< 1 Sama’ila 13 >

1 Shawulu yana da shekara talatin sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi sarautar Isra’ila shekara arba’in da biyu.
Saul hade varit konung ett år, och när han nu regerade över Israel på andra året,
2 Sai ya zaɓi sojoji dubu uku daga jama’ar Isra’ila. Ya keɓe dubu biyu su kasance tare da shi a Mikmash da kuma a tuddan yankin Betel. Ya kuma bar dubu ɗaya tare da ɗansa Yonatan a Gibeya a yankin zuriyar Benyamin. Sauran sojojin kuwa Shawulu ya sallame su su koma gidajensu.
utvalde han åt sig tre tusen män ur Israel. Av dessa hade Saul själv hos sig två tusen i Mikmas och i Betels bergsbygd, och ett tusen hade Jonatan hos sig i Gibea i Benjamin. Men det övriga folket hade han låtit gå hem, var och en till sin hydda.
3 Yonatan ya kai wa Filistiyawa hari a Geba, sai Filistiyawa suka sami labarin. Sai Shawulu ya sa aka busa ƙaho ko’ina a ƙasar ya ce, “Bari Ibraniyawa su ji!”
Och Jonatan dräpte filistéernas fogde i Geba; och filistéerna fingo höra det. Men Saul lät stöta i basun över hela landet och säga: »Detta må hebréerna höra.»
4 Haka kuwa dukan Isra’ila suka ji labari cewa, “Shawulu ya kai hari a ƙasar Filistiyawa, yanzu Isra’ila ta zama abin ƙi ga Filistiyawa.” Aka kira mutane su haɗu da Shawulu a Gilgal.
Så fick hela Israel höra omtalas att Saul hade dräpt filistéernas fogde, och att Israel därigenom hade blivit förhatligt för filistéerna. Och folket bådades upp att följa Saul till Gilgal.
5 Sai Filistiyawa suka taru don su yi yaƙi da Isra’ilawa. Suka fito da kekunan-dawakan yaƙi dubu talatin, da masu hawan dawakai dubu shida, da sojoji masu yawa kamar yashi a bakin teku. Suka tafi Mikmash a gabashin Bet-Awen, suka kafa sansani a can.
Under tiden hade filistéerna församlat sig för att strida mot Israel: trettio tusen vagnar och sex tusen ryttare, och fotfolk så talrikt som sanden på havets strand; och de drogo upp och lägrade sig vid Mikmas, öster om Bet-Aven.
6 Sa’ad da Filistiyawa suka fāɗa wa Isra’ilawa da yaƙi mai tsanani, suka sa su cikin wani hali mai wuya, sai Isra’ilawa suka ɓuya a kogwanni, da ciyayi, da duwatsu, da ramummuka, da rijiyoyi.
Då nu israeliterna sågo sig vara i nöd, i det att folket svårt ansattes, gömde sig folket i grottor, i skogssnår och bland klippor, i fasta valv och i gropar.
7 Waɗansunsu ma suka haye Urdun zuwa ƙasar Gad da Gileyad. Shawulu ya zauna Gilgal, dukan ƙungiyoyi sojojin da suke tare da shi suka yi rawan jiki don tsoro.
Och somliga av hebréerna gingo över Jordan in i Gads och Gileads land. Men Saul var ännu kvar i Gilgal; och allt folket följde honom med bävan.
8 Ya jira har kwana bakwai bisa ga lokacin da Sama’ila ya bayar. Amma Sama’ila bai zo Gilgal ba, mutanen Shawulu suka fara watsewa.
När han nu hade väntat sju dagar, intill den tid Samuel hade bestämt men Samuel likväl icke kom till Gilgal, begynte folket skingra sig och gå ifrån honom.
9 Sai ya ce, “Ku kawo mini hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama.” Sai Shawulu ya miƙa hadaya ta ƙonawa.
Då sade Saul: »Fören fram till mig brännoffers- och tackoffersdjuren.» Därpå frambar han brännoffret.
10 Daidai yana gama miƙa hadaya ke nan sai Sama’ila ya iso. Shawulu kuma ya fito domin yă yi masa maraba.
Men just när han hade slutat att frambära brännoffret, kom Samuel. Då gick Saul honom till mötes för att hälsa honom.
11 Sama’ila ya ce, “Me ke nan ka yi?” Shawulu ya ce, “Sa’ad da na ga mutane suna watsewa, kai kuwa ba ka zo cikin lokaci ba, ga Filistiyawa kuma suna taruwa a Mikmash,
Men Samuel sade: »Vad har du gjort!» Saul svarade: »När jag såg att folket skingrade sig och gick ifrån mig, under det att du icke kom inom den bestämda tiden, fastän filistéerna voro församlade vid Mikmas,
12 sai na yi tunani cewa, ‘Yanzu Filistiyawa za su gangaro su fāɗa mini a Gilgal, ga ni kuma ban riga na nemi nufin Ubangiji ba.’ Shi ya sa ya zama mini tilas in miƙa hadaya ta ƙonawa.”
då tänkte jag: Nu komma filistéerna hitned mot mig i Gilgal, och jag har ännu icke bönfallit inför HERREN. Då tog jag mod till mig och offrade brännoffret.»
13 Sama’ila ya ce, “Ka yi wauta da ba ka bi umarnin da Ubangiji Allahnka ya ba ka ba. Da ka yi haka da Ubangiji ya tabbatar maka da sarautar Isra’ila har abada.
Samuel sade till Saul: »Du har handlat dåraktigt. Du har icke hållit det bud HERREN, din Gud, har givit dig; eljest skulle HERREN hava befäst ditt konungadöme över Israel för evig tid.
14 Amma yanzu, masarautarka ba za tă dawwama ba, Ubangiji ya riga ya sami wani wanda zuciyarsa ke ƙauna, ya naɗa shi shugaban mutanensa gama ba ka bi umarnin Ubangiji ba.”
Men nu skall ditt konungadöme icke bliva beståndande. HERREN har sökt sig en man efter sitt hjärta, och honom har HERREN förordnat till furste över sitt folk, eftersom du icke har hållit vad HERREN bjöd dig.»
15 Sama’ila ya tashi daga Gilgal ya tafi Gibeya a ƙasar Benyamin. Shawulu kuma ya ƙidaya mutanen da suke tare da shi, yawansu ya kai wajen mutum ɗari shida.
Därefter stod Samuel upp och gick från Gilgal till Gibea i Benjamin. Men Saul mönstrade det folk som fanns hos honom: vid pass sex hundra man.
16 Shawulu da ɗansa Yonatan da mutanen da suke tare da shi suka zauna a Geba ta Benyamin. Sa’an nan Filistiyawa suka yi sansani a Mikmash.
Och Saul och hans son Jonatan stannade i Geba i Benjamin med det folk som fanns hos dem, under det att filistéerna hade lägrat sig vid Mikmas.
17 Rundunar mayaƙa uku suka fito daga sansani Filistiyawa. Ɗaya ta nufi Ofra, zuwa ƙasar Shuwal.
Och en härskara, delad i tre hopar, drog ut ur filistéernas läger för att härja: en hop tog vägen till Ofra i Sualslandet,
18 Runduna guda kuma ta nufi Bet-Horon, ɗayan kuwa ta nufi iyakar da take fuskantar Kwarin Ziboyim wajen jeji.
en hop tog vägen till Bet-Horon, och en hop tog vägen till det område som vetter åt Seboimsdalen, åt öknen till.
19 Ba a sami maƙeri ɗaya a dukan ƙasar Isra’ila ba domin Filistiyawa sun ce, “In ba haka ba Ibraniyawa za su ƙera wa kansu takuba ko māsu.”
Ingen smed fanns då i hela Israels land, ty filistéerna fruktade att hebréerna skulle låta göra sig svärd eller spjut.
20 Saboda haka dukan Isra’ila sukan gangara zuwa wajen Filistiyawa domin su gyara bakin garemaninsu, da fartanansu, da gaturansu, da kuma laujunansu.
Och så måste en israelit alltid begiva sig ned till filistéerna, om han ville låta vässa sin lie eller sin plogbill eller sin yxa eller sin skära,
21 Duk lokacin da za su gyara bakin garmansu da fartanyarsu sai sun biya tsabar azurfa biyu. Haka ma idan za su gyara gatari ko bakunan abin korar shanun noma sai sun biya tsabar azurfa ɗaya.
när det hade blivit något fel med eggen på skärorna eller plogbillarna, eller med gafflarna eller yxorna, eller när oxpikarnas uddar behövde rätas.
22 A ranar da yaƙi ya tashi, ba a sami wanda yake da takobi ko māshi ba a cikin mutanen da suke tare da Shawulu da Yonatan. Sai dai Shawulu da ɗansa Yonatan kaɗai.
Härav kom sig, att när striden skulle stå, ingen enda av Sauls och Jonatans folk hade ett svärd eller ett spjut; allenast Saul själv och hans son Jonatan hade sådana.
23 Ana nan sai sojojin Filistiyawa suka fita zuwa mashigin Mikmash.
Men filistéerna läto en utpost rycka fram till passet vid Mikmas.

< 1 Sama’ila 13 >