< 1 Sama’ila 13 >

1 Shawulu yana da shekara talatin sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi sarautar Isra’ila shekara arba’in da biyu.
Šaulu je bilo ... godina kad je postao kralj, a kraljevao je ... i dvije godine nad Izraelom.
2 Sai ya zaɓi sojoji dubu uku daga jama’ar Isra’ila. Ya keɓe dubu biyu su kasance tare da shi a Mikmash da kuma a tuddan yankin Betel. Ya kuma bar dubu ɗaya tare da ɗansa Yonatan a Gibeya a yankin zuriyar Benyamin. Sauran sojojin kuwa Shawulu ya sallame su su koma gidajensu.
Šaul izabra sebi tri tisuće Izraelaca: dvije tisuće od njih bijahu sa Šaulom u Mikmasu i u Betelskoj gori, a jedna tisuća bijaše s Jonatanom u Benjaminovoj Gebi. Ostali je narod Šaul otpustio svakoga u njegov šator.
3 Yonatan ya kai wa Filistiyawa hari a Geba, sai Filistiyawa suka sami labarin. Sai Shawulu ya sa aka busa ƙaho ko’ina a ƙasar ya ce, “Bari Ibraniyawa su ji!”
Jonatan sruši filistejski stup koji je stajao u Gibei i Filistejci saznaše da su se Hebreji pobunili. Šaul zapovjedi te zatrubiše u rog po svoj zemlji
4 Haka kuwa dukan Isra’ila suka ji labari cewa, “Shawulu ya kai hari a ƙasar Filistiyawa, yanzu Isra’ila ta zama abin ƙi ga Filistiyawa.” Aka kira mutane su haɗu da Shawulu a Gilgal.
i sav Izrael doznade novost: “Šaul je srušio filistejski stup, Izrael se omrazio Filistejcima!” I narod se poče skupljati oko Šaula u Gilgalu.
5 Sai Filistiyawa suka taru don su yi yaƙi da Isra’ilawa. Suka fito da kekunan-dawakan yaƙi dubu talatin, da masu hawan dawakai dubu shida, da sojoji masu yawa kamar yashi a bakin teku. Suka tafi Mikmash a gabashin Bet-Awen, suka kafa sansani a can.
A Filistejci se skupiše da vojuju na Izraela: tri tisuće bojnih kola, šest tisuća konja, a mnoštvo naroda kao pijeska na morskoj obali. I utaboriše se kod Mikmasa, istočno od Bet Avena.
6 Sa’ad da Filistiyawa suka fāɗa wa Isra’ilawa da yaƙi mai tsanani, suka sa su cikin wani hali mai wuya, sai Isra’ilawa suka ɓuya a kogwanni, da ciyayi, da duwatsu, da ramummuka, da rijiyoyi.
Kad su Izraelci vidjeli da su u nevolji i da je narod pritisnut od neprijatelja, posakrivaše se u pećine, jame, kamenjake, jarke i čatrnje.
7 Waɗansunsu ma suka haye Urdun zuwa ƙasar Gad da Gileyad. Shawulu ya zauna Gilgal, dukan ƙungiyoyi sojojin da suke tare da shi suka yi rawan jiki don tsoro.
Neki su prešli i preko gazova Jordana u zemlju Gadovu i Gileadovu. Šaul je još bio u Gilgalu, a sav je narod oko njega drhtao od straha.
8 Ya jira har kwana bakwai bisa ga lokacin da Sama’ila ya bayar. Amma Sama’ila bai zo Gilgal ba, mutanen Shawulu suka fara watsewa.
On pričeka sedam dana kako mu je odredio Samuel; ali kad Samuel nije došao u Gilgal, narod se stade razilaziti od Šaula.
9 Sai ya ce, “Ku kawo mini hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama.” Sai Shawulu ya miƙa hadaya ta ƙonawa.
Tada reče Šaul: “Donesite mi žrtvu paljenicu i žrtve pričesnice!” I prinese žrtvu paljenicu.
10 Daidai yana gama miƙa hadaya ke nan sai Sama’ila ya iso. Shawulu kuma ya fito domin yă yi masa maraba.
I upravo je završavao žrtvu paljenicu, kad eto Samuela; Šaul mu iziđe u susret da ga pozdravi.
11 Sama’ila ya ce, “Me ke nan ka yi?” Shawulu ya ce, “Sa’ad da na ga mutane suna watsewa, kai kuwa ba ka zo cikin lokaci ba, ga Filistiyawa kuma suna taruwa a Mikmash,
Samuel ga upita: “Što si učinio?” A Šaul odgovori: “Kad sam vidio da se narod razilazi od mene, a ti da ne dolaziš do određenoga dana, a Filistejci se skupili u Mikmasu,
12 sai na yi tunani cewa, ‘Yanzu Filistiyawa za su gangaro su fāɗa mini a Gilgal, ga ni kuma ban riga na nemi nufin Ubangiji ba.’ Shi ya sa ya zama mini tilas in miƙa hadaya ta ƙonawa.”
pomislio sam: sad će udariti Filistejci na me u Gilgalu, a ja neću stići molitvom ublažiti Jahvu! Zato se odvažih i prinesoh žrtvu paljenicu.”
13 Sama’ila ya ce, “Ka yi wauta da ba ka bi umarnin da Ubangiji Allahnka ya ba ka ba. Da ka yi haka da Ubangiji ya tabbatar maka da sarautar Isra’ila har abada.
Samuel tada reče Šaulu: “Ludo si radio! Da si održao zapovijed koju ti je dao Jahve, tvoj Bog, Jahve bi učvrstio tvoje kraljevstvo nad Izraelom dovijeka.
14 Amma yanzu, masarautarka ba za tă dawwama ba, Ubangiji ya riga ya sami wani wanda zuciyarsa ke ƙauna, ya naɗa shi shugaban mutanensa gama ba ka bi umarnin Ubangiji ba.”
A sada se tvoje kraljevstvo neće trajno održati: Jahve je potražio sebi čovjeka po svom srcu i odredio ga za kneza nad svojim narodom, jer ti nisi održao što ti je Jahve zapovjedio.”
15 Sama’ila ya tashi daga Gilgal ya tafi Gibeya a ƙasar Benyamin. Shawulu kuma ya ƙidaya mutanen da suke tare da shi, yawansu ya kai wajen mutum ɗari shida.
Nato Samuel ustade i ode iz Gilgala svojim putem. Što je naroda ostalo, pođe za Šaulom u susret ratnicima. Kad su došli iz Gilgala u Gebu Benjaminovu, Šaul pobroji narod koji je ostao uza nj i bijaše ga oko šest stotina ljudi.
16 Shawulu da ɗansa Yonatan da mutanen da suke tare da shi suka zauna a Geba ta Benyamin. Sa’an nan Filistiyawa suka yi sansani a Mikmash.
Šaul i sin mu Jonatan s ljudima što bijahu s njima zaposjeli su Benjaminovu Gebu, a Filistejci se utaborili u Mikmasu.
17 Rundunar mayaƙa uku suka fito daga sansani Filistiyawa. Ɗaya ta nufi Ofra, zuwa ƙasar Shuwal.
Tada iz filistejskog tabora izađe četa pljačkaša u tri odjela: jedan odio udari prema Ofri u zemlju šualsku;
18 Runduna guda kuma ta nufi Bet-Horon, ɗayan kuwa ta nufi iyakar da take fuskantar Kwarin Ziboyim wajen jeji.
drugi odio krenu prema Bet Horonu, a treći odio udari prema Gebi koja se uz Dolinu hijena diže nad pustinjom.
19 Ba a sami maƙeri ɗaya a dukan ƙasar Isra’ila ba domin Filistiyawa sun ce, “In ba haka ba Ibraniyawa za su ƙera wa kansu takuba ko māsu.”
A po svoj zemlji Izraelovoj nije bilo kovača, jer su Filistejci rekli: “Treba sve učiniti da Hebreji ne bi pravili sebi mačeva i kopalja.”
20 Saboda haka dukan Isra’ila sukan gangara zuwa wajen Filistiyawa domin su gyara bakin garemaninsu, da fartanansu, da gaturansu, da kuma laujunansu.
Zato su svi Izraelci išli k Filistejcima ako je tko htio da prekuje svoj raonik ili motiku, svoju sjekiru ili ostan za volove.
21 Duk lokacin da za su gyara bakin garmansu da fartanyarsu sai sun biya tsabar azurfa biyu. Haka ma idan za su gyara gatari ko bakunan abin korar shanun noma sai sun biya tsabar azurfa ɗaya.
A cijena je bila dvije trećine šekela za raonike i motike, jedna trećina za oštrenje sjekire i za nasađivanje ostana.
22 A ranar da yaƙi ya tashi, ba a sami wanda yake da takobi ko māshi ba a cikin mutanen da suke tare da Shawulu da Yonatan. Sai dai Shawulu da ɗansa Yonatan kaɗai.
Tako se dogodilo da na dan bitke kod Mikmasa nitko od svega naroda koji bijaše sa Šaulom i Jonatanom nije imao ni mača ni koplja u ruci; samo ih imahu Šaul i njegov sin Jonatan.
23 Ana nan sai sojojin Filistiyawa suka fita zuwa mashigin Mikmash.
A dotle jedna straža filistejska bijaše izišla prema klancu kod Mikmasa.

< 1 Sama’ila 13 >