< 1 Sama’ila 13 >
1 Shawulu yana da shekara talatin sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi sarautar Isra’ila shekara arba’in da biyu.
Saul was — years old when he began to reign; and two years he reigned over Israel.
2 Sai ya zaɓi sojoji dubu uku daga jama’ar Isra’ila. Ya keɓe dubu biyu su kasance tare da shi a Mikmash da kuma a tuddan yankin Betel. Ya kuma bar dubu ɗaya tare da ɗansa Yonatan a Gibeya a yankin zuriyar Benyamin. Sauran sojojin kuwa Shawulu ya sallame su su koma gidajensu.
And Saul chose him three thousand men of Israel; whereof two thousand were with Saul in Michmas and in the mount of Beth-el, and a thousand were with Jonathan in Gibeath-benjamin; and the rest of the people he sent every man to his tent.
3 Yonatan ya kai wa Filistiyawa hari a Geba, sai Filistiyawa suka sami labarin. Sai Shawulu ya sa aka busa ƙaho ko’ina a ƙasar ya ce, “Bari Ibraniyawa su ji!”
And Jonathan smote the garrison of the Philistines that was in Geba, and the Philistines heard of it. And Saul blew the horn throughout all the land, saying: 'Let the Hebrews hear.'
4 Haka kuwa dukan Isra’ila suka ji labari cewa, “Shawulu ya kai hari a ƙasar Filistiyawa, yanzu Isra’ila ta zama abin ƙi ga Filistiyawa.” Aka kira mutane su haɗu da Shawulu a Gilgal.
And all Israel heard say that Saul had smitten the garrison of the Philistines, and that Israel also had made himself odious with the Philistines. And the people were gathered together after Saul to Gilgal.
5 Sai Filistiyawa suka taru don su yi yaƙi da Isra’ilawa. Suka fito da kekunan-dawakan yaƙi dubu talatin, da masu hawan dawakai dubu shida, da sojoji masu yawa kamar yashi a bakin teku. Suka tafi Mikmash a gabashin Bet-Awen, suka kafa sansani a can.
And the Philistines assembled themselves together to fight with Israel, thirty thousand chariots, and six thousand horsemen, and people as the sand which is on the sea-shore in multitude; and they came up, and pitched in Michmas, eastward of Beth-aven.
6 Sa’ad da Filistiyawa suka fāɗa wa Isra’ilawa da yaƙi mai tsanani, suka sa su cikin wani hali mai wuya, sai Isra’ilawa suka ɓuya a kogwanni, da ciyayi, da duwatsu, da ramummuka, da rijiyoyi.
When the men of Israel saw that they were in a strait — for the people were distressed — then the people did hide themselves in caves, and in thickets, and in rocks, and in holds, and in pits.
7 Waɗansunsu ma suka haye Urdun zuwa ƙasar Gad da Gileyad. Shawulu ya zauna Gilgal, dukan ƙungiyoyi sojojin da suke tare da shi suka yi rawan jiki don tsoro.
Now some of the Hebrews had gone over the Jordan to the land of Gad and Gilead; but as for Saul, he was yet in Gilgal, and all the people followed him trembling.
8 Ya jira har kwana bakwai bisa ga lokacin da Sama’ila ya bayar. Amma Sama’ila bai zo Gilgal ba, mutanen Shawulu suka fara watsewa.
And he tarried seven days, according to the set time that Samuel had appointed; but Samuel came not to Gilgal; and the people were scattered from him.
9 Sai ya ce, “Ku kawo mini hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama.” Sai Shawulu ya miƙa hadaya ta ƙonawa.
And Saul said: 'Bring hither to me the burnt-offering and the peace-offerings.' And he offered the burnt-offering.
10 Daidai yana gama miƙa hadaya ke nan sai Sama’ila ya iso. Shawulu kuma ya fito domin yă yi masa maraba.
And it came to pass that, as soon as he had made an end of offering the burnt-offering, behold, Samuel came; and Saul went out to meet him, that he might salute him.
11 Sama’ila ya ce, “Me ke nan ka yi?” Shawulu ya ce, “Sa’ad da na ga mutane suna watsewa, kai kuwa ba ka zo cikin lokaci ba, ga Filistiyawa kuma suna taruwa a Mikmash,
And Samuel said: 'What hast thou done?' And Saul said: 'Because I saw that the people were scattered from me, and that thou camest not within the days appointed, and that the Philistines assembled themselves together against Michmas;
12 sai na yi tunani cewa, ‘Yanzu Filistiyawa za su gangaro su fāɗa mini a Gilgal, ga ni kuma ban riga na nemi nufin Ubangiji ba.’ Shi ya sa ya zama mini tilas in miƙa hadaya ta ƙonawa.”
therefore said I: Now will the Philistines come down upon me to Gilgal, and I have not entreated the favour of the LORD; I forced myself therefore, and offered the burnt-offering.'
13 Sama’ila ya ce, “Ka yi wauta da ba ka bi umarnin da Ubangiji Allahnka ya ba ka ba. Da ka yi haka da Ubangiji ya tabbatar maka da sarautar Isra’ila har abada.
And Samuel said to Saul: 'Thou hast done foolishly; thou hast not kept the commandment of the LORD thy God, which He commanded thee; for now would the LORD have established thy kingdom upon Israel for ever.
14 Amma yanzu, masarautarka ba za tă dawwama ba, Ubangiji ya riga ya sami wani wanda zuciyarsa ke ƙauna, ya naɗa shi shugaban mutanensa gama ba ka bi umarnin Ubangiji ba.”
But now thy kingdom shall not continue; the LORD hath sought him a man after His own heart, and the LORD hath appointed him to be prince over His people, because thou hast not kept that which the LORD commanded thee.'
15 Sama’ila ya tashi daga Gilgal ya tafi Gibeya a ƙasar Benyamin. Shawulu kuma ya ƙidaya mutanen da suke tare da shi, yawansu ya kai wajen mutum ɗari shida.
And Samuel arose, and got him up from Gilgal unto Gibeath-benjamin. And Saul numbered the people that were present with him, about six hundred men.
16 Shawulu da ɗansa Yonatan da mutanen da suke tare da shi suka zauna a Geba ta Benyamin. Sa’an nan Filistiyawa suka yi sansani a Mikmash.
And Saul, and Jonathan his son, and the people that were present with them, abode in Gibeath-benjamin; but the Philistines encamped in Michmas.
17 Rundunar mayaƙa uku suka fito daga sansani Filistiyawa. Ɗaya ta nufi Ofra, zuwa ƙasar Shuwal.
And the spoilers came out of the camp of the Philistines in three companies: one company turned unto the way that leadeth to Ophrah, unto the land of Shual;
18 Runduna guda kuma ta nufi Bet-Horon, ɗayan kuwa ta nufi iyakar da take fuskantar Kwarin Ziboyim wajen jeji.
and another company turned the way to Beth-horon; and another company turned the way of the border that looketh down upon the valley of Zeboim toward the wilderness.
19 Ba a sami maƙeri ɗaya a dukan ƙasar Isra’ila ba domin Filistiyawa sun ce, “In ba haka ba Ibraniyawa za su ƙera wa kansu takuba ko māsu.”
Now there was no smith found throughout all the land of Israel; for the Philistines said: 'Lest the Hebrews make them swords or spears';
20 Saboda haka dukan Isra’ila sukan gangara zuwa wajen Filistiyawa domin su gyara bakin garemaninsu, da fartanansu, da gaturansu, da kuma laujunansu.
but all the Israelites went down to the Philistines, to sharpen every man his plowshare, and his coulter, and his axe, and his mattock.
21 Duk lokacin da za su gyara bakin garmansu da fartanyarsu sai sun biya tsabar azurfa biyu. Haka ma idan za su gyara gatari ko bakunan abin korar shanun noma sai sun biya tsabar azurfa ɗaya.
And the price of the filing was a pim for the mattocks, and for the coulters, and for the forks with three teeth, and for the axes; and to set the goads.
22 A ranar da yaƙi ya tashi, ba a sami wanda yake da takobi ko māshi ba a cikin mutanen da suke tare da Shawulu da Yonatan. Sai dai Shawulu da ɗansa Yonatan kaɗai.
So it came to pass in the day of battle, that there was neither sword nor spear found in the hand of any of the people that were with Saul and Jonathan; but with Saul and with Jonathan his son was there found.
23 Ana nan sai sojojin Filistiyawa suka fita zuwa mashigin Mikmash.
And the garrison of the Philistines went out unto the pass of Michmas.