< 1 Sama’ila 14 >
1 Wata rana Yonatan ɗan Shawulu ya ce wa saurayin da yake ɗaukar masa makamai, “Zo mu tafi wajen sansanin Filistiyawa a wancan hayi.” Amma bai gaya wa mahaifinsa ba.
Hnin at a om nen tah Saul capa Jonathan loh a hno phuei cadong te, “Halo lamtah rhalvang ah Philisti rhaltawt hmuen te paan sih,” a ti nah. Tedae a napa taengla puen pawh.
2 Shawulu kuwa na zaune a gindin itacen rumman a bayan garin Gibeya a Migron. Tare da shi akwai mutum wajen ɗari shida.
Te vaengah Saul tah Gibeah bawt ah, Migron kah tale thing hmuiah ngol tih a taengkah pilnam he hlang ya rhuk tluk omuh.
3 A cikinsu akwai Ahiya sanye da efod. Shi yaron Ikabod ɗan’uwan Ahitub ne, ɗan Finehas, ɗan Eli, firist na Ubangiji a Shilo. Ba wanda ya san cewa Yonatan ya tafi wani wuri.
Te vaengah hnisui aka bai tih Shiloh ah BOEIPA kah khosoih la aka om Eli capa Phinekha koca Ikhabod mana Ahitub capa Ahijah khaw om. Tedae Jonathan a caeh te pilnam loh a ming moenih.
4 A kowane gefe na mashigin da Yonatan ya so yă bi zuwa wurin Filistiyawa, akwai hawa mai tsawo, ana kira ɗaya Bozez, ɗayan kuma ana kira Senet.
Philisti rhaltawt hmuen paan ham te Jonathan loh a laklo kah lamkai longah a mae. Te vaengah rhalvangan khat benah thaelpang cangngok la om tih rhalvangan khat benah thaelpang cangngok la om bal. Pakhat a ming ah Bozez tih pakhat tah a ming ah Seneh ni.
5 Hawan da yake arewa yana fuskantar Mikmash, wanda yake kudu kuma yana fuskantar Geba.
Lungto cangngok pakhat te tlangpuei kah Mikmash imdan ah, pakhat te tuithim kah Geba imdan ah tungpuei la pai.
6 Yonatan ya ce wa saurayin mai ɗaukan makamai, “Zo mu haye zuwa mashigin mutane marasa kaciyan nan, wataƙila Ubangiji zai yi aiki a madadinmu. Ba abin da zai iya hana Ubangiji yin aikin ceto ta wurin mutane masu yawa, ko ta wurin mutane kaɗan.”
Jonathan loh a hno phuei cadong te, “Cet sih lamtah, pumdul rhoek kah rhaltawt hmuen ke paan sih. Amih te BOEIPA loh mamih ham a saii khaming. A yol a yet neh khang ham te BOEIPA taengah kanghalhkung a om moenih.
7 Mai ɗaukan makaman ya ce, “Ka yi duk abin da yake zuciyarka. Ci gaba, ina tare da kai gaba da baya.”
Te dongah a hno phuei loh, “Na thinko ah aka om te tah boeih saii ngawn. Na ngaih bangla vikvuek uh ngawn, na thinko kah bangla nang taengah ka om ngawn he,” a ti nah.
8 Yonatan ya ce, “To, zo mu haye zuwa wajen mutanen, mu sa su gan mu.
Te vaengah Jonathan loh, “Mamih rhoi loh hlang te m'paan coeng tih amih taengla m'phoe pawn ni he.
9 In suka ce mana, ‘Ku tsaya nan har mu zo wurinku,’ za mu dakata inda muke, ba za mu haura wajensu ba.
Tedae mamih rhoi taengah ni, “Nangmih taengla kaimih ka pawk hil duem rhoi dae,” a ti uh atah mah paihmuen ah pai sih lamtah amih taengla cet boel sih,” a ti nah.
10 Amma in suka ce mana, ‘Ku haura wurinmu,’ to, sai mu haura, wannan zai zama mana alama cewa Ubangiji ya bashe su a hannunmu.”
Tedae, “Kaimih taengla ha luei laeh,” a ti uh van atah luei van sih. Amih te BOEIPA loh mamih kut dongah m'paek coeng dongah tahae kah he mamih ham miknoek la om coeng,” a ti nah.
11 Sai suka nuna kansu a sansanin Filistiyawa. Sai Filistiyawa suka ce, “Ku duba ga Ibraniyawa suna fitowa daga cikin ramummuka inda suka ɓuya.”
Te phoeiah amih rhoi khaw Philisti rhaltawt hmuen taengla a moe rhoi hatah Philisti rhoek loh, “Aka thuh uh tangtae Hebrew loh a khui lamkah ha moe ke,” a ti uh.
12 Mutanen da suke sansanin suka kira Yonatan da mai ɗaukan makamansa da babbar murya suka ce, “Ku hauro wajenmu, mu kuwa za mu koya muku hankali.” Sai Yonatan ya ce wa mai ɗaukan makamansa, “Biyo ni, gama Ubangiji ya bashe su a hannun Isra’ila.”
Te dongah rhaltawt hlang rhoek loh Jonathan neh a hno phuei te a doo tih, “Kaimih taengla ha luei rhoi lamtah nangmih rhoi te olka kan thuituen eh?,” a ti nah. Te dongah a hno phuei te Jonathan loh, “Kai hnukah halo laeh, amih he BOEIPA loh Israel kut dongah a paek coeng,” a ti nah.
13 Sai Yonatan ya hau dutsen da rarrafe, mai ɗaukan makamansa kuwa yana biye. Yonatan ya yi ta fyaɗa Filistiyawa da ƙasa, mai ɗaukan makamansa kuma ya yi ta karkashe su.
Jonathan te a kut a kho neh a luei vaengah a hno phuei loh a hnukah a rhoi van. Te vaengah Jonathan mikhmuh kah aka cungku rhoek te a hno phuei loh a hnukah a ngawn pah.
14 A wannan karo na farko Yonatan da mai ɗaukan makamansa suka kashe mutum wajen ashirin a wani fili mai fāɗi rabin kadada.
Jonathan neh a hno phuei loh a tloek lamhma dongah khohmuen kah rhoi hma ngancawn ah hlang pakul tluk tah hmasoe la om.
15 Sai tsoro ya kama dukan sojojin Filistiyawa, waɗanda suke cikin sansanin da waɗanda suke fili, har da waɗanda suke waje, da kuma waɗanda suke kai hari, ƙasa ta girgiza. Allah ne ya kawo wannan rikicewa.
Te vaengah lambong khuiah khaw, lohma ah khaw, rhaltawt hmuen kah pilnam boeih khuiah khaw thuennah om. Amih a lakueng uh vaengah diklai te tlai tih Pathen taengkah thuennah bangla a om pah.
16 Masu gadin Shawulu a Gebiya da take a Benyamin suka duba sai ga rundunar Filistiyawa a warwatsewa ko’ina.
Benjamin Gibeah kah Saul kah rhaltawt rhoek loh a sawt uh vaengah tah hlangping te tarha paci tih he ben he bang la a caeh pah.
17 Sai Shawulu ya ce wa mutanen da suke tare da shi, “Ku ƙidaya mayaƙa ku ga wane ne ba ya nan.” Da suka ƙirga sai suka tarar Yonatan da mai ɗaukan makamansa ba sa nan.
Te dongah Saul loh a taengkah pilnam te, “So uh lah, mamih taeng lamkah aka cet rhoek te thuep uh lah,” a ti nah. Te vaengah Jonathan neh a hno phuei te hah tarha a tae uh.
18 Shawulu ya ce wa Ahiya, “Kawo akwatin alkawarin Allah.” (A lokacin akwatin alkawarin yana tare da Isra’ilawa.)
Tekah khohnin ah Pathen kah thingkawng he Israel ca rhoek taengla a om coeng dongah Ahijah te Saul loh, “Pathen kah thingkawng te hang khuen,” a ti nah.
19 Yayinda Shawulu yake magana da firist kuwa, harguwa ya yi ta ƙaruwa a sansanin Filistiyawa. Sai Shawulu ya ce wa firist, “Janye hannunka.”
Saul loh khosoih te a voek vaengah Philisti rhaehhmuen khuikah hlangping aka pongpa te a yet la muep pongpa uh. Te dongah khosoih te Saul loh, “Na kut te vawk poem ne,” a ti nah.
20 Sa’an nan Shawulu da dukan mutanensa suka taru suka tafi yaƙi. Suka tarar Filistiyawa sun ruɗe suna yaƙi da juna da takubansu.
Te daengah Saul neh a taengkah pilnam pum te a hueh tih caem te a paan uh. Tedae hlang kah cunghang loh a hui te a cuk thil tarha dongah soekloeknah loh len khungdaeng.
21 Ibraniyawan da suke tare da Filistiyawa a dā, waɗanda suka bi Filistiyawan zuwa sansanin yaƙinsu, suka juya, suka goyi bayan Shawulu da Yonatan sa’ad da yaƙin ya taso.
Hebrew rhoek loh hlaem hlavai ah tah Philisti taengla om uh tih rhaehhmuen kaepvai ah amih taengla cet uh. Tedae amih khaw Saul neh Jonathan taengkah Israel taengla koep om uh.
22 Sa’ad da dukan Isra’ilawan da suka ɓuya a duwatsu a ƙasar Efraim suka ji labari cewa Filistiyawa suna gudu, sai suka fito suka fafare su.
Philisti rhoek rhaelrham coeng tila Ephraim tlang ah aka thuh Israel hlang boeih loh a yaak uh vaengah caemtloek dongah amih taengah koep kaibaeng uh.
23 Haka Ubangiji ya kuɓutar da Isra’ila a wannan rana. Yaƙin kuwa ya ci gaba har gaba da Bet-Awen.
Tekah khohnin ah Israel te BOEIPA loh a khang dongah caem loh Bethaven a poeng phai.
24 A wannan rana, Isra’ilawa suka sha wahala ƙwarai domin Shawulu ya sa mutane suka yi rantsuwa cewa, “La’ananne ne mutumin da ya ci abinci kafin fāɗuwar rana, kafin in ɗauki fansa a kan abokan gābana.” Don haka ba mutumin da ya ɗanɗana abinci.
Te khohnin ah Israel hlang te a tueihno coeng. Saul loh pilnam te a tap tih, “Hlaem duela buh aka ca hlang te tah thaephoei thil saeh, ka thunkha soah phu ka loh vaengah,” a ti. Te dongah pilnam boeih loh buh ten pawh.
25 Dukan rundunar ta shiga kurmi, sai ga zuma a ƙasa.
Te daengah khohmuen pum loh duup neh diklai hman kah khoitui aka om te a paan uh pueng.
26 Da suka shiga ciki kurmin, suka ga zuma tana zubowa, duk da haka ba wanda ya sa yatsansa ya lasa saboda tsoron rantsuwar da suka yi.
Pilnam loh duup khuiah khoitui tuicip te lawt a thoeng thil. Tedae olhlo te pilnam loh a rhih dongah a ka khuila a kut puei pawh.
27 Yonatan bai san cewa mahaifinsa ya sa mutane suka yi rantsuwa ba. Sai ya sa gindin sandan da yake hannunsa a saƙar zuma, ya kai bakinsa. Nan da nan sai ya ji ƙarfin jiki ya zo masa.
Tedae a napa loh pilnam a toem a ngam vaengah Jonathan loh ya pawh. Te dongah a kut dongkah caitueng hmuidong te a khoh tih duup kah khoitui khuila a nuem. A hmuh lawt neh a kut te a ka dongla a coh hatah a mik a tueng pah.
28 Sai wani soja ya gaya masa cewa, “Mahaifinka ya sa kowa ya yi rantsuwa cewa, ‘La’ananne ne mutumin da ya ci abinci kafin fāɗuwar rana!’ Shi ya sa duk sojojin ba su da ƙarfi.”
Te vaengah pilnam khuikah hlang pakhat loh a doo tih, “Pilnam te na pa loh ol a caeng a caeng tih, 'Tihnin ah caak aka ca hlang tah thaephoei thil la om coeng,’ a ti nah dongah pilnam he lamlum,” a ti nah.
29 Yonatan ya ce, “Mahaifina ya jefa ƙasar cikin matsala. Duba yadda na ji ƙarfin jiki sa’ad da na ɗanɗana wannan’yar zuma mana.
Te vaengah Jonathan loh, “Khohmuen kongah a pa loh n'lawn coeng. He khoitui bet ka ten dongah ka mik a tueng he hmu uh van lah.
30 Da yaya zai kasance ke nan da a ce an bar sojoji suka ci abincin da suka ƙwace daga abokan gābansu? Ai, da gawawwakin Filistiyawan da aka kashe sun fi haka.”
A thunkha kah kutbuem a hmuh uh te pilnam loh tihnin ah ca lammah ca van mai koinih Philisti khuiah hmasoe yet pawt suidae a?,” a ti.
31 A ranan nan Isra’ilawa suka yi ta kashe Filistiyawa daga Mikmash har zuwa Aiyalon. Bayan haka gajiya ta kama su sosai saboda yunwa.
Tekah khohnin ah Philisti te Mikmash lamloh Aijalon duela a tloek uh tih pilnam khaw mat tawn.
32 Sai suka yi warwason ganima, suka kwashe tumaki, da shanu, da maruƙa, suka yayyanka su, suka ci naman ɗanye.
Te tlam te a saii vaengah pilnam te kutbuem kutbuem dongla cu. Te phoeiah boiva khaw, saelhung khaw, saelhung ca khaw a loh uh. Te te diklai ah a ngawn uh tih a thii khaw pilnam loh a caak thil.
33 Sai wani mutum ya ce wa Shawulu, “Duba, ga mutane suna zunubi ga Ubangiji, suna cin nama da jini.” Shawulu ya ce, “Kun ci amana. Ku mirgino babban dutse zuwa wurina nan da nan.”
Te dongah Saul taengla puen uh tih, “Thii a caak dongah pilnam loh BOEIPA taengah tholh uh coeng ke,” a ti nah. Tedae, “Na hnukpoh uh tih tihnin ah kai taengla lungnu nam paluet uh,” a ti nah.
34 Sa’an nan ya ce, “Ku tafi ku faɗa wa jama’a duka, su kawo shanu da tumaki a nan, su yayyanka, su ci a nan, don kada su yi wa Ubangiji zunubi da cin nama ɗanye.” Haka nan kowa ya kawo saniyarsa a daren, ya yanka a can.
Te phoeiah Saul loh, “Pilnam taengah taekyak uh lamtah amih te thui pah. Hlang boeih loh kai taengla a vaito khaw, hlang boeih loh a tu hang khuen saeh. He ah ngawn uh lamtah ca uh. Tedae a thii neh na caak ham tah BOEIPA taengah na tholh uh pawt nim?,” a ti nah. Te dongah khoyin ah tah pilnam boeih loh amah kah vaito te a kut dongah rhip a khuen uh tih pahoi a ngawn uh.
35 Sa’an nan Shawulu ya gina wa Ubangiji bagade. Wannan ne bagade na farkon da ya gina.
Te vaengah Saul loh BOEIPA ham hmueihtuk a suem te anih loh BOEIPA ham lamhma cuek a suem hmueihtuk la om.
36 Shawulu ya ce, “Mu bi gangara mu fafare Filistiyawa da dare mu washe su har gari yă waye, mu kuma karkashe kowannensu, kada mu bar wani da rai.” Suka ce, “Ka yi duk abin da ka ga ya fi maka kyau.” Amma firist ya ce, “Bari mu nemi nufin Allah tukuna.”
Te phoeiah Saul loh, “Khoyin ah Philisti hnuk te suntlak thil sih lamtah mincang khosae duela amih te poelyoe sih, amih hlang te hlun boel sih,” a ti nah hatah, “Na mik dongah aka then sarhui tah saii laeh,” a ti nauh. Tedae khosoih longtah, “Pathen taengla pahoi nawn uh sih,” a ti nah.
37 Saboda haka Shawulu ya tambayi Allah ya ce, “Mu bi bayan Filistiyawa? Za ka bashe su a hannun Isra’ila?” Amma Allah bai ba shi amsa a ranar ba.
Te dongah Pathen te Saul loh, “Philisti hnukah ka suntla aya? Amih ke Israel kut ah na paek aya? tila a dawt. Tedae tekah khohnin ah anih te doo pawh.
38 Saboda haka Shawulu ya ce, “Ku zo nan dukanku shugabannin rundunoni, mu bincika mu san zunubin da ya kawo rashin amsan nan yau.
Te dongah Saul loh, “Pilnam te a cong cong ah boeih ha mop saeh lamtah ming uh saeh. Tihnin kah aka om tholhnah he hmu uh van saeh.
39 Muddin Ubangiji wanda ya ceci Isra’ila yana raye, ko da ɗana Yonatan ne ya yi zunubin, dole yă mutu.” Amma ba ko ɗaya daga cikinsu da ya ce uffam.
BOEIPA kah hingnah dongah Israel he a khang. Te loh ka ca Jonathan om puei mai cakhaw Jonathan he duek rhoe duek saeh,” a ti. Tedae pilnam boeih loh anih te doo voel pawh.
40 Sai Shawulu ya ce wa dukan Isra’ilawa, “Ku tsaya a can, ni kuma da Yonatan ɗana mu tsaya a nan.” Mutanen suka ce, “Ka yi abin da ya fi maka kyau.”
Te phoeiah, “Nangmih Israel pum te rhalvangan pakhat ah om lamtah kai neh ka capa Jonathan tah rhalvangan pakhat ah ka om eh?,” a ti nah. Tedae Saul te pilnam loh, “Na mikhmuh ah aka then tah saii ngawn,” a ti nah.
41 Sa’an nan Shawulu ya yi addu’a ga Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, “Me ya sa ba ka amsa mini addu’ata a yau ba? Idan wannan laifina ne, ko kuwa na ɗana, Yonatan, ka nuna mana ta wurin Urim, amma idan laifin mutanen ne ka amsa ta wurin Tummim.” Ba a sami mutane da laifi ba, amma ƙuri’a ta fāɗa a kan Yonatan da Shawulu.
Te dongah Israel Pathen BOEIPA te Saul loh, “A cuemthuek mah m'pae,” a ti nah. Te dongah Jonathan neh Saul te a tuuk tih pilnam te loeih.
42 Shawulu ya ce, “Ku jefa ƙuri’a tsakanina da ɗana Yonatan.” Sai ƙuri’ar ta fāɗa a kan Yonatan.
Saul loh, “Kai laklo neh ka capa Jonathan laklo ah hmulung naan lah,” a ti nah tih Jonathan a tuuk.
43 Sai Shawulu ya ce wa Yonatan, “Gaya mini mene ne ka yi.” Yonatan ya ce masa, “Na ɗanɗana zuma kaɗan daga gindin sandanta. Yanzu kuwa dole in mutu!”
Te phoeiah Saul loh Jonathan te, “Na saii te kai taengah thui lah,” a ti nah. Te dongah Jonathan loh anih taengla a puen pah tih, “Khoitui a yol, ka kut dongkah caitueng hmuidong kah te ka ten la ka ten mai nen nim kai ka duek tarha eh?,” a ti nah.
44 Shawulu ya ce, “Bari hukunci mai tsanani na Allah yă kasance a kaina, in ba ka mutu ba, Yonatan.”
Saul loh, “Jonathan! duek khaw duek laeh, Pathen loh n'saii vetih n'talh bal ve,” a ti nah.
45 Amma mutane suka ce wa Shawulu, “A ce Yonatan yă mutu bayan shi ya kawo babban nasara a Isra’ila? Faufau, muddin Ubangiji yana raye, ko gashin kansa ɗaya ba zai fāɗi a ƙasa ba, gama abin da ya yi yau, Allah ne yana tare da shi.” Ta haka mutane suka ceci Yonatan daga mutuwa.
Tedae Saul taengah pilnam loh, “Israel khuiah khangnah a len la aka saii Jonathan te duek saeh e? BOEIPA kah hingnah nen tah savisava, tihnin ah he Pathen loh a saii puei dongah, a lu lamkah samtlang pakhat pataeng lai la rhul mahpawh,” a ti nah. Te dongah Jonathan te pilnam loh a lat tih duek pawh.
46 Sai Shawulu ya daina bin Filistiyawa, suka koma ƙasarsu.
Te daengah Saul khaw Philisti hnuk lamloh vik nong tih Philisti khaw amah hmuen la cet uh.
47 Bayan Shawulu ya hau karagar mulkin Isra’ila, ya yi yaƙi da abokan gābansu ta kowane gefe. Mowabawa, Ammonawa, mutanen Edom, sarakunan Zoba, da kuma Filistiyawa. Duk wurin da ya juya, ya hore su.
Saul loh Israel soah mangpa la huul uh tih, a kaepvai kah a thunkha boeih, Moab khaw, Ammon ca rhoek khaw, Edom khaw, Zobah manghai rhoek neh Philisti khaw a vathoh thil boeih te a hoilae tih, a tulnoi.
48 Ya yi jaruntaka sosai, ya ci Amalekawa da yaƙi, ya kuma ceci Isra’ila daga hannuwan waɗanda suka ƙwace musu kaya.
Caem neh a saii tih Amalek te a tloek dongah anih aka reth kut lamloh Israel te a huul.
49 ’Ya’yan Shawulu maza su ne, Yonatan, Ishbi, da Malki-Shuwa. Sunan babban’yarsa ita ce Merab, ƙaramar kuma Mikal.
Saul ca rhoek he Jonathan khaw, Ishee khaw, Malkhishua khaw, a canu rhoi khaw a ming om uh. A canu a ham ming tah Merab tih a noe ming Mikhal ni.
50 Sunan matarsa kuwa Ahinowam,’yar Ahimawaz. Sunan shugaban ƙungiyar sojan Shawulu kuwa Abner ne ɗan Ner, shi Ner kuwa ɗan’uwan mahaifin Shawulu ne.
Saul yuu, a ming ah Ahinoam he Ahimaaz canu ni. Anih kah caempuei mangpa, a ming ah Abner he khaw Saul kah a napanoe Ner capa ni.
51 Mahaifin Shawulu, Kish da kuma Ner mahaifin Abner,’ya’yan Abiyel ne.
Kish he tah Saul kah a napa la om tih, Abiel capa Abner he tah Ner kah a napa la om.
52 Dukan kwanakin Shawulu sun kasance na yaƙe-yaƙe da Filistiyawa ne. Duk lokacin da Shawulu ya ga ƙaƙƙarfan mutum ko jarumi, sai yă ɗauke shi aikin sojansa.
Saul tue khuiah he Philisti neh caemtloek he a tlungluen la om. Te dongah Saul loh hlang boeih te hlangrhalh neh tatthai ca khaw boeih a hmuh tih amah taengla a coi.