< 1 Sama’ila 13 >

1 Shawulu yana da shekara talatin sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi sarautar Isra’ila shekara arba’in da biyu.
Après cela, Saül choisit trois mille hommes, parmi ceux d'Israël. Il y en eut avec lui deux mille à Machmas et en la montagne de Béthel, et avec Jonathan mille, à Gabaa en Benjamin. Le reste du peuple fut congédié, et chacun retourna en sa demeure.
2 Sai ya zaɓi sojoji dubu uku daga jama’ar Isra’ila. Ya keɓe dubu biyu su kasance tare da shi a Mikmash da kuma a tuddan yankin Betel. Ya kuma bar dubu ɗaya tare da ɗansa Yonatan a Gibeya a yankin zuriyar Benyamin. Sauran sojojin kuwa Shawulu ya sallame su su koma gidajensu.
Après cela, Saül choisit trois mille hommes, parmi ceux d'Israël. Il y en eut avec lui deux mille à Machmas et en la montagne de Béthel, et avec Jonathan mille, à Gabaa en Benjamin. Le reste du peuple fut congédié, et chacun retourna en sa demeure.
3 Yonatan ya kai wa Filistiyawa hari a Geba, sai Filistiyawa suka sami labarin. Sai Shawulu ya sa aka busa ƙaho ko’ina a ƙasar ya ce, “Bari Ibraniyawa su ji!”
Jonathan battit le Nasib, étranger qui demeurait sur la colline; les Philistins l'apprirent, et Saül fit retentir la trompette en toute la terre promise, disant: Les esclaves secouent le joug.
4 Haka kuwa dukan Isra’ila suka ji labari cewa, “Shawulu ya kai hari a ƙasar Filistiyawa, yanzu Isra’ila ta zama abin ƙi ga Filistiyawa.” Aka kira mutane su haɗu da Shawulu a Gilgal.
Et tout Israël écouta ceux qui publiaient: Saül a détruit le Nasib étranger; et Israël se souleva contre les Philistins, et tous les fils d'Israël suivirent Saül en Galgala.
5 Sai Filistiyawa suka taru don su yi yaƙi da Isra’ilawa. Suka fito da kekunan-dawakan yaƙi dubu talatin, da masu hawan dawakai dubu shida, da sojoji masu yawa kamar yashi a bakin teku. Suka tafi Mikmash a gabashin Bet-Awen, suka kafa sansani a can.
Cependant, les Philistins se réunirent pour porter la guerre en Israël; ils firent marcher contre Israël trente mille chars, six mille cavaliers et des piétons nombreux comme le sable de la mer; ils campèrent à Machmas, en face de Béthoron du Midi.
6 Sa’ad da Filistiyawa suka fāɗa wa Isra’ilawa da yaƙi mai tsanani, suka sa su cikin wani hali mai wuya, sai Isra’ilawa suka ɓuya a kogwanni, da ciyayi, da duwatsu, da ramummuka, da rijiyoyi.
Or, Israël vit qu'il était trop faible pour les aborder; et le peuple se cacha dans les cavernes, dans les lieux fermés, dans les rochers, dans les puits, dans les citernes.
7 Waɗansunsu ma suka haye Urdun zuwa ƙasar Gad da Gileyad. Shawulu ya zauna Gilgal, dukan ƙungiyoyi sojojin da suke tare da shi suka yi rawan jiki don tsoro.
Ceux qui avaient passé le Jourdain le traversèrent encore pour se réfugier dans les territoires de Gad et de Galaad. Et Saül était encore à Galgala, et toute la troupe qui le suivait était frappée d'effroi.
8 Ya jira har kwana bakwai bisa ga lokacin da Sama’ila ya bayar. Amma Sama’ila bai zo Gilgal ba, mutanen Shawulu suka fara watsewa.
Il laissa écouler sept jours, comme le lui avait dit Samuel; mais Samuel ne vint pas le trouver en Galgala, et la troupe qui l'entourait se dispersa.
9 Sai ya ce, “Ku kawo mini hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama.” Sai Shawulu ya miƙa hadaya ta ƙonawa.
Et Saül dit: Amenez ici des victimes pour que je prépare un holocauste et des hosties pacifiques; puis, il offrit l'holocauste.
10 Daidai yana gama miƙa hadaya ke nan sai Sama’ila ya iso. Shawulu kuma ya fito domin yă yi masa maraba.
Comme il achevait le sacrifice, Samuel arriva, et Saül sortit à sa rencontre afin de lui rendre hommage.
11 Sama’ila ya ce, “Me ke nan ka yi?” Shawulu ya ce, “Sa’ad da na ga mutane suna watsewa, kai kuwa ba ka zo cikin lokaci ba, ga Filistiyawa kuma suna taruwa a Mikmash,
Et Samuel dit: Qu'as-tu fait? Et Saül répondit: J'ai vu que le peuple autour de moi se dispersait, que tu n'étais point venu au temps indiqué, et que les Philistins étaient réunis à Machmas,
12 sai na yi tunani cewa, ‘Yanzu Filistiyawa za su gangaro su fāɗa mini a Gilgal, ga ni kuma ban riga na nemi nufin Ubangiji ba.’ Shi ya sa ya zama mini tilas in miƙa hadaya ta ƙonawa.”
Et j'ai dit: Maintenant les Philistins vont descendre sur moi à Galgala et je n'ai point prié devant le Seigneur: je me suis donc résolu à offrir l'holocauste.
13 Sama’ila ya ce, “Ka yi wauta da ba ka bi umarnin da Ubangiji Allahnka ya ba ka ba. Da ka yi haka da Ubangiji ya tabbatar maka da sarautar Isra’ila har abada.
Et Samuel dit à Saül: Tu as agi en insensé, car tu n'as point obéi à mon ordre, à l'ordre du Seigneur, au moment où le Seigneur t'avait préparé sur son peuple une royauté perpétuelle.
14 Amma yanzu, masarautarka ba za tă dawwama ba, Ubangiji ya riga ya sami wani wanda zuciyarsa ke ƙauna, ya naɗa shi shugaban mutanensa gama ba ka bi umarnin Ubangiji ba.”
Maintenant donc cette royauté ne te restera pas, et Dieu se cherchera un homme selon son cœur; et le Seigneur le chargera de gouverner son peuple, parce que tu n'as pas observé le commandement du Seigneur.
15 Sama’ila ya tashi daga Gilgal ya tafi Gibeya a ƙasar Benyamin. Shawulu kuma ya ƙidaya mutanen da suke tare da shi, yawansu ya kai wajen mutum ɗari shida.
Et Samuel partit, il quitta Galgala, et ce qu'il y avait encore là de peuple suivit Saül pour rejoindre les hommes de guerre. Quand ils furent arrivés de Galgala en Gabaa, Saül passa en revue la troupe qui se trouvait avec lui; elle était réduite à six cents hommes.
16 Shawulu da ɗansa Yonatan da mutanen da suke tare da shi suka zauna a Geba ta Benyamin. Sa’an nan Filistiyawa suka yi sansani a Mikmash.
Et Saül, avec son fils Jonathan et la troupe qui les avait suivis, s'arrêta à Gabaa en Benjamin, où tous pleurèrent; cependant les Philistins étaient campés à Machmas.
17 Rundunar mayaƙa uku suka fito daga sansani Filistiyawa. Ɗaya ta nufi Ofra, zuwa ƙasar Shuwal.
Et ceux-ci, portant avec eux le ravage, sortirent de leur camp en trois troupes: l'une prit le chemin de Gophera sur le territoire de Sogal.
18 Runduna guda kuma ta nufi Bet-Horon, ɗayan kuwa ta nufi iyakar da take fuskantar Kwarin Ziboyim wajen jeji.
Une autre prit la route de Béthoron; la troisième, le chemin de Gabaa, qui fait un détour vers Haï des Sabim.
19 Ba a sami maƙeri ɗaya a dukan ƙasar Isra’ila ba domin Filistiyawa sun ce, “In ba haka ba Ibraniyawa za su ƙera wa kansu takuba ko māsu.”
Et, sur tout le territoire d'Israël, on ne trouvait pas un seul forgeron, parce que les Philistins avaient dit: Il ne faut pas que les Hébreux fabriquent lance ou épée.
20 Saboda haka dukan Isra’ila sukan gangara zuwa wajen Filistiyawa domin su gyara bakin garemaninsu, da fartanansu, da gaturansu, da kuma laujunansu.
Et tout Israël descendait chez les Philistins pour forger chacun sa faucille, ses outils, sa hache ou sa faux.
21 Duk lokacin da za su gyara bakin garmansu da fartanyarsu sai sun biya tsabar azurfa biyu. Haka ma idan za su gyara gatari ko bakunan abin korar shanun noma sai sun biya tsabar azurfa ɗaya.
On était près de vendanger; or, pour un outil à dents, il fallait payer trois sicles, et autant pour une hache ou pour une faux.
22 A ranar da yaƙi ya tashi, ba a sami wanda yake da takobi ko māshi ba a cikin mutanen da suke tare da Shawulu da Yonatan. Sai dai Shawulu da ɗansa Yonatan kaɗai.
Et, dans les jours de la guerre de Machmas, on ne trouva pas une épée ni une lance dans la main de l'un des fils d'Israël qui accompagnaient Saül et Jonathan; on n'en eût trouvé que dans les mains du roi et de son fils.
23 Ana nan sai sojojin Filistiyawa suka fita zuwa mashigin Mikmash.
Cependant, des Philistins étaient sortis du côté opposé au camp de Machmas.

< 1 Sama’ila 13 >