (A lokacin akwatin alkawarin yana tare da Isra’ilawa.)
Et Saül dit à Achias: « Fais approcher l’arche de Dieu. » — Car l’arche de Dieu était en ce jour-là avec les enfants d’Israël. —
19 Yayinda Shawulu yake magana da firist kuwa, harguwa ya yi ta ƙaruwa a sansanin Filistiyawa. Sai Shawulu ya ce wa firist, “Janye hannunka.”
Pendant que Saül parlait au prêtre, le tumulte qui se faisait dans le camp des Philistins allait croissant; et Saül dit au prêtre: « Retire ta main. »
20 Sa’an nan Shawulu da dukan mutanensa suka taru suka tafi yaƙi. Suka tarar Filistiyawa sun ruɗe suna yaƙi da juna da takubansu.
Puis Saül et tout le peuple qui était avec lui, s’étant rassemblés, s’avancèrent jusqu’au lieu du combat, et voici que l’épée de l’un était tournée contre l’autre, et la confusion était extrême.
21 Ibraniyawan da suke tare da Filistiyawa a dā, waɗanda suka bi Filistiyawan zuwa sansanin yaƙinsu, suka juya, suka goyi bayan Shawulu da Yonatan sa’ad da yaƙin ya taso.
Les Hébreux qui étaient auparavant avec les Philistins, étant montés avec eux au camp tout autour, se mirent eux aussi du côté de ceux d’Israël qui étaient avec Saül et Jonathas.
22 Sa’ad da dukan Isra’ilawan da suka ɓuya a duwatsu a ƙasar Efraim suka ji labari cewa Filistiyawa suna gudu, sai suka fito suka fafare su.
Tous les hommes d’Israël qui s’étaient cachés dans la montagne d’Ephraïm, apprenant la fuite des Philistins, s’attachèrent également à les poursuivre en combattant.
23 Haka Ubangiji ya kuɓutar da Isra’ila a wannan rana. Yaƙin kuwa ya ci gaba har gaba da Bet-Awen.
C’est ainsi que Yahweh délivra Israël ce jour-là. Le combat se poursuivit jusqu’à Beth-Aven.
24 A wannan rana, Isra’ilawa suka sha wahala ƙwarai domin Shawulu ya sa mutane suka yi rantsuwa cewa, “La’ananne ne mutumin da ya ci abinci kafin fāɗuwar rana, kafin in ɗauki fansa a kan abokan gābana.” Don haka ba mutumin da ya ɗanɗana abinci.
Les hommes d’Israël étaient à bout de forces en ce jour-là. Saül fit jurer le peuple, en disant: « Maudit soit l’homme qui prendra de la nourriture jusqu’au soir, jusqu’à ce que je me sois vengé de mes ennemis! » Et personne ne goûta de nourriture.
25 Dukan rundunar ta shiga kurmi, sai ga zuma a ƙasa.
Tout le peuple vint dans la forêt, et il y avait du miel à la surface du sol.
26 Da suka shiga ciki kurmin, suka ga zuma tana zubowa, duk da haka ba wanda ya sa yatsansa ya lasa saboda tsoron rantsuwar da suka yi.
Et le peuple entra dans la forêt, il vit du miel qui coulait; mais nul ne porta la main à la bouche, car le peuple avait crainte du serment.
27 Yonatan bai san cewa mahaifinsa ya sa mutane suka yi rantsuwa ba. Sai ya sa gindin sandan da yake hannunsa a saƙar zuma, ya kai bakinsa. Nan da nan sai ya ji ƙarfin jiki ya zo masa.
Mais Jonathas n’avait pas entendu lorsque son père avait fait faire le serment au peuple; il avança l’extrémité du bâton qu’il avait à la main et, l’ayant plongé dans un rayon de miel, il ramena sa main à sa bouche, et ses yeux furent éclaircis.
28 Sai wani soja ya gaya masa cewa, “Mahaifinka ya sa kowa ya yi rantsuwa cewa, ‘La’ananne ne mutumin da ya ci abinci kafin fāɗuwar rana!’ Shi ya sa duk sojojin ba su da ƙarfi.”
Alors quelqu’un du peuple, prenant la parole, lui dit: « Ton père a fait jurer le peuple, en disant: Maudit soit l’homme qui prendra de la nourriture aujourd’hui! Et le peuple était épuisé. »
29 Yonatan ya ce, “Mahaifina ya jefa ƙasar cikin matsala. Duba yadda na ji ƙarfin jiki sa’ad da na ɗanɗana wannan’yar zuma mana.
Jonathas dit: « Mon père a causé le malheur du peuple. Voyez donc comme mes yeux sont clairs, parce que j’ai goûté un peu de ce miel!
30 Da yaya zai kasance ke nan da a ce an bar sojoji suka ci abincin da suka ƙwace daga abokan gābansu? Ai, da gawawwakin Filistiyawan da aka kashe sun fi haka.”
Ah! Si le peuple avait mangé aujourd’hui du butin trouvé chez ses ennemis, combien la défaite des Philistins n’aurait-elle pas été plus grande! »
31 A ranan nan Isra’ilawa suka yi ta kashe Filistiyawa daga Mikmash har zuwa Aiyalon. Bayan haka gajiya ta kama su sosai saboda yunwa.
Ils battirent ce jour-là les Philistins depuis Machmas jusqu’à Ajalon, et le peuple était tout défaillant.
32 Sai suka yi warwason ganima, suka kwashe tumaki, da shanu, da maruƙa, suka yayyanka su, suka ci naman ɗanye.
Le peuple se jeta sur le butin et, ayant pris des brebis, des bœufs et des veaux, il les égorgèrent sur la terre, et le peuple en mangea avec le sang.
33 Sai wani mutum ya ce wa Shawulu, “Duba, ga mutane suna zunubi ga Ubangiji, suna cin nama da jini.” Shawulu ya ce, “Kun ci amana. Ku mirgino babban dutse zuwa wurina nan da nan.”
On le rapporta à Saül, en disant: « Voici que le peuple pèche contre Yahweh, en mangeant la chair avec le sang. » Saül dit: « Vous avez commis une infidélité, roulez à l’instant vers moi une grande pierre. »
34 Sa’an nan ya ce, “Ku tafi ku faɗa wa jama’a duka, su kawo shanu da tumaki a nan, su yayyanka, su ci a nan, don kada su yi wa Ubangiji zunubi da cin nama ɗanye.” Haka nan kowa ya kawo saniyarsa a daren, ya yanka a can.
Et Saül dit: « Dispersez-vous parmi le peuple, et dites-leur: Amenez-moi chacun votre bœuf et chacun votre brebis; égorgez-les ici; vous en mangerez alors et vous ne pécherez pas contre Yahweh en mangeant avec le sang. » Et chacun parmi tout le peuple amena pendant la nuit son bœuf par la main, et l’égorgea là.
35 Sa’an nan Shawulu ya gina wa Ubangiji bagade. Wannan ne bagade na farkon da ya gina.
Saül bâtit un autel à Yahweh; ce fut le premier autel qu’il éleva pour Yahweh.
36 Shawulu ya ce, “Mu bi gangara mu fafare Filistiyawa da dare mu washe su har gari yă waye, mu kuma karkashe kowannensu, kada mu bar wani da rai.” Suka ce, “Ka yi duk abin da ka ga ya fi maka kyau.” Amma firist ya ce, “Bari mu nemi nufin Allah tukuna.”
Saül dit: « Descendons, pendant qu’il fait nuit, à la poursuite des Philistins, pillons les jusqu’à ce que luise le matin, et n’en laissons pas survivre un seul. » Ils dirent: « Fais tout ce qui te semblera bon. » Mais le grand prêtre dit: « Approchons-nous ici de Dieu. »
37 Saboda haka Shawulu ya tambayi Allah ya ce, “Mu bi bayan Filistiyawa? Za ka bashe su a hannun Isra’ila?” Amma Allah bai ba shi amsa a ranar ba.
Et Saül consulta Dieu: « Descendrai-je à la poursuite des Philistins? Les livrerez-vous entre les mains d’Israël? » Et Yahweh ne lui donna pas de réponse ce jour-là.
38 Saboda haka Shawulu ya ce, “Ku zo nan dukanku shugabannin rundunoni, mu bincika mu san zunubin da ya kawo rashin amsan nan yau.
Saül dit: « Approchez ici, vous tous, chefs du peuple; recherchez et voyez quel est le péché qui a été commis aujourd’hui.
39 Muddin Ubangiji wanda ya ceci Isra’ila yana raye, ko da ɗana Yonatan ne ya yi zunubin, dole yă mutu.” Amma ba ko ɗaya daga cikinsu da ya ce uffam.
Car, aussi vrai que Yahweh, le libérateur d’Israël, est vivant, le péché fût-il sur mon fils Jonathas, il mourra. » Et dans tout le peuple personne ne lui répondit.
40 Sai Shawulu ya ce wa dukan Isra’ilawa, “Ku tsaya a can, ni kuma da Yonatan ɗana mu tsaya a nan.” Mutanen suka ce, “Ka yi abin da ya fi maka kyau.”
Il dit à tout Israël: « Vous, mettez-vous d’un côté, et moi et mon fils Jonathas nous serons de l’autre côté. » Et le peuple dit à Saül: « Fais ce qui te semblera bon. »
41 Sa’an nan Shawulu ya yi addu’a ga Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, “Me ya sa ba ka amsa mini addu’ata a yau ba? Idan wannan laifina ne, ko kuwa na ɗana, Yonatan, ka nuna mana ta wurin Urim, amma idan laifin mutanen ne ka amsa ta wurin Tummim.” Ba a sami mutane da laifi ba, amma ƙuri’a ta fāɗa a kan Yonatan da Shawulu.
Saül dit à Yahweh: « Dieu d’Israël, fais connaître la vérité! » Jonathas et Saül furent désignés, et le peuple fut libéré.
42 Shawulu ya ce, “Ku jefa ƙuri’a tsakanina da ɗana Yonatan.” Sai ƙuri’ar ta fāɗa a kan Yonatan.
Alors Saül dit: « Jetez le sort entre moi et Jonathas, mon fils. » Et Jonathas fut désigné.
43 Sai Shawulu ya ce wa Yonatan, “Gaya mini mene ne ka yi.” Yonatan ya ce masa, “Na ɗanɗana zuma kaɗan daga gindin sandanta. Yanzu kuwa dole in mutu!”
Saül dit à Jonathas: « Déclare-moi ce que tu as fait. » Jonathas le lui déclara, en disant: « J’ai goûté un peu de miel, avec l’extrémité du bâton que j’avais à la main; me voici, je mourrai! »
44 Shawulu ya ce, “Bari hukunci mai tsanani na Allah yă kasance a kaina, in ba ka mutu ba, Yonatan.”
Et Saül dit: « Que Dieu me traite dans toute sa rigueur, si tu ne meurs pas, Jonathas! »
45 Amma mutane suka ce wa Shawulu, “A ce Yonatan yă mutu bayan shi ya kawo babban nasara a Isra’ila? Faufau, muddin Ubangiji yana raye, ko gashin kansa ɗaya ba zai fāɗi a ƙasa ba, gama abin da ya yi yau, Allah ne yana tare da shi.” Ta haka mutane suka ceci Yonatan daga mutuwa.
Le peuple dit à Saül: « Jonathas mourrait donc, lui qui a opéré cette grande délivrance en Israël? Loin de nous! Yahweh est vivant! il ne tombera pas à terre un cheveu de sa tête car c’est avec Dieu qu’il a agi en ce jour. » C’est ainsi que le peuple sauva Jonathas, et il ne mourut point.
46 Sai Shawulu ya daina bin Filistiyawa, suka koma ƙasarsu.
Saül monta à Gabaa, sans poursuivre les Philistins et les Philistins regagnèrent leur pays.
47 Bayan Shawulu ya hau karagar mulkin Isra’ila, ya yi yaƙi da abokan gābansu ta kowane gefe. Mowabawa, Ammonawa, mutanen Edom, sarakunan Zoba, da kuma Filistiyawa. Duk wurin da ya juya, ya hore su.
Lorsque Saül eut pris possession de la royauté sur Israël, il fit la guerre aux alentours à tous ses ennemis, à Moab, aux enfants, d’Ammon, à Edom, aux rois de Soba et aux Philistins, et, partout où il se tournait, il l’emportait.
48 Ya yi jaruntaka sosai, ya ci Amalekawa da yaƙi, ya kuma ceci Isra’ila daga hannuwan waɗanda suka ƙwace musu kaya.
Il fit des exploits, battit Amalec et délivra Israël de la main de ceux qui le pillaient.
49 ’Ya’yan Shawulu maza su ne, Yonatan, Ishbi, da Malki-Shuwa. Sunan babban’yarsa ita ce Merab, ƙaramar kuma Mikal.
Les fils de Saül étaient Jonathas, Jessui et Melchisua; ses deux filles s’appelaient, l’aînée Mérob, et la plus jeune Michol.
50 Sunan matarsa kuwa Ahinowam,’yar Ahimawaz. Sunan shugaban ƙungiyar sojan Shawulu kuwa Abner ne ɗan Ner, shi Ner kuwa ɗan’uwan mahaifin Shawulu ne.
Le nom de la femme de Saül était Achinoam, fille d’Achimaas. Le nom du chef de son armée était Abner, fils de Ner, oncle de Saül.
51 Mahaifin Shawulu, Kish da kuma Ner mahaifin Abner,’ya’yan Abiyel ne.
Cis, père de Saül, et Ner, père d’Abner, étaient fils d’Abiel.
52 Dukan kwanakin Shawulu sun kasance na yaƙe-yaƙe da Filistiyawa ne. Duk lokacin da Shawulu ya ga ƙaƙƙarfan mutum ko jarumi, sai yă ɗauke shi aikin sojansa.
La guerre fut acharnée contre les Philistins pendant tous les jours de Saül, et quand Saül apercevait un homme fort et vaillant, il l’attachait à son service.

< 1 Sama’ila 14 >