< 1 Sama’ila 13 >

1 Shawulu yana da shekara talatin sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi sarautar Isra’ila shekara arba’in da biyu.
Şaul paççah ıxhamee, mang'uqa xhebts'al senniy vod. Mana yoq'ts'ale q'olle senna İzrailyna paççah ıxha.
2 Sai ya zaɓi sojoji dubu uku daga jama’ar Isra’ila. Ya keɓe dubu biyu su kasance tare da shi a Mikmash da kuma a tuddan yankin Betel. Ya kuma bar dubu ɗaya tare da ɗansa Yonatan a Gibeya a yankin zuriyar Benyamin. Sauran sojojin kuwa Shawulu ya sallame su su koma gidajensu.
Şaulee cune g'oşunbışeeqa xhebıd aazır İzrailyğançena g'əyxə. Manbışda q'öd aazır insan cukasana Mikmas eyhene şahareeyiy Bet-Elyne tepabışee vooxhe. Aazır insanmee cune duxayka, Yonatanıka, Benyaminna nasıl vooxhene Givea eyhene şaharee vooxhe. Mansa axuyn milletmee Şaulee cone xaybışeeqa yəqqı'l ha'a.
3 Yonatan ya kai wa Filistiyawa hari a Geba, sai Filistiyawa suka sami labarin. Sai Shawulu ya sa aka busa ƙaho ko’ina a ƙasar ya ce, “Bari Ibraniyawa su ji!”
Yonatanee Giveayeene Filiştinaaşde zastaaveebın eskerar gyabat'a, manıd Filiştinaaşik'le ats'axhxhen. Şauleeme: «Cühüt'yaaşik'le g'ayxhecenva!» uvhu, ölkavolle şeypur hook'as ulyookka.
4 Haka kuwa dukan Isra’ila suka ji labari cewa, “Shawulu ya kai hari a ƙasar Filistiyawa, yanzu Isra’ila ta zama abin ƙi ga Filistiyawa.” Aka kira mutane su haɗu da Shawulu a Gilgal.
İzrailybışde gırgıng'uk'le Şaulee, Filiştinaaşde zastaveebın eskerar gyapt'ıyıd, Filiştinaaşik'le İzrailybı g'umooce qeepxhayıd g'ayxhiyn. Millet Şaulne hiqiy-alla salecenva Gilgaleeqa qoyt'al.
5 Sai Filistiyawa suka taru don su yi yaƙi da Isra’ilawa. Suka fito da kekunan-dawakan yaƙi dubu talatin, da masu hawan dawakai dubu shida, da sojoji masu yawa kamar yashi a bakin teku. Suka tafi Mikmash a gabashin Bet-Awen, suka kafa sansani a can.
Filiştinarıb İzrailybışika səvxəsva savayle. Manbışe xhebts'al aazır dəv'əyn daşk'a, yixhıd aazırır balkanılyna sa'a. Manbışda g'oşun deryahne mıglekna g'um xhinne geeb vuxha. Manbı apk'ın Bet-Aven eyhene şaharne şargıl Mikmasee çadırbı giyxə.
6 Sa’ad da Filistiyawa suka fāɗa wa Isra’ilawa da yaƙi mai tsanani, suka sa su cikin wani hali mai wuya, sai Isra’ilawa suka ɓuya a kogwanni, da ciyayi, da duwatsu, da ramummuka, da rijiyoyi.
İzrailybışik'le cok ixhesın g'acumee, co ooşaa'a g'avcumee, manbı mağarabışee, axtıne ok'bışee, suvabışee, k'oralybışee, kahrızbışee dyuguleebaxhenbı.
7 Waɗansunsu ma suka haye Urdun zuwa ƙasar Gad da Gileyad. Shawulu ya zauna Gilgal, dukan ƙungiyoyi sojojin da suke tare da shi suka yi rawan jiki don tsoro.
Manbışiken sabarabı İordanne damayne şene aqvalqa Qadne nasıleneyiy Gileadne cigabışeeqa ılğeebaç'e. Şaul vuc Gilgalee axva, cukane milletınıd qəpq'ı'niyvalin yik'bı qoda eyxhe.
8 Ya jira har kwana bakwai bisa ga lokacin da Sama’ila ya bayar. Amma Sama’ila bai zo Gilgal ba, mutanen Shawulu suka fara watsewa.
Şaulee, Şamuelee uvhuyn xhinne yighılle yiğna gozet ha'an. Mane gahıl Şamuel Gilgalqa arayle deş. Şaulne hiqiy-alla sabıyn insanar heebaxa giviyğal.
9 Sai ya ce, “Ku kawo mini hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama.” Sai Shawulu ya miƙa hadaya ta ƙonawa.
Şaulee eyhen: – Gyoxhxhan ha'asıniy medın q'urbanbı zasqa qale. Mang'vee vuceecab gyooxhan haa'ana q'urban ablyaa'a.
10 Daidai yana gama miƙa hadaya ke nan sai Sama’ila ya iso. Shawulu kuma ya fito domin yă yi masa maraba.
Gyooxhan haa'ana q'urban ablyav'u ç'əveepxhamee, Şamuel qarı hiyxhar. Şaul salam hevlesva mang'une ögilqa qığeç'e.
11 Sama’ila ya ce, “Me ke nan ka yi?” Shawulu ya ce, “Sa’ad da na ga mutane suna watsewa, kai kuwa ba ka zo cikin lokaci ba, ga Filistiyawa kuma suna taruwa a Mikmash,
Şamuelee eyhen: – Ğu in hı'iyn kar hucoone? Şaulee mang'us cuvab qele: – Zak'le g'acuyn yizde hıqiy-alladın millet hexva vod, ğunar ğu eyhene yiğıl arı hirxhıl deş, Filiştinarıb Mikmasqa vob sabı.
12 sai na yi tunani cewa, ‘Yanzu Filistiyawa za su gangaro su fāɗa mini a Gilgal, ga ni kuma ban riga na nemi nufin Ubangiji ba.’ Shi ya sa ya zama mini tilas in miƙa hadaya ta ƙonawa.”
Zı zaled-alqa uvhuyn: «Həşde xhinnee Filiştinar Gilgalılqa zalqa k'yooharas, zımee Rəbbina xayir-düə alyapt'ı deş». Mançil-allar zıcar zı gyooxhan haa'ana q'urban ablyaa'as alikkı.
13 Sama’ila ya ce, “Ka yi wauta da ba ka bi umarnin da Ubangiji Allahnka ya ba ka ba. Da ka yi haka da Ubangiji ya tabbatar maka da sarautar Isra’ila har abada.
Şamuelee Şauluk'le eyhen: – Ğu ək'el deşin kar hı'ı. Yiğne Allahne, Rəbbine, əmrılqa əməl hı'ı deş. Ğu məxüd hidi'iynxhiy, Rəbbee yiğna paççahiyvalla İzrailil oğa gırgıne gahbışis havaacesdaniy.
14 Amma yanzu, masarautarka ba za tă dawwama ba, Ubangiji ya riga ya sami wani wanda zuciyarsa ke ƙauna, ya naɗa shi shugaban mutanensa gama ba ka bi umarnin Ubangiji ba.”
Həşdemee yiğna paççahiyvalla xıliyba ts'ıts'uvxhes deş. Rəbbee Cus ıkkanna, Cune yik'es sik'ına insan t'abal hı'ı. Ğu Rəbbine əmrılqa əməl hidi'iynçil-alla, Rəbbee mana insan Cune milletna xərna gixhxhı.
15 Sama’ila ya tashi daga Gilgal ya tafi Gibeya a ƙasar Benyamin. Shawulu kuma ya ƙidaya mutanen da suke tare da shi, yawansu ya kai wajen mutum ɗari shida.
Mançile qiyğa Şamuel Gilgaleençe qığeç'u, Benyaminaaşine Givea eyhene şahareeqa ılqeç'e. Şaulee cun insanar qəpq'ı'mee, yixhıd vəşilqa ələəna insan eyxhe.
16 Shawulu da ɗansa Yonatan da mutanen da suke tare da shi suka zauna a Geba ta Benyamin. Sa’an nan Filistiyawa suka yi sansani a Mikmash.
Şaulıy cuna dix Yonatan, cone insanaaşika Benyaminaaşine Givea eyhene şaharee ulyobzur vuxha. Filiştinarmee mane gahıl, Mikmasee çadırbı gı'xı', ulyobzur vuxha.
17 Rundunar mayaƙa uku suka fito daga sansani Filistiyawa. Ɗaya ta nufi Ofra, zuwa ƙasar Shuwal.
Filiştinaaşin g'oşunbı xhebne cigeeqa bit'aleetxha hücum haa'asva qığeedaç'e. Manbışda sa deste Şualne cigabışeene Ofra eyhene şaharne suralqa siviyk'al.
18 Runduna guda kuma ta nufi Bet-Horon, ɗayan kuwa ta nufi iyakar da take fuskantar Kwarin Ziboyim wajen jeji.
Manasa desteb Bet-Xoronne yəqqı'lqa avayk'an. Xheyib'esda destemee Tsevoimne q'adaalilqa, sarhadılqa avayk'an. Maa sahraaniy vob.
19 Ba a sami maƙeri ɗaya a dukan ƙasar Isra’ila ba domin Filistiyawa sun ce, “In ba haka ba Ibraniyawa za su ƙera wa kansu takuba ko māsu.”
Filiştinaaşe uvhuynniy: «Hasre cühüt'yaaşe g'ılınciy nize hıma'acen». Mançil-allad İzrailee sa ixheyir yiva getas əxəna insan deşdaniy.
20 Saboda haka dukan Isra’ila sukan gangara zuwa wajen Filistiyawa domin su gyara bakin garemaninsu, da fartanansu, da gaturansu, da kuma laujunansu.
Gırgın İzrailybı kyotanbı, toxabı, yak'vbı, ərabbı ek'a'asva Filiştinaaşde k'anyaqa abayle vuxha.
21 Duk lokacin da za su gyara bakin garmansu da fartanyarsu sai sun biya tsabar azurfa biyu. Haka ma idan za su gyara gatari ko bakunan abin korar shanun noma sai sun biya tsabar azurfa ɗaya.
Manbışike kyotan, yaba, yak'v, rab, toxa ek'a'as sa pim nuk'raynaniy hooqqana.
22 A ranar da yaƙi ya tashi, ba a sami wanda yake da takobi ko māshi ba a cikin mutanen da suke tare da Shawulu da Yonatan. Sai dai Shawulu da ɗansa Yonatan kaɗai.
Mançil-allad dəv'ənang'a Şaulneyiy Yonatanne milletıqa g'ılıncbıyiy nizebı ıxha deş. G'ılınciy nize saccu Şauluqayiy cune duxayqa Yonatanıqa ıxha.
23 Ana nan sai sojojin Filistiyawa suka fita zuwa mashigin Mikmash.
Filiştinaaşda deste Mikmasısneene ı'lğəəne cigeeqa qavayle.

< 1 Sama’ila 13 >