< 1 Sama’ila 13 >
1 Shawulu yana da shekara talatin sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi sarautar Isra’ila shekara arba’in da biyu.
Saul war ein Jahr im Königtum und regierte zwei Jahre über Israel;
2 Sai ya zaɓi sojoji dubu uku daga jama’ar Isra’ila. Ya keɓe dubu biyu su kasance tare da shi a Mikmash da kuma a tuddan yankin Betel. Ya kuma bar dubu ɗaya tare da ɗansa Yonatan a Gibeya a yankin zuriyar Benyamin. Sauran sojojin kuwa Shawulu ya sallame su su koma gidajensu.
Und Saul erwählte sich dreitausend Mann aus Israel; und bei Saul waren zweitausend in Michmasch und auf dem Berge von Bethel, und tausend waren bei Jonathan zu Gibea-Benjamin, und das übrige Volk entsandte er, jeden Mann in seine Zelte.
3 Yonatan ya kai wa Filistiyawa hari a Geba, sai Filistiyawa suka sami labarin. Sai Shawulu ya sa aka busa ƙaho ko’ina a ƙasar ya ce, “Bari Ibraniyawa su ji!”
Und Jonathan schlug den Posten der Philister in Geba, und die Philister hörten es. Und Saul ließ im ganzen Lande in die Posaune stoßen und sagen: Die Hebräer sollen das hören.
4 Haka kuwa dukan Isra’ila suka ji labari cewa, “Shawulu ya kai hari a ƙasar Filistiyawa, yanzu Isra’ila ta zama abin ƙi ga Filistiyawa.” Aka kira mutane su haɗu da Shawulu a Gilgal.
Und ganz Israel hörte sagen: Saul hat den Posten der Philister geschlagen, und Israel stinkt auch bei den Philistern; und alles Volk wurde gerufen nach Gilgal, hinter Saul her.
5 Sai Filistiyawa suka taru don su yi yaƙi da Isra’ilawa. Suka fito da kekunan-dawakan yaƙi dubu talatin, da masu hawan dawakai dubu shida, da sojoji masu yawa kamar yashi a bakin teku. Suka tafi Mikmash a gabashin Bet-Awen, suka kafa sansani a can.
Und die Philister versammelten sich, mit Israel zu streiten, dreißigtausend Streitwagen und sechstausend Reiter und des Volkes wie der Sand am Meeresufer in Menge, und sie zogen herauf und lagerten in Michmasch, östlich von Beth-Aven.
6 Sa’ad da Filistiyawa suka fāɗa wa Isra’ilawa da yaƙi mai tsanani, suka sa su cikin wani hali mai wuya, sai Isra’ilawa suka ɓuya a kogwanni, da ciyayi, da duwatsu, da ramummuka, da rijiyoyi.
Und die Männer von Israel sahen, daß sie in Drangsal waren, denn das Volk war in der Enge, und das Volk versteckte sich in Höhlen und in Dornhecken und in Felsklippen und in Festen und in Gruben.
7 Waɗansunsu ma suka haye Urdun zuwa ƙasar Gad da Gileyad. Shawulu ya zauna Gilgal, dukan ƙungiyoyi sojojin da suke tare da shi suka yi rawan jiki don tsoro.
Und es gingen Hebräer über den Jordan in das Land Gad und Gilead. Saul aber war noch in Gilgal und alles Volk hinter ihm erzitterte.
8 Ya jira har kwana bakwai bisa ga lokacin da Sama’ila ya bayar. Amma Sama’ila bai zo Gilgal ba, mutanen Shawulu suka fara watsewa.
Und es wartete sieben Tage, bis zu der Zeit, die Samuel bestimmt hatte. Aber Samuel kam nicht nach Gilgal und das Volk zerstreute sich von ihm.
9 Sai ya ce, “Ku kawo mini hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama.” Sai Shawulu ya miƙa hadaya ta ƙonawa.
Und Saul sprach: Bringt mir das Brandopfer und die Dankopfer herbei; und er opferte das Brandopfer auf.
10 Daidai yana gama miƙa hadaya ke nan sai Sama’ila ya iso. Shawulu kuma ya fito domin yă yi masa maraba.
Und es geschah, als er das Brandopfer aufzuopfern vollendet hatte, siehe, da kam Samuel, und Saul ging hinaus, ihm entgegen, daß er ihn segne.
11 Sama’ila ya ce, “Me ke nan ka yi?” Shawulu ya ce, “Sa’ad da na ga mutane suna watsewa, kai kuwa ba ka zo cikin lokaci ba, ga Filistiyawa kuma suna taruwa a Mikmash,
Und Samuel sprach: Was hast du getan? Und Saul sprach: Weil ich sah, daß das Volk sich von mir zerstreute, und du zur bestimmten Zeit der Tage nicht kamst, und die Philister in Michmasch sich versammelten;
12 sai na yi tunani cewa, ‘Yanzu Filistiyawa za su gangaro su fāɗa mini a Gilgal, ga ni kuma ban riga na nemi nufin Ubangiji ba.’ Shi ya sa ya zama mini tilas in miƙa hadaya ta ƙonawa.”
Und ich sprach: Jetzt werden die Philister wider mich nach Gilgal herabkommen, und ich habe das Angesicht Jehovahs noch nicht angefleht; da hielt ich an mich und opferte das Brandopfer auf.
13 Sama’ila ya ce, “Ka yi wauta da ba ka bi umarnin da Ubangiji Allahnka ya ba ka ba. Da ka yi haka da Ubangiji ya tabbatar maka da sarautar Isra’ila har abada.
Samuel aber sprach zu Saul: Du hast närrisch gehandelt, du hast das Gebot Jehovahs, deines Gottes, das Er dir geboten, nicht gehalten; denn jetzt hätte Jehovah dein Königtum über Israel auf ewig befestigt.
14 Amma yanzu, masarautarka ba za tă dawwama ba, Ubangiji ya riga ya sami wani wanda zuciyarsa ke ƙauna, ya naɗa shi shugaban mutanensa gama ba ka bi umarnin Ubangiji ba.”
Nun aber wird dein Königtum nicht bestätigt. Jehovah hat Sich einen Mann nach Seinem Herzen gesucht, und Jehovah hat ihm geboten, Führer zu sein über Sein Volk, weil du nicht gehalten hast, was Jehovah dir gebot.
15 Sama’ila ya tashi daga Gilgal ya tafi Gibeya a ƙasar Benyamin. Shawulu kuma ya ƙidaya mutanen da suke tare da shi, yawansu ya kai wajen mutum ɗari shida.
Und Samuel machte sich auf und ging hinauf von Gilgal nach Gibeah-Benjamin; Saul aber musterte das Volk, das sich bei ihm fand, bei sechshundert Mann.
16 Shawulu da ɗansa Yonatan da mutanen da suke tare da shi suka zauna a Geba ta Benyamin. Sa’an nan Filistiyawa suka yi sansani a Mikmash.
Und Saul und Jonathan, sein Sohn, und das Volk, das sich bei ihnen fand, lagen in Geba-Benjamin, die Philister aber lagerten in Michmasch.
17 Rundunar mayaƙa uku suka fito daga sansani Filistiyawa. Ɗaya ta nufi Ofra, zuwa ƙasar Shuwal.
Und es ging ein Verheerungszug aus dem Lager der Philister in drei Haufen aus. Ein Haufe wandte sich auf den Weg nach Ophrah zum Lande Schual;
18 Runduna guda kuma ta nufi Bet-Horon, ɗayan kuwa ta nufi iyakar da take fuskantar Kwarin Ziboyim wajen jeji.
Und ein Haufe wandte sich auf den Weg nach Beth-Choron, und ein Haufe wandte sich auf den Weg nach der Grenze, die hinschaut über die Schlucht Zeboim nach der Wüste zu.
19 Ba a sami maƙeri ɗaya a dukan ƙasar Isra’ila ba domin Filistiyawa sun ce, “In ba haka ba Ibraniyawa za su ƙera wa kansu takuba ko māsu.”
Es fand sich aber im ganzen Lande Israel kein Schmied, denn die Philister sagten: Damit die Hebräer sich weder Schwert noch Spieß machen.
20 Saboda haka dukan Isra’ila sukan gangara zuwa wajen Filistiyawa domin su gyara bakin garemaninsu, da fartanansu, da gaturansu, da kuma laujunansu.
Und ganz Israel ging zu den Philistern hinab, wenn ein Mann seine Pflugschar und seine Hacke und seine Axt und seine Sichel wollte schmieden lassen.
21 Duk lokacin da za su gyara bakin garmansu da fartanyarsu sai sun biya tsabar azurfa biyu. Haka ma idan za su gyara gatari ko bakunan abin korar shanun noma sai sun biya tsabar azurfa ɗaya.
Und es waren Scharten an den Schneiden der Pflugscharen und der Hacken und der Dreizacken und der Äxte, und die Ochsenstacheln waren zu spitzen.
22 A ranar da yaƙi ya tashi, ba a sami wanda yake da takobi ko māshi ba a cikin mutanen da suke tare da Shawulu da Yonatan. Sai dai Shawulu da ɗansa Yonatan kaɗai.
Und am Tage des Streites fand sich weder Schwert noch Spieß in der Hand des ganzen Volkes, das mit Saul und Jonathan war, aber bei Saul und seinem Sohne Jonathan fanden sie sich.
23 Ana nan sai sojojin Filistiyawa suka fita zuwa mashigin Mikmash.
Und der Posten der Philister zog aus nach dem Passe von Michmasch.