< 1 Sama’ila 13 >

1 Shawulu yana da shekara talatin sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi sarautar Isra’ila shekara arba’in da biyu.
Saul was a child of one year when he began to reign, and he reigned two years over Israel.
2 Sai ya zaɓi sojoji dubu uku daga jama’ar Isra’ila. Ya keɓe dubu biyu su kasance tare da shi a Mikmash da kuma a tuddan yankin Betel. Ya kuma bar dubu ɗaya tare da ɗansa Yonatan a Gibeya a yankin zuriyar Benyamin. Sauran sojojin kuwa Shawulu ya sallame su su koma gidajensu.
And Saul chose him three thousand men of Israel: and two thousand were with Saul in Machmas, and in mount Bethel: and a thousand with Jonathan in Gabaa of Benjamin, and the rest of the people he sent back every man to their dwellings.
3 Yonatan ya kai wa Filistiyawa hari a Geba, sai Filistiyawa suka sami labarin. Sai Shawulu ya sa aka busa ƙaho ko’ina a ƙasar ya ce, “Bari Ibraniyawa su ji!”
And Jonathan smote the garrison of the Philistines which was in Gabaa. And when the Philistines had heard of it, Saul sounded the trumpet over all the land, saying: Let the Hebrews hear.
4 Haka kuwa dukan Isra’ila suka ji labari cewa, “Shawulu ya kai hari a ƙasar Filistiyawa, yanzu Isra’ila ta zama abin ƙi ga Filistiyawa.” Aka kira mutane su haɗu da Shawulu a Gilgal.
And all Israel heard this report: Saul hath smitten the garrison of the Philistines: and Israel took courage against the Philistines. And the people were called together after Saul to Galgal.
5 Sai Filistiyawa suka taru don su yi yaƙi da Isra’ilawa. Suka fito da kekunan-dawakan yaƙi dubu talatin, da masu hawan dawakai dubu shida, da sojoji masu yawa kamar yashi a bakin teku. Suka tafi Mikmash a gabashin Bet-Awen, suka kafa sansani a can.
The Philistines also were assembled to fight against Israel, thirty thousand chariots, and six thousand horsemen, and a multitude of people besides, like the sand on the sea shore for number. And going up they camped in Machmas at the east of Bethaven.
6 Sa’ad da Filistiyawa suka fāɗa wa Isra’ilawa da yaƙi mai tsanani, suka sa su cikin wani hali mai wuya, sai Isra’ilawa suka ɓuya a kogwanni, da ciyayi, da duwatsu, da ramummuka, da rijiyoyi.
And when the men of Israel saw that they were straitened, (for the people were distressed, ) they hid themselves in caves, and in thickets, and in rocks, and in dens, and in pits.
7 Waɗansunsu ma suka haye Urdun zuwa ƙasar Gad da Gileyad. Shawulu ya zauna Gilgal, dukan ƙungiyoyi sojojin da suke tare da shi suka yi rawan jiki don tsoro.
And some of the Hebrews passed over the Jordan into the land of Gad and Galaad. And when Saul was yet in Galgal, all the people that followed him were greatly afraid.
8 Ya jira har kwana bakwai bisa ga lokacin da Sama’ila ya bayar. Amma Sama’ila bai zo Gilgal ba, mutanen Shawulu suka fara watsewa.
And he waited seven days according to the appointment of Samuel, I and Samuel came not to Galgal, and the people slipt away from him.
9 Sai ya ce, “Ku kawo mini hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama.” Sai Shawulu ya miƙa hadaya ta ƙonawa.
Then Saul said: Bring me the holocaust, and the peace offerings. And he offered the holocaust.
10 Daidai yana gama miƙa hadaya ke nan sai Sama’ila ya iso. Shawulu kuma ya fito domin yă yi masa maraba.
And when he had made an end of offering the holocaust, behold Samuel came: and Saul went forth to meet him and salute him.
11 Sama’ila ya ce, “Me ke nan ka yi?” Shawulu ya ce, “Sa’ad da na ga mutane suna watsewa, kai kuwa ba ka zo cikin lokaci ba, ga Filistiyawa kuma suna taruwa a Mikmash,
And Samuel said to him: What hast thou done? Saul answered: Because I saw that the people slipt from me, and thou wast not come according to the days appointed, and the Philistines were gathered together in Machmas,
12 sai na yi tunani cewa, ‘Yanzu Filistiyawa za su gangaro su fāɗa mini a Gilgal, ga ni kuma ban riga na nemi nufin Ubangiji ba.’ Shi ya sa ya zama mini tilas in miƙa hadaya ta ƙonawa.”
I said: Now will the Philistines come down upon me to Galgal, and I have not appeased the face of the Lord. Forced by necessity, I offered the holocaust.
13 Sama’ila ya ce, “Ka yi wauta da ba ka bi umarnin da Ubangiji Allahnka ya ba ka ba. Da ka yi haka da Ubangiji ya tabbatar maka da sarautar Isra’ila har abada.
And Samuel said to Saul: Thou hast done foolishly, and hast not kept the commandments of the Lord thy God, which he commanded thee. And if thou hadst not done thus, the Lord would now have established thy kingdom over Israel for ever.
14 Amma yanzu, masarautarka ba za tă dawwama ba, Ubangiji ya riga ya sami wani wanda zuciyarsa ke ƙauna, ya naɗa shi shugaban mutanensa gama ba ka bi umarnin Ubangiji ba.”
But thy kingdom shall not continue. The Lord hath sought him a man according to his own heart: and him hath the Lord commanded to be prince over his people, because thou hast not observed that which the Lord commanded.
15 Sama’ila ya tashi daga Gilgal ya tafi Gibeya a ƙasar Benyamin. Shawulu kuma ya ƙidaya mutanen da suke tare da shi, yawansu ya kai wajen mutum ɗari shida.
And Samuel arose and went up from Galgal to Gabaa of Benjamin. And the rest of the people went up after Saul, to meet the people who fought against them, going from Galgal to Gabaa in the hill of Benjamin. And Saul numbered the people, that were found with him, about six hundred men.
16 Shawulu da ɗansa Yonatan da mutanen da suke tare da shi suka zauna a Geba ta Benyamin. Sa’an nan Filistiyawa suka yi sansani a Mikmash.
And Saul and Jonathan his son, and the people that were present with them, were in Gabaa of Benjamin: but the Philistines encamped in Machmas.
17 Rundunar mayaƙa uku suka fito daga sansani Filistiyawa. Ɗaya ta nufi Ofra, zuwa ƙasar Shuwal.
And there went out of the camp of the Philistines three companies to plunder. One company went towards the way of Ephra to the land of Sual;
18 Runduna guda kuma ta nufi Bet-Horon, ɗayan kuwa ta nufi iyakar da take fuskantar Kwarin Ziboyim wajen jeji.
And another went by the way of Beth-horon, and the third turned to the way of the border, above the valley of Seboim towards the desert.
19 Ba a sami maƙeri ɗaya a dukan ƙasar Isra’ila ba domin Filistiyawa sun ce, “In ba haka ba Ibraniyawa za su ƙera wa kansu takuba ko māsu.”
Now there was no smith to be found in all the land of Israel, for the Philistines had taken this precaution, lest the Hebrews should make them swords or spears.
20 Saboda haka dukan Isra’ila sukan gangara zuwa wajen Filistiyawa domin su gyara bakin garemaninsu, da fartanansu, da gaturansu, da kuma laujunansu.
So all Israel went down to the Philistines, to sharpen every man his ploughshare, and his spade, and his axe, and his rake.
21 Duk lokacin da za su gyara bakin garmansu da fartanyarsu sai sun biya tsabar azurfa biyu. Haka ma idan za su gyara gatari ko bakunan abin korar shanun noma sai sun biya tsabar azurfa ɗaya.
So that their shares, and their spades, and their forks, and their axes were blunt, even to the goad, which was to be mended.
22 A ranar da yaƙi ya tashi, ba a sami wanda yake da takobi ko māshi ba a cikin mutanen da suke tare da Shawulu da Yonatan. Sai dai Shawulu da ɗansa Yonatan kaɗai.
And when the day of battle was come, there was neither sword nor spear found in the hand of any of the people that were with Saul and Jonathan, except Saul and Jonathan his son.
23 Ana nan sai sojojin Filistiyawa suka fita zuwa mashigin Mikmash.
And the army of the Philistines went out in order to advance further in Machmas.

< 1 Sama’ila 13 >