< 1 Sama’ila 13 >

1 Shawulu yana da shekara talatin sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi sarautar Isra’ila shekara arba’in da biyu.
Solo da lalelegele, ode 30 agoane esalu, e da hina bagade dunu hamoi. E da hina bagade hamone, Isala: ili dunu ouligilala, ode 42 baligi.
2 Sai ya zaɓi sojoji dubu uku daga jama’ar Isra’ila. Ya keɓe dubu biyu su kasance tare da shi a Mikmash da kuma a tuddan yankin Betel. Ya kuma bar dubu ɗaya tare da ɗansa Yonatan a Gibeya a yankin zuriyar Benyamin. Sauran sojojin kuwa Shawulu ya sallame su su koma gidajensu.
Solo da dunu 3,000 agoane ilegei. Dunu 2,000 agoane da hi oule Bedele goumi sogega amola Migema: se sogega. Amalu dunu l, 000 eno Solo da ea mano Yonada: ne oule masa: ne, Gibia moilai (Bediamini fi ilia soge ganodini galu) amoga asunasi. Amalu Solo da dadi gagui oda amo, ili diasua buhagima: ne sia: i.
3 Yonatan ya kai wa Filistiyawa hari a Geba, sai Filistiyawa suka sami labarin. Sai Shawulu ya sa aka busa ƙaho ko’ina a ƙasar ya ce, “Bari Ibraniyawa su ji!”
Yonada: ne da Giba sogega, Filisidini dadi gagui dunu ouligisu dunu fane legei dagoi. Filisidini dunu huluane da amo hou nabi dagoi. Amalalu, Solo da Hibulu dunu huluane gegesu amoma misa: ne sia: i. Ea sia: adole iasu dunu ilia da Isala: ili fifilai huluane nabima: ne, dalabede fulabosu.
4 Haka kuwa dukan Isra’ila suka ji labari cewa, “Shawulu ya kai hari a ƙasar Filistiyawa, yanzu Isra’ila ta zama abin ƙi ga Filistiyawa.” Aka kira mutane su haɗu da Shawulu a Gilgal.
Ilia da Isala: ili dunu huluane amo Solo da Filisidini dadi gagui ouligisu dunu fanelegei dagoi olelei. Amola Filisidini dunu da Isala: ili dunu bagade higasa, amola olelei. Amaiba: le, dunu ilia da Solo ea ili Giliga: lega masa: ne sia: si, amoga nabawene asi.
5 Sai Filistiyawa suka taru don su yi yaƙi da Isra’ilawa. Suka fito da kekunan-dawakan yaƙi dubu talatin, da masu hawan dawakai dubu shida, da sojoji masu yawa kamar yashi a bakin teku. Suka tafi Mikmash a gabashin Bet-Awen, suka kafa sansani a can.
Filisidini dunu ilia da Isala: ili dunuma gegemusa: wa: i. Ilia da hosiga hiougisu sa: liode 30,000 agoane ba: i, amola hosi da: iya fila heda: i gegesu dunu 6,000 agoane ba: i, amola dadi gagui dunu da gilisidafa idimu hamedei, hano bega: bosoda: i afae afae ea idi defele ba: i. Ilia da Migema: se moilai (amo da Beda: ifane moilaiga gusudili galu) amoga asili, ha wa: i fisisu gagui.
6 Sa’ad da Filistiyawa suka fāɗa wa Isra’ilawa da yaƙi mai tsanani, suka sa su cikin wani hali mai wuya, sai Isra’ilawa suka ɓuya a kogwanni, da ciyayi, da duwatsu, da ramummuka, da rijiyoyi.
Amalalu, Filisidini dunu da Isala: ili dunuma gasa fili, doagala: i. Gasa bagade gegebeba: le, Isala: ili dunu da bu dabe gegemu hamedei ba: i. Ilia hobeale, mogili da magufu gelabo amola uli dogoi amola gele sogebi, amola hano si amo ganodini wamoaligi.
7 Waɗansunsu ma suka haye Urdun zuwa ƙasar Gad da Gileyad. Shawulu ya zauna Gilgal, dukan ƙungiyoyi sojojin da suke tare da shi suka yi rawan jiki don tsoro.
Dunu oda da Yodane Hano degele, Ga: de amola Gilia: de ilia ouligisu soge ole amo alofele asi. Solo da Giliga: lega esalu, amola dadi gagui dunu amola eno dunu ema gilisi da bagadewane beda: ga yagugududalu.
8 Ya jira har kwana bakwai bisa ga lokacin da Sama’ila ya bayar. Amma Sama’ila bai zo Gilgal ba, mutanen Shawulu suka fara watsewa.
Solo da Sa: miuele Giliga: lega misunu sia: si amo misa: bela: le eso fesuale agoane Giliga: lega ouesalu, be Sa: miuele da hame misi. Dunu oda ilia da Solo ea mae ba: ma: ne wamo hobeale afia: i.
9 Sai ya ce, “Ku kawo mini hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama.” Sai Shawulu ya miƙa hadaya ta ƙonawa.
Amaiba: le, Solo da ilima amane sia: i, “Wadela: i Hou Dabe Ima: ne gobele salasu liligi amola Hahawane Gilisili Olofole gobele salasu liligi nama gaguli misa.” Amalalu, e da amo liligi gobele sali.
10 Daidai yana gama miƙa hadaya ke nan sai Sama’ila ya iso. Shawulu kuma ya fito domin yă yi masa maraba.
Gobele sali amo dagomu galu, Sa: miuele da doaga: i. Solo da Sa: miuele yosia: musa: amola sia: gadomusa: asi.
11 Sama’ila ya ce, “Me ke nan ka yi?” Shawulu ya ce, “Sa’ad da na ga mutane suna watsewa, kai kuwa ba ka zo cikin lokaci ba, ga Filistiyawa kuma suna taruwa a Mikmash,
Be Sa: miuele da amane sia: i, “Dia da adi hamobela: ?” Solo da adole i, “Dunu ilia da naba: le hobeale gogosa, amola di da di misunusa: ilegele sia: i amo defele hame misi. Amaia amoiwane da Filisidini dadi gagui dunu da nini doaga: la: musa: , Migema: sega gilisilala.
12 sai na yi tunani cewa, ‘Yanzu Filistiyawa za su gangaro su fāɗa mini a Gilgal, ga ni kuma ban riga na nemi nufin Ubangiji ba.’ Shi ya sa ya zama mini tilas in miƙa hadaya ta ƙonawa.”
Amaiba: le na dawa: i amo da Filisidini ilia Giliga: lega wi nama doaga: la: ma: bela: le dawa: i, amola na da ilima hasalasima: ne, Hina Godema hame adole ba: i. Amaiba: le na dawa: i, amo da gobele salasu gobele salimusa: dawa: i.”
13 Sama’ila ya ce, “Ka yi wauta da ba ka bi umarnin da Ubangiji Allahnka ya ba ka ba. Da ka yi haka da Ubangiji ya tabbatar maka da sarautar Isra’ila har abada.
“Di da gagaoulewane hamoi galu,” Sa: miuele da adole i. “Di da dia Hina Gode Ea hamoma: ne dima olelei, amo defele hame hamoi. Di da amo hamoma: ne sia: i Hina Gode Ea dima i, amo defele hamosu ganiaba, di da Isala: ili ouligili fifi asi bagade sedagila: loba.
14 Amma yanzu, masarautarka ba za tă dawwama ba, Ubangiji ya riga ya sami wani wanda zuciyarsa ke ƙauna, ya naɗa shi shugaban mutanensa gama ba ka bi umarnin Ubangiji ba.”
Be waha da dia gebewane hame ouligisa ahoanumu. Bai dia Hina Gode Ea sia: defele hame hamoi, amola Gode da Ea hanai dunu eno hogole, amo ea da hina bagade hamone Isala: ili dunu ouligimu.”
15 Sama’ila ya tashi daga Gilgal ya tafi Gibeya a ƙasar Benyamin. Shawulu kuma ya ƙidaya mutanen da suke tare da shi, yawansu ya kai wajen mutum ɗari shida.
Sa: miuele da Giliga: le yolesili asi dagoi. Solo da ea dadi gagui dunu ilima madelale gegemusa: ahoabeba: le, dunu oda da ea baligiga aligili fa: no bobogei. Ilia da Giliga: leganini Gibiaga (Bediamini ea ouligisu soge amo ganodini) amoga asili doaga: i. Solo da e fisili asi dunu amo abodele ba: i, e da ba: loba dunu da 600 agoane ba: i.
16 Shawulu da ɗansa Yonatan da mutanen da suke tare da shi suka zauna a Geba ta Benyamin. Sa’an nan Filistiyawa suka yi sansani a Mikmash.
Solo, ea mano Yonada: ne amola ea dadi gagui dunu ilia da wa: i asili Gibaga ha wa: i fisisu gaguli fi. (amo da Bediamini ea ouligibi soge amo ganodini) Be Filisidini ilia ha wa: i fisisu da Migema: sega galu.
17 Rundunar mayaƙa uku suka fito daga sansani Filistiyawa. Ɗaya ta nufi Ofra, zuwa ƙasar Shuwal.
Filisidini ilia da Migema: seganini Isala: ili dunu doaga: la: musa: udiana mogili asi. Mogili afae da Ofala moilai bai bagade (Sioule soge ganodini) amoga doagala: musa: asi,
18 Runduna guda kuma ta nufi Bet-Horon, ɗayan kuwa ta nufi iyakar da take fuskantar Kwarin Ziboyim wajen jeji.
mogili da Bedehoulone moilaigadi asi amola mogi da soge alalo amo da Sibouimi Fago amola hafoga: i soge amoga gadodili dialebe amoga asi.
19 Ba a sami maƙeri ɗaya a dukan ƙasar Isra’ila ba domin Filistiyawa sun ce, “In ba haka ba Ibraniyawa za su ƙera wa kansu takuba ko māsu.”
Isala: ili dunu afaega da gulaga dadi hahamosu hame dawa: i galu, bai Filisidini dunu ilia da Hibulu dunu ilia gegesu gobihei sedade amola gegesu dadi debesa: besa: le, sema bagade ilegei.
20 Saboda haka dukan Isra’ila sukan gangara zuwa wajen Filistiyawa domin su gyara bakin garemaninsu, da fartanansu, da gaturansu, da kuma laujunansu.
(Isala: ili dunu ilia da Filisidini dunuma asili, ilia osobo gidinasu, goahei amola gisi nosu amo debemusa: ahoasu.
21 Duk lokacin da za su gyara bakin garmansu da fartanyarsu sai sun biya tsabar azurfa biyu. Haka ma idan za su gyara gatari ko bakunan abin korar shanun noma sai sun biya tsabar azurfa ɗaya.
Debesea, bidi adosu da gasa fonobahadi afaega da goahei debesu amola bulamagau sese ahoasu ifa seda debesu, amola gasa adunaga osobo gidinasu amola moi dogosu debesu).
22 A ranar da yaƙi ya tashi, ba a sami wanda yake da takobi ko māshi ba a cikin mutanen da suke tare da Shawulu da Yonatan. Sai dai Shawulu da ɗansa Yonatan kaɗai.
Gegesu amoga Isala: ili dadi gagui iliga da Solo amola ea mano Yonada: ne elea fawane da gegesu gobihei sedade amola goge agei gagui.
23 Ana nan sai sojojin Filistiyawa suka fita zuwa mashigin Mikmash.
Filisidini dunu ilia da dadi gagui mogili Migema: sega Adobo Gigiadofa Ahoasu amo sosodo aligima: ne asunasi.

< 1 Sama’ila 13 >