< 1 Sama’ila 13 >

1 Shawulu yana da shekara talatin sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi sarautar Isra’ila shekara arba’in da biyu.
Reino Saúl por un año. Y cuando cumplió dos años de reinado.
2 Sai ya zaɓi sojoji dubu uku daga jama’ar Isra’ila. Ya keɓe dubu biyu su kasance tare da shi a Mikmash da kuma a tuddan yankin Betel. Ya kuma bar dubu ɗaya tare da ɗansa Yonatan a Gibeya a yankin zuriyar Benyamin. Sauran sojojin kuwa Shawulu ya sallame su su koma gidajensu.
Entonces Saúl tomó para sí tres mil hombres de Israel, de los cuales mantuvo dos mil con él en Micmas y en la montaña de Betel, y mil estaban con Jonatán en Guibea, en la tierra de Benjamín: El resto de las personas ordenó que se fueran a sus campamentos.
3 Yonatan ya kai wa Filistiyawa hari a Geba, sai Filistiyawa suka sami labarin. Sai Shawulu ya sa aka busa ƙaho ko’ina a ƙasar ya ce, “Bari Ibraniyawa su ji!”
Y Jonatán atacó a la fuerza armada de los filisteos estacionados en Guibea; y se dio a los filisteos la noticia de que los hebreos se volvían contra ellos. Y Saúl hizo sonar un cuerno por toda la tierra,
4 Haka kuwa dukan Isra’ila suka ji labari cewa, “Shawulu ya kai hari a ƙasar Filistiyawa, yanzu Isra’ila ta zama abin ƙi ga Filistiyawa.” Aka kira mutane su haɗu da Shawulu a Gilgal.
Y todo Israel tenía la noticia de que Saúl había atacado a los filisteos, y que Israel era odiado por los filisteos. Y la gente se unió después de Saúl a Gilgal.
5 Sai Filistiyawa suka taru don su yi yaƙi da Isra’ilawa. Suka fito da kekunan-dawakan yaƙi dubu talatin, da masu hawan dawakai dubu shida, da sojoji masu yawa kamar yashi a bakin teku. Suka tafi Mikmash a gabashin Bet-Awen, suka kafa sansani a can.
Y los filisteos se juntaron para hacer la guerra a Israel, tres mil carruajes de guerra, seis mil jinetes y un ejército de personas numerosas como la arena del mar; subieron y tomaron su posición en Micmas, al al este de Bet-aven.
6 Sa’ad da Filistiyawa suka fāɗa wa Isra’ilawa da yaƙi mai tsanani, suka sa su cikin wani hali mai wuya, sai Isra’ilawa suka ɓuya a kogwanni, da ciyayi, da duwatsu, da ramummuka, da rijiyoyi.
Cuando los hombres de Israel vieron el peligro en el que se encontraban, (porque la gente estaba preocupada), se cubrieron en las grietas de las laderas y en los bosques y en las rocas, los hoyos y los huecos.
7 Waɗansunsu ma suka haye Urdun zuwa ƙasar Gad da Gileyad. Shawulu ya zauna Gilgal, dukan ƙungiyoyi sojojin da suke tare da shi suka yi rawan jiki don tsoro.
Y gran parte de la gente había pasado el Jordán a la tierra de Gad y de Galaad; pero Saúl todavía estaba en Gilgal, y toda la gente lo siguió temblando de miedo.
8 Ya jira har kwana bakwai bisa ga lokacin da Sama’ila ya bayar. Amma Sama’ila bai zo Gilgal ba, mutanen Shawulu suka fara watsewa.
Y siguió esperando allí durante siete días, el tiempo fijado por Samuel, pero Samuel no vino a Gilgal; y la gente empezaba a alejarse de él.
9 Sai ya ce, “Ku kawo mini hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama.” Sai Shawulu ya miƙa hadaya ta ƙonawa.
Entonces Saúl dijo: Ven, dame el holocausto y las ofrendas de paz. E hizo una ofrenda quemada al Señor.
10 Daidai yana gama miƙa hadaya ke nan sai Sama’ila ya iso. Shawulu kuma ya fito domin yă yi masa maraba.
Y cuando terminó la ofrenda quemada, vino Samuel; y Saúl salió a verlo y le dio una bendición.
11 Sama’ila ya ce, “Me ke nan ka yi?” Shawulu ya ce, “Sa’ad da na ga mutane suna watsewa, kai kuwa ba ka zo cikin lokaci ba, ga Filistiyawa kuma suna taruwa a Mikmash,
Y Samuel dijo: ¿Qué has hecho? Y Saúl dijo: Porque vi que la gente se estaba alejando de mí, y tú no habías venido en el tiempo que se había fijado, y los filisteos se habían reunido en Micmas;
12 sai na yi tunani cewa, ‘Yanzu Filistiyawa za su gangaro su fāɗa mini a Gilgal, ga ni kuma ban riga na nemi nufin Ubangiji ba.’ Shi ya sa ya zama mini tilas in miƙa hadaya ta ƙonawa.”
Dije: Ahora los filisteos bajarán sobre mí en Gilgal, y no he orado pidiendo ayuda al Señor; así que, me vi forzado a hacerlo, hice una ofrenda quemada.
13 Sama’ila ya ce, “Ka yi wauta da ba ka bi umarnin da Ubangiji Allahnka ya ba ka ba. Da ka yi haka da Ubangiji ya tabbatar maka da sarautar Isra’ila har abada.
Entonces Samuel dijo a Saúl: Has hecho una estupidez: no guardaste las reglas que el SEÑOR tu Dios te dio; El propósito del Señor era hacer que tu reinado sobre Israel fuera segura para siempre.
14 Amma yanzu, masarautarka ba za tă dawwama ba, Ubangiji ya riga ya sami wani wanda zuciyarsa ke ƙauna, ya naɗa shi shugaban mutanensa gama ba ka bi umarnin Ubangiji ba.”
Pero ahora tu reinado no continuará: el Señor buscara un hombre que le agrade en todo sentido conforme a su corazón, le dará el lugar de gobernante sobre su pueblo, porque no has hecho lo que el Señor Te dio órdenes de hacer.
15 Sama’ila ya tashi daga Gilgal ya tafi Gibeya a ƙasar Benyamin. Shawulu kuma ya ƙidaya mutanen da suke tare da shi, yawansu ya kai wajen mutum ɗari shida.
Luego subió Samuel de Gilgal y el resto de la gente subió después de Saúl contra los hombres de guerra, y vinieron de Gilgal a Gibeah en la tierra de Benjamín: y Saúl tomó el número de las personas que estaban Con él, unos seiscientos hombres.
16 Shawulu da ɗansa Yonatan da mutanen da suke tare da shi suka zauna a Geba ta Benyamin. Sa’an nan Filistiyawa suka yi sansani a Mikmash.
Y Saúl, con su hijo Jonatán y la gente que estaba con ellos, esperaba en Geba, en la tierra de Benjamín, pero las tiendas de los filisteos estaban en Micmas.
17 Rundunar mayaƙa uku suka fito daga sansani Filistiyawa. Ɗaya ta nufi Ofra, zuwa ƙasar Shuwal.
Y tres escuadrones de hombres salieron de los filisteos para destruir la tierra; Un y escuadrón pasó por el camino que va a Ofra, a la tierra de Sual.
18 Runduna guda kuma ta nufi Bet-Horon, ɗayan kuwa ta nufi iyakar da take fuskantar Kwarin Ziboyim wajen jeji.
Y otro fue en dirección a Bet-horon; y otro fue por la colina mirando hacia el valle de Zeboim, en dirección al desierto.
19 Ba a sami maƙeri ɗaya a dukan ƙasar Isra’ila ba domin Filistiyawa sun ce, “In ba haka ba Ibraniyawa za su ƙera wa kansu takuba ko māsu.”
No había herrero en toda la tierra de Israel; porque los filisteos no lo permitían, Por temor a los hebreos se hicieran espadas o lanzas.
20 Saboda haka dukan Isra’ila sukan gangara zuwa wajen Filistiyawa domin su gyara bakin garemaninsu, da fartanansu, da gaturansu, da kuma laujunansu.
Pero todos los israelitas tenían que ir a los filisteos para afilar sus arados y azadones, hachas y hoces;
21 Duk lokacin da za su gyara bakin garmansu da fartanyarsu sai sun biya tsabar azurfa biyu. Haka ma idan za su gyara gatari ko bakunan abin korar shanun noma sai sun biya tsabar azurfa ɗaya.
Se cobraba ocho gramos de plata para afilar, los instrumentos en sus arados, azadones, horquillas y hachas, y para poner puntas de hierro en sus varas de empuje de bueyes.
22 A ranar da yaƙi ya tashi, ba a sami wanda yake da takobi ko māshi ba a cikin mutanen da suke tare da Shawulu da Yonatan. Sai dai Shawulu da ɗansa Yonatan kaɗai.
En el día de la pelea en Micmas, no se vio ni una espada ni una lanza en las manos de ninguna de las personas con Saúl y Jonatán: solo Saúl y su hijo Jonatán los tuvieron.
23 Ana nan sai sojojin Filistiyawa suka fita zuwa mashigin Mikmash.
Y la fuerza armada de los filisteos salió al estrecho camino de Micmas.

< 1 Sama’ila 13 >